Aminiya:
2025-06-16@12:02:49 GMT

Sojoji sun hallaka shugabannin ’yan bindiga 2 da wasu a Katsina 

Published: 15th, March 2025 GMT

Dakarun Sojin Saman Najeriya (NAF), sun kashe manyan shugabannin ’yan bindiga guda biyu, Gero (Alhaji) da Alhaji Riga, tare da wasu mayaƙansu sama da 20 a wani hari ta sama da suka kai a Jihar Katsina.

Harin ya faru ne a ranar Laraba, 13 ga watan Maris, a dajin da ke Ƙaramar Hukumar Faskari.

Gwamnatin Tarayya ta musanta zargin Amurka kan cin zarafin Kiristoci  Kotun ɗaukaka ƙara ba ta soke naɗin Sanusi II ba — Gwamnatin Kano

Rundunar Operation Fansan Yamma ta NAF ce ta ƙaddamar da harin bayan samun sahihan bayanai kan maɓoyar maharan.

A cewar Mataimakin Kakakin NAF, Kyaftin Kabiru Ali, ya ce dakarun sun lalata sansanin maharan.

“An kashe ƙarin ‘yan ta’adda a tsaunukan da ke kusa, kuma har yanzu ana ci gaba da binciken irin ɓarnar da aka yi musu,” in ji shi.

Gero da Riga sun shahara wajen bai wa ‘yan ta’adda mafaka, waɗanda ke yawan kai matafiya hare-hare a kan titin Funtua zuwa Gusau.

Mutuwarsu ta zama babban ci gaba ga jami’an tsaro da ke aiki tuƙuru don tabbatar da zaman lafiya a yankin Arewa maso Yamma.

“Wannan babban ci gaba ne a yaƙin da muke yi da ɓarayin daji a Katsina da kewaye.

“Sojojin sama tare da haɗin gwiwar dakarun ƙasa za su ci gaba da kai wa maɓoyar ‘yan ta’adda hare-hare har sai an samu cikakken zaman lafiya,” in ji shi.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: hari Shugabannin Yan Bindiga

এছাড়াও পড়ুন:

Sojojin Kasar Iran Sun Ce Bazasu Dakatar Da Yaki ba Har Zuwa Samun Nasara A kan HKI

Babban kwamandan dokarun khatamul Ambiya (s) a nan birnin Tehran ya bayyana cewa sojojinsa zasu ci gaba da fafatawa da HKI har zuwa lokacinda zata dakatar da kawowa Iran yaki, ko kuma ta sami nasara a kansu,

Kamfanin dillancin labaran Tasnim na kasar Iran ya nakalto Janar Ali Shudmoni, yana fadar haka a yau Lahadi bayan da suke cilla makamai masu linzami da kuma jiragen yaki wadanda ake sarrafasu da nesa kan HKI a karon farko na rana, a cikin kwanaki uku da fara yakin.

Janar Shodmani ya kara da cewa zasu ci gaba da kaiwa yahudawan hare-hare har zuwa lokacinda zasu yi nadama sun daina yakin.

Kwamnatin ya bayyana cewa ya zuwa yanzu sun saminar kasar lalata cibiyoyin da jiragen yakin HKI suke shan makamashi wanda yake basu damar isa kasar Iran don kai hare-hare.  Banda haka akwai nasarori da dama da suka samu a hare-haren wadanda nan gaba zasu bayyana.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sabon harin Iran ya hallaka mana mutum 8 – Isra’ila
  • Iran ta kai sabbin hare-hare birnin Tel Aviv da Haifa
  • Iran Ta Cilla Makamai Kan HKI Da Rana A Karon Farko A Yau Lahadi
  • Sojojin Kasar Iran Sun Ce Bazasu Dakatar Da Yaki ba Har Zuwa Samun Nasara A kan HKI
  • Babban Hafsan Soji Ya Ƙalubalanci Sabbin Sojoji Da Su Shirya Yaƙi Da ‘Yan Ta’adda
  • HOTUNA: Yadda aka yi sulhu da ƙasurgumin ɗan fashin daji Ado Aliero a Katsina
  • Iran Ta Sanar Da Dakatar Da Tattaunawa Da Amurka A Wannan Lokaci Da Take Fuskantar Yaki Daga Isra’ila
  • ’Yan bindiga sun kashe mutum 100 a Benuwe
  • Sojoji Sun kama ɗan China da wasu 4 kan zargin safarar makamai a Borno da Yobe
  • HKI Ta Rufe Filin Saukar Jiragen Sama Na Ben Gorion Tare Da Dauke Jiragenta  Zuwa Waje