Aminiya:
2025-06-15@07:15:48 GMT

Yadda ake ‘Spring rolls’

Published: 1st, March 2025 GMT

Assalamu alaikum uwargida tare da fatan alheri kuma kuna cikin koshin lafiya.

Kamar yadda a kullum nake ba da shawarar cewa, yana da kyau uwargida ta ƙware wajen girke-girke, wato yana da matukar muhimmanci ta ƙware wajen girkin gargajiya da na zamani da kuma na ƙasashen waje.

Ramadan: Saudiyya ta bai wa Kano da wasu jihohi kyautar dabino katan 1,250 Falalar Ramadan: Wata na rahama, gafara, da tsira daga wuta

Don haka ne a yau na kawo muku yadda ake ‘spring roll’.

Bayan abincin buɗe baki, uwargida za ta iya koyan wannan girki a matsayin sana’a da za ta iya kawo mata kuɗi.

Abubuwan da ake bukata: · Karas · Albasa · Attaruhu · Tafarnuwa · Kabeji · Kayan dandano · Koren tattasai · Kori · Man gyada · filawa

Yadda ake yin hadin:

A sami kwano sannan a zuba garin filawa da ruwa ya dan yi tsororo. Sannan a sami tukunya a zuba man gyada kadan sannan ana zubawa ana kwashe wa.

Za a ga ya yi lafelafe. Bayan an gama da ƙullun sai a ajiye su a gefe.

A kankare karas a yayyanka shi kananan tare da kabeji a wanke a ajiye a gefe. Bayan haka, sai a jajjaga tafarnuwa da attaruhu.

A yayyanka albasa da koren tattasai a dora tukunya sannan a zuba karas da jajjagen attaruhu da yankakken kabeji da albasa a yi ta gauraya su.

Sannan a dauko magi da kori a zuba har sai ya dan nuna sannan a sauke a bari ya huce.

Bayan ya huce sannan sai a dauko wannan wainar filawar da aka ajiye sai a rika diba cokali biyu na hadin a zuba a kai sannan a yi masa nadin tabarma a kalmashe bakin sannan a sake dora man gyada a wuta a soya har sai ya soyu sannan a sauke.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: uwargida

এছাড়াও পড়ুন:

Hajjin 2025: Yadda Alhazan Nijeriya 7 Suka Rasa Rayukansu A Saudi Arabiya

Duk da cewa, yanayin zafi ya yawaita a kasar ta Saudiyya, yayin gudanar da aikin Hajjin 2025, koda-yake; akasarin wadanda suka mutu daga Nijeriyar tsofaffi ne.

Rasuwar farko da aka sanar ta wani Alhaji ce daga Jihar Oyo, Alhaji Sulaimon Hamzat, wanda ya rasu a ranar 17 ga Mayun 2025 a kasar ta Saudiyya.

Na biye da shi kuma daga Jihar Abiya ne, mai suna Alhaji Saleh, Shugaban Kasuwar Shanu ta Lokpanta, wanda ya rasu a garin Makka a daren ranar Litinin 26 ga watan Mayun 2025.

Bayan haka kuma, sai wata Hajiya mai shekaru 75 daga Jattu Uzairue a Karamar Hukumar Etsako ta yamma da ke Jihar Edo, Adizatu Dazumi, wadda ta mutu a ranar Litinin 26 ga Mayun 2025, bayan gajeriyar rashin lafiya.

An samu rahoton cewa, Dazumi ta kamu da rashin lafiya jim kadan bayan kammala dawafi, inda aka garzaya ta ita zuwa asibitin Sarki Fahad da ke Makka a ranar Lahadi, washegari kuma ta mutu.

Haka zalika, wata Hajiya daga Jihar Filato ta rasu a birnin Makka da ke Saudiyya, yayin gudanar da wannan aiki Hajjin 2025.

Marigayiyar, mai suna Hajiya Jamila Muhammad, ta rasu ne sakamakon cutar Siga da ke fama da shi a asibitin Sarki Abdul’aziz da ke birnin Makka.

Kwana daya kafin fara aikin Hajjin 2025, wani Alhaji daga Jihar Kano mai suna Shu’aibu Jibrin, ya rasu a garin Makka.

Haka nan kuma, wani Alhajin Nijeriya ya rasu a filin Arfa.

A cewar Shugaban Hukumar Alhazai ta Nijeriya, Farfesa Abdullahi Saleh Usman, “Mun samu labari mara dadi cewa; mun rasa mahajjatanmu a yau Arfat, dayan kuma ya rasu kafin mu bar Makka,” in ji shi.

Ya kuma ce, mutuwar Alhazan daga Allah ne; inda ya kawar da rade-radin da ake yin a cewa, zafin rana ne ya haddasa su.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Danbun Shinkafa Da Nama Da Kifi
  • Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (1)
  • Amfanin ‘Ya’yan Gwanda Da Yadda Ake Sarrafa Su
  • Sarkakiyar Da Ke Tattare Da Zaben 2027 Da Yadda Za Ta Kaya
  • Farashin fetur ya tashi a kasuwar duniya bayan harin Isra’ila a Iran
  • Hajjin 2025: Yadda Alhazan Nijeriya 7 Suka Rasa Rayukansu A Saudi Arabiya
  • Yadda mota ta kashe mutum 8 ’yan gida daya bayan dawowa daga yawon Sallah a Kaduna
  • ICPC Ta Gurfanar Da Ma’aikacin Kotu Bisa Badakalar Naira Miliyan 9.2
  • Guguwa ta hallaka mutum 6, ta jikkata 30 a Taraba
  • Kocin Kano Pillars Usman Abdullahi Ya Ajiye Aikinsa