Assalamu alaikum uwargida tare da fatan alheri kuma kuna cikin koshin lafiya.
Kamar yadda a kullum nake ba da shawarar cewa, yana da kyau uwargida ta ƙware wajen girke-girke, wato yana da matukar muhimmanci ta ƙware wajen girkin gargajiya da na zamani da kuma na ƙasashen waje.
Ramadan: Saudiyya ta bai wa Kano da wasu jihohi kyautar dabino katan 1,250 Falalar Ramadan: Wata na rahama, gafara, da tsira daga wutaDon haka ne a yau na kawo muku yadda ake ‘spring roll’.
Bayan abincin buɗe baki, uwargida za ta iya koyan wannan girki a matsayin sana’a da za ta iya kawo mata kuɗi.
Abubuwan da ake bukata: · Karas · Albasa · Attaruhu · Tafarnuwa · Kabeji · Kayan dandano · Koren tattasai · Kori · Man gyada · filawa
Yadda ake yin hadin:
A sami kwano sannan a zuba garin filawa da ruwa ya dan yi tsororo. Sannan a sami tukunya a zuba man gyada kadan sannan ana zubawa ana kwashe wa.
Za a ga ya yi lafelafe. Bayan an gama da ƙullun sai a ajiye su a gefe.
A kankare karas a yayyanka shi kananan tare da kabeji a wanke a ajiye a gefe. Bayan haka, sai a jajjaga tafarnuwa da attaruhu.
A yayyanka albasa da koren tattasai a dora tukunya sannan a zuba karas da jajjagen attaruhu da yankakken kabeji da albasa a yi ta gauraya su.
Sannan a dauko magi da kori a zuba har sai ya dan nuna sannan a sauke a bari ya huce.
Bayan ya huce sannan sai a dauko wannan wainar filawar da aka ajiye sai a rika diba cokali biyu na hadin a zuba a kai sannan a yi masa nadin tabarma a kalmashe bakin sannan a sake dora man gyada a wuta a soya har sai ya soyu sannan a sauke.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: uwargida
এছাড়াও পড়ুন:
Yadda aka kama ɗan bindiga ɗauke da N13m da bindigogi a hanyar Jos
Sojoji sun kama wani ƙasurgumin mai garkuwa da mutane ɗauke da tsabar kuɗi Naira miliyan 13 a kan hanyar Kaduna zuwa Jos a Jihar Kaduna.
Dakarun Rundunar Operation Safe Haven sun kuma ƙwace bindigogi ƙirar AK-47 guda biyu da harsasai 30 a hannun ɗan ta’addan a Ƙaramar Hukumar Sanga ta Jihar Kaduna.
Kakakin rundunar, Manjo Samson Zhakom, ya ce dubun ɗan ta’addan ta cika ne a wani shingen bincike da ke yankin Agameti a kan babbar hanyar Wamba zuwa Jos.
Manjo Zhakom ya ce a ranar Laraba, sojoji suka tsayar da wata mota ƙirar Volkswagen Golf da ke ɗauke da mutum uku, amma kafin ta ƙaraso inda za ta tsaya, biyu daga cikin mutanen suka fice suka tsere.
Sojoji sun kashe ’yan fashin daji masu yawan gaske a Zamfara Ya kamata mulkin Najeriya ya ci gaba da zama a hannun ’yan Kudu — Hannatu MusawaYa bayyana cewa sojojin sun gano ramin harbin bindiga da kuma jini a jikin motar, kuma direban ya yi yunƙurin ba su cin hanci amma suka ƙi karba.
“Suka kama shi, bayan cikar wanda ake zargin da kuma cikin motar suka gano bindigogi biyu ƙirar AK-47 da harsasai 30 da wayoyi guda uku da layu da tsabar kuɗi N13,742,000, da wuƙa da sauransu.
“A yayin bincike ya amsa cewa yana da hannu garkuwa da mutane a kan hanyar Jos zuwa Makurɗi, kuma ya amince ya kai sojoji maɓoyarsa.
“A yayin da suke tafiya, wanda ake zargin ya yi yunƙurin ƙwace makamin jami’anmu, amma suka murƙushe shi” in ji shi.
Manjo Zangon ya ce rundunar na ci gaba da zurfafa bincike domin kamo sauran ’yan ta’addan da kuma tabbatar da tsaron rayuka da dukiyoyin al’umma.