HausaTv:
2025-07-10@15:43:22 GMT

Kwamandan Sojin Iran Ya Jaddada Kare Kan Iyakokin Jamhuriyar Musulunci Ta Iran

Published: 10th, July 2025 GMT

Kwamandan sojojin kasa na sojojin Iran ya jaddada wajabcin Karin daukan matakan kare iyakokin Jamhuriyar Musulunci ta Iran

Kwamandan sojojin kasa na kasar Iran Birgediya Janar Kiomars Heidari ya jaddada wajibcin kare cikakken kan iyakokin kasar akida, al’adu, da yanki, yana mai cewa: Dole ne dukkanmu al\umma su zama masu kare wannan kasa da kuma samun kwarin gwiwa daga tafarkin shahidai.

A yayin wata ganawa da iyalan shahidan kwanaki 12 da gwamnatin sahayoniyawa ta kakaba wa Iran a birnin Sarpol-e Zahab na lardin Kermanshah a ranar Larabar da ta gabata, Birgediya Janar Heidari ya bayyana cewa: Sojojin kasar suna kan gaba wajen kare ‘yancin kai da yankinsu na kasar, kuma a kodayaushe suna nuna godiya da irin hakurin da iyalan shahidan suke yi.

Ya kara da cewa: Tutar tsaro da tsayin daka za ta ci gaba da tashi har zuwa bayyanar Imam Mahdi (Allah madaukakin sarki ya gaggauta bayyanar da shi), kuma a ko da yaushe za ta kasance tana daga hannun mujahidai masu sadaukarwa.

Babban kwamandan dakarun sojin kasar Iran ya bayyana cewa: Shahidai masu haskaka hanyar daukakan ne da ‘yancin al’ummar Iran, kuma sun sadaukar da rayuwarsu wajen tabbatar da tsaro da kuma abin alfaharin al’ummar musulmi a yau.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Shugaban Majalisar Shawarar Musulunci  ya Bayyana Yadda Iran Da Mayar Da Martani Mai Gauni Kan Isra’ila

Shugaban Majalisar Shawarar Musulunci ta Iran ya jaddada cewa; Mayar da martanin Iran ga ‘yan sahayoniyya sun murkushe girman kan makiya

Shugaban Majalisar Shawarar Musulunci ta Iran Muhammad Baqir Qalibaf ya jaddada cewa: Martanin da Iran ta mayar wa yahudawan sahayoniyya a lokacin arangamar da suka yi a baya-bayan nan abin nuni ne, domin kuwa a duk tsawon tarihin haramtacciyar kasar Isra’ila ba ta taba samun irin wannan martanin mai gauni ba.

Ghalibaf, wanda ya karbi bakwancin jakadan Belarus a birnin Tehran, Dmitry Kaltsov, a jiya Laraba, ya yaba da matakin da gwamnatin Belarus ta dauka dangane da hare-haren da yahudawan sahayoniyya da Amurka suka dauika na kai wa cibiyoyin makamashin nukiliyar Iran hare-haren wuce gona da iri. Yana mai cewa, hare-haren da suka kai kan cibiyoyin makamashin nukiliyar kasar Iran na daga cikin munanan ayyukan da Amurka da yahudawan sahayoniyya suka aikata, idan aka yi la’akari da kasancewar Iran mamba a yarjejeniyar hana yaduwar makaman nukiliya ta NPT da kuma yadda ayyukan kasarta suke gudana  karkashin kulawar hukumar ta kula da makamashin nukiliya ta kasa da kasa ta IAEA.

Shugaban Majalisar Shawarar Musuluncin ya kuma jaddada cewa: A lokacin da aka kai wa Iran hari mahukuntan ta suna gudanar da shawarwari ne da Amurka kan batun shirin, har ma an sanya ranar da za a yi shawarwarin zagaye na shida. Ya kara da cewa: A cikin irin wannan yanayi, Iran ta ga irin yadda gwamnatin ‘yan sahayoniyya da Amurka suka kai wa Iran hari, yayin da a baya ta yi gargadin cewa, za ta mayar da martani mai karfi kan masu wuce gona da iri a duk wani harin da aka kai kan yankin kasarta. A kan haka, duniya ta shaida yadda Iran ta mayar da martani kan hare-haren wuce gona da irin gwamnatin ‘yan sahayoniyya da Amurka.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Shugaban Majalisar Shawarar Musulunci  ya Bayyana Yadda Iran Da Mayar Da Martani Mai Gauni Kan Isra’ila
  • Babban Kwamandan Sojin Iran Ya Bayyana Cewa Iran Ta Koyawa Gwamnatin Isra’ila Hankali
  • Manazaecin Kasar Amurka Ya Ce; Isra’ila Ta Sha Kashi A  Yakinta Da Jamhuriyar Musulunci Ta Iran
  • Akwai Bukatar Sin Da Masar Su Zurfafa Hadin Gwiwa Domin Kare Muradunsu
  • Hukumar Kiyaye Hadura Ta Kasa Za Ta Aiki Da ‘Yan Jarida A Kano
  • Iran Ta Tabbatar Da Cewa Tana Iya Yakar Amurka Da HKI A Lokaci Guda
  • Kakakin Hafsan Hafsoshin Sojin Iran Ya Ce: Iranta Dorawa Amurka Alhakin Duk Harin Da Ta Fuskanta
  • TCN Ta Wayar Da Kan Al’ummomin Kaduna Kan Illar Lalata Kayan Wuta Da Gini Karkashen Babbar Wayar Wuta 
  • Ministan Harkokin Wajen Kasar Iran Yace Mutanen Kasarsa Suna Cikin Shiri Don Kare Kansu Da Karfi