’Yan sanda sun ƙaddamar da samamen “Operation Kukan Kura”, sun kama mutum 98 a Kano
Published: 10th, July 2025 GMT
Rundunar ’Yan Sandan Jihar Kano, ta kama mutum 98 da ake zargi da aikata laifuka daban-daban, ciki har da fashi da makami, safarar miyagun ƙwayoyi, sata, zamba da kuma tayar da hankalin jama’a.
An kama waɗannan mutane ne ƙarƙashin sabon samamen da rundunar ta ƙaddamar mai suna “Operation Kukan Kura” wanda ya fara aiki a ranar 1 ga watan Yuli, 2025.
Kwamishinan ’Yan Sandan Kano, Ibrahim Adamu Bakori, ne ya bayyana hakan yayin taron manema labarai da aka gudanar a hedikwatar rundunar da ke Bompai a ranar Alhamis.
Ya ce wannan aiki wani ɓangare ne na ƙoƙarin daƙile aikata laifuka da tabbatar da zaman lafiya a faɗin Jihar Kano.
Ya ce samamen ya samu goyon bayan Sufetan Janar na ’Yan Sanda, Kayode Adeolu Egbetokun, domin ƙarfafa haɗin kai da al’umma wajen yaƙi da laifuka.
Kwamishinan, ya bayyana cewa wannan aiki yana bin tsarin aikin rundunar, wanda ke nufin haɗa kai da al’umma wajen hana aikata laifuka.
Rundunar ta nazarci halin tsaro a jihar tare da duba yankunan da laifuka suka fi yawa kafin ta ƙaddamar da samamen.
Ya ce babban burin wannan aiki shi ne zama tamkar wata hanyar gargaɗi domin gano da kuma daƙile barazanar laifuka tun kafin su faru.
Daga cikin waɗanda aka kama akwai mutum 21 da ake zargi da fashi da makami, huɗu ana zargin su da garkuwa da mutane, biyar kan safarar miyagun ƙwayoyi.
Sauran sun haɗa da mutum 12 da ake zargi da satar motoci, huɗu ana zargin su da zamba, sai wasu biyar da ake zargi da sata, da kuma mutum 47 da ake zargi da tayar da hankalin jama’a.
Kayayyakin da aka ƙwato sun haɗa da motoci guda shida, adaidaita sahu guda takwas, babura guda tara, tabar wiwi, kwalabe 86 na kayan maye, takubba 16 da wuƙaƙe.
Kwamishinan, ya ce waɗannan nasarori za a ci gaba da amfani da su wajen inganta dabarun aiki da rundunar ke aiwatarwa.
Ya ƙara da cewa rundunar za ta ci gaba da ɗaukar matakan kare rayuka da dukiyoyin al’ummar Jihar Kano.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Yan Sanda Ɓata gari da ake zargi da
এছাড়াও পড়ুন:
Hukumar Kiyaye Hadura Ta Kasa Za Ta Aiki Da ‘Yan Jarida A Kano
Hukumar kiyaye hadurra ta kasa (FRSC) reshen jihar Kano, ta bayyana kudurinta na kara zurfafa dangantakarta da kungiyar ‘yan jarida ta kasa NUJ reshen jihar Kano.
Wannan alkawari ya fito ne daga bakin kwamandan sashin, Kwamandan Corps Muhammad Bature, a lokacin da yake karbar sabbin shugabannin majalisar a hedikwatar hukumar FRSC da ke Kano.
Sabbin shugabannin kungiyar masu aiko da rahotanni ta NUJ sun ziyarci hukumar FRSC ta Kano domin taya rundunar murna kan kokarin da take yi na inganta hanyoyin kiyaye hadurra da kuma gano sabbin hanyoyin hadin gwiwa.
Kwamandan sashin ya yi maraba da ziyarar, inda ya bayyana ta a matsayin wata babbar alama ta tabbatar da ci gaba da hadin gwiwa tsakanin FRSC da NUJ.
Ya bayyana jin dadinsa na yin aiki kafada da kafada da NUJ domin inganta moriyar juna.
Kwamandan sashin ya kuma gayyaci mambobin Kungiyar da su shiga rundunar FRSC Special Marshal Corps a matsayin masu aikin sa kai. Wannan shiri na da nufin tallafa wa kokarin da hukumar ta ke yi a fadin kasar na rage hadurran ababen hawa da asarar rayuka.
Da yake mayar da martani ga kwamandan sashin, zababben shugaban kungiyar ta Chapel, Murtala Adewale, ya ce makasudin ziyarar shi ne don kara tabbatar da alakar da ke tsakanin FRSC da jami’an kungiyar.
Adewale ya bayyana kwarin gwiwarsa na cewa FRSC zai bayar da dandali fadakarwa da zai kara wayar da kan jama’a kan kiyaye hanyoyin mota a fadin Kano da ma wajen.
Abdullahi Jalaluddeen Kano