Mataimakin Gwamnan Sakkwato bai karɓi shanun tallafin layya ba — Hukumar Zakka
Published: 16th, June 2025 GMT
An samu cece-ku-ce a Jihar Sakkwato bayan da wata jita-jita ta yaɗu cewa Mataimakin Gwamnan jihar, ya karɓi shanu 400 da aka tanadar domin tallafa wa marasa galihu domin yin layya a lokacin Sallah Babba.
An ce shanun wata ƙungiya ce daga ƙasar Turkiyya ta bayar da su, ta hannun Hukumar Zakka da Waƙafi ta jihar, domin tallafa wa waɗanda ba su da halin yin layya.
Sai dai an zargi Mataimakin Gwamnan da karɓe su don amfanin kansa.
Wannan batu ya jawo jama’a a jihar suk dinga bayyana ra’ayoyinsu, inda wasu ke zargin an fifita jami’an gwamnati fiye da talakawa da aka yi nufin bai qa shanun.
Wasu sun zargi cewa malamai, limamai, ‘yan siyasa da ƙungiyoyin addini ne suka fi cin moriyar shanun.
Sai dai a wata hira da wakilinmu ya yi, da mataimakin gwamnan ya musanta karɓar shanun.
Ya ce: “Hukumar Zakka ce ke raba wa ’yan gudun hijira da ke fama da matsalar tsaro kamar a Sabon Birni da Isa.
“A shekarar da ta gabata sun karɓi shanu 20 kowane. Haka nan Illela da Gwadabawa sun samu goma-goma.”
Ya ƙara da cewa ba shi da hannu kai-tsaye, domin an tuntuɓar shi ne kawai a matsayin wanda zai jagoranci rarraba shanun ga jama’ar yankin da ke ƙarƙashinsa.
Shugaban Hukumar Zakka da Waƙafi ta jihar, Malam Muhammad Lawal Maidoki, ya ƙara bayyana cewa:
“Mataimakin gwamna bai karɓi shanun ba. An kafa kwamiti ƙarƙashinsa domin kula da rabon a yankin Gabas da ke fama da matsalar tsaro. Shanun sun ƙare kafin a gama rabawa. An ware 150, amma 106 ne aka samu.”
Ya kuma bayyana cewa sun yi niyyar yanka shanu 4,500 amma saboda wasu matsaloli, ciki har da rashin samun dabbobi da suka cika sharuɗan layya, sun yanka 3,000 kacal.
Malam Maidoki ya nemi afuwa ga duk wanda bai samu shanun ba, da waɗanda aka saba bai wa amma aka kasa ba su, da waɗanda suke tsammanin samun amma ba su samu ba.
Ya ƙara da cewa sun rubuta sunayen waɗanda ba su samu ba domin tunawa da su a shekara mai zuwa.
“Muna fata Allah Ya kawo mu wata shekara cikin lafiya da dama don ci gaba da tallafa wa marasa ƙarfi a irin wannan lokaci,” in ji shi.
A cewar hukumar, shirin ya laƙume sama da Naira biliyan ɗaya, kuma an raba naman layya ga dubban mutane da ba su samu damar yin yanka ba.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Hukumar Zakka mataimakin gwamna Sakkwato zargi Hukumar Zakka
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamnan Kaduna ya bai wa sabon Sarkin Moro’a sandar mulki
Gwamnan Jihar Kaduna, Uba Sani, ya bai wa sabon Sarkin Moro’a, Mai Martaba Isiaku Tagwai Sambo sandar mulki, a wani biki da aka gudanar a garin Manchok da ke Ƙaramar Hukumar Kaura.
Gwamna Sani, ya bayyana cewa sarakunan gargajiya na taka muhimmiyar rawa wajen zaman lafiya, haɗin kai da kuma ci gaban al’umma.
Ya kamata Isra’ila da Iran su kawo ƙarshen rikicin da ke tsakaninsu — Gwamnatin Tarayya Mahara sun kashe mutum 26 a sabon hari a BinuwaiYa ce gwamnatinsa na bai wa sarakunan gargajiya cikakken goyon baya saboda irin rawar da suke takawa a harkar mulki da ci gaban jama’a.
“Mun jajirce wajen haɗa kan al’umma a faɗin Jihar Kaduna, ba tare da nuna bambanci ba.
“Yanzu Jihar Kaduna ta fi samun tsaro da kwanciyar hankali fiye da da. Wannan nasara ta samuwa ne sakamakon gudunmawar sarakunan gargajiya,” in ji Gwamnan.
Ya kuma buƙaci al’ummar jihar da su zauna lafiya da juna tare da yin aiki tare domin ciyar da jihar gaba.
Haka kuma, ya roƙi sarakunan da su ci gaba da jagorantar al’ummominsu cikin adalci da riƙon amana.
Bikin naɗin sarautar ya samu halartar baƙi daga sassa daban-daban, bayan rasuwar tsohon Sarkin Moro’a, Malam Tagwai Sambo, wanda ya rasu ranar 14 ga watan Yuni 2024.
Tsohon Sarkin ya rasu yana da shekaru 88, bayan mulkin shekaru 58.
Sabon Sarkin, Mai Martaba Isiaku Tagwai Sambo, ya gode wa gwamnati da al’ummar Moro’a bisa amincewar da suka yi masa.
Ya yi alƙawarin mulki cikin gaskiya da riƙon amana tare da bin doka da oda.
“Zamu haɗa kai da majalisar masarauta da kuma ɗaukacin al’umma domin tafiyar da wannan mulki yadda ya kamata,” in ji shi.