Amma duk da haka, hatta wake-wake da raye-raye da kuma abinda ya shafi sinima, tsofaffin jarumai ne su ka kawo su a masana’antar Kannywood, saboda haka ya kasance wani lokaci mai ban sha’awa a tarihi lokacin da Hamisu Lamido Iyan-Tama ya hadu da Hindatu Bashir a kan dandamali don ba shi lambar yabo.

Dukkanmu sai muka tuna da fim dinsu na Badakala (wanda wani jarumi Bashir Mudi Yakasai ya shirya), inda suka yi fim mai dauke da rawa da waka na farko a cikin fina-finan Hausa,wato a shekarar 1997 wannan fim ya daga abinda yanzu ake kira Hausa Afropop, domin shi ne wakar fina-finan Hausa ta farko da aka kai wa Rabi’u BK a kasuwar Kofar Wambai domin sayar da shi a matsayin shirin waka mai zaman kansa, Dan Azumi Baba, wanda ya rubuta labarin, ya na nan tare da su a wannan babban taron.

Tsoffin jaruman Kannywood a bisa wata kungiya mai zaman kanta wadda akasari mata suka kafa wacce a yanzu na ke kira “Hausa Classic Cinema” karkashin jagorancin mutane irin su Wasila Isma’il, sun yanke shawarar gudanar da taron shekara-shekara domin yaba wa kansu da kuma wadanda suka bayar da gudunmawa wajen ci gaban masana’antar.

Ni dai ban san su ba, kuma Hindatu Bashir da ta shirya taron na shekarar 2025 sai da ta bi ta hannun mutane biyu domin su zo wurina su kawo mani goron gayyata, Hamisu Lamido Iyan-Tama ya kira ni ‘yan sa’o’i kadan kafin taron ya nemi in halarta, mutane biyu ne kacal a Kannywood da za su umarce ni da in yi irin wannan abu, kuma zan yi su ne Hamisu Iyan Tama da Alkanawy, da na shirya sai na tafi tare da dana Munzir.

Wadannan tsofaffin jarumai sun kasance fuskokin fina-finan Hausa na gargajiya da labarun soyayya, eh labarun soyayya da a kan iya samun rikice-rikice na cikin gida sanadiyar soyayya kuma a samu mafita cikin sauki ta hanyar salo daban-daban, ba tare da sun nuna wani abu na tsiraici ba saboda dukkansu sun mallaki hankalinsu tun kafin su shiga harkar, saboda haka dole ne su tsare mutuncin kansu da na iyalinsu.

Manyan dattawan jarumai da su ka halarci wannan taron a ranar akwai Ado Ahmad Gidan Dabino, Dan Azumi Baba, Balaraba Ramat Yakubu, Bala Anas Babinlata, Hamisu Lamido Iyan-Tama da sauran wadanda su ka kafa kuma su ka zage damtse wajen ganin masana’antar ta tsayu da kafafunta tun daga shekarun 1990 zuwa yanzu, dayan jinsin kuma akwai dattawan jarumai mata kamar ita kanta da ta shirya taron Hindatu Bashir, Hajara Usman, Hadiza Kabara, Ladin Cima, Maijidda Abbas, Rukayya Dawayya, da wasu da yawa da ba zan iya tunawa ba.

A bangaren mu da muke zaune a teburin manyan baki kuwa akwai Muhammadu Rabi’u Rikadawa, sai Dan Azumi Baba, ni kaina, Ado Ahmad, Hajiya Balaraba, Ladi Cima da Hajara Usman,na yi matukar farin ciki da kasancewa cikin wadannan yan wasan kwaikwayo da furodusoshi,dukkan wurin cike yake da mutane, har ba za mu iya ganin sauran wadanda ke zaune a wannan teburi na manyan baki ba, amma dai na san cewar su ma sun bayar da irin tasu gudunmawar wajen wannan babban aiki da aka faro shekaru fiye da Talatin da su ka wuce.

An bai wa Ado Ahmad Gidan Dabino lambar yabo ta “Trailblazer Award, a matsayin wanda ya share fage ga al’ummar da su ka shigo Kannywood ta hanyar wani shiri nasa mai suna “In Da So Da Kauna”, fim din ya fayyace irin nau’in soyayya tun daga farko,ya kuma hada da hakikanin tarihin rayuwar Hausawa tare da hasashen goben bahaushe wanda a wancan lokacin har littafi ya rubuta akan wannan makala.

An bai wa Dan Azumi lambar yabo ta “Star Producer Award” bisa la’akari da rawar da ya taka a masana’antar nishadin Hausa baki daya, tabbas hakane, domin shi ne ya gano Hamisu Lamido-Iyan-Tama, babban dan wasan kwaikwayo mai ban sha’awa wanda zai iya tsayuwa a duk inda wani jarumi ya tsaya ko da kuwa a masana’antar Hollywood ne.

Abin ban mamaki duka biyun Dan Azumi da Ado sun fara zama kwararrun marubutan Hausa kafin su yi kaura zuwa masana’antar fim a matsayin uwayen da su ka kafa ta, a tsakiyar shekarun 1990, a farkon shekarar 2000 an mayar da su zuwa matsayin mashawarta kawai, rawar da su ka taka a cikin manyan fina-finai na baya bayan inda Ado Ahmad ya fito a matsayin Gwamna (Kwana Casa’in) wanda shirin siyasa ne, da Dan Azumi a matsayin Kamaye a shirin Dadin Kowa, wanda akayi saboda hadin kan al’umma, ya nuna cewar DA TSOHUWAR ZUMA AKE MAGANI, don kuwa bani tunanin akwai wani daga cikin matasan jarumai na yanzu da zai yarda ya taka irin wannan rawar.

Balaraba Ramat Yakubu ta samu lambar yabo ta “Legendary Producer Award, inda aka karramata da lambar yabo ta furodusar da ta taka muhimmiyar rawa wajen ci gaban masana’antar Kannywood, fina finanta irinsu Sai A Lahira” da “Alhaki Kwikwiyo” za su dade ana tunawa dasu a tarihin wannan masana’antar a kodayaushe, abinda na kira “Kannywood Classics”, Hamisu Lamido Iyan-Tama ya sami shaidar wani mutum da ya nunawa manyan gobe hanyar da ya kamata su bi a wannan masana’antar.

An ba ni lambar yabo ta “Special Recognition” a matsayin wadanda ba jaruman fim ba amma kuma su ka bayar da gudunmawarsu ta wata sigar, amma kuma sun cancanci karramawa saboda irin gudunmawar da suka bayar ta hanyar inganta da kuma kiyaye al’adun Hausa ta hanyar fim”, duk da cewar rukunin gajerun bidiyo ya kamata ace na fito amma dai wannan kyautar na dauke ta a matsayin karramawa ta musamman a wajena.

A kan dandamalin “Red Carpet”, an tambaye ni yadda na ji game da taron, sai na mayar da martani cewa taron ya fayyace ainahin abinda ake kira Da Tsohuwar Zuma Ake Magani, duba da dimbin taurarin da su ka halarci taron, wadanda su ne uwa da magoyiyar masana’antar nishadin zamani ta Hausa, wadannan taurari sun samar da fina-finai masu tsafta, wanda ake yaba wa kuma ana kiransu da ‘Classics’.

Sun gabatar da fina finai na Iyali da sauran abubuwan da su ka shafi rayuwar Malam Bahaushe, amma da wasu su ka zo sai suka yi watsi da wadannan fina finai suka kama wasu labaran karya game da Hausa da rayuwarsu, irin wadannan tsofaffin gwanaye wadanda ke da tsantsar sani na al’adar fina-finan Hausa ne za su kai ga farfado da fina-finan Hausa, su ne za su jagoranci hanyar kai masana’antar Kannywood zuwa Tudun Mun Tsira.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Farfesa Abdallah Kannywood Hamisu Lamido Iyan Tama a masana antar lambar yabo ta

এছাড়াও পড়ুন:

Kamfanonin Waje Sun Ce Dole Ne Su Shiga A Dama Da Su A Cikin Kasuwar Kasar Sin

Yayin taron shekara-shekara na tattaunawar CBD na shekarar 2025 da aka rufe a yau Juma’a 13 ga wata, mashawarci kana kwararre a hukumar kasuwancin kasar Sin ta kasar Birtaniya, kuma shugaban cibiyar bunkasa kasuwanci tsakanin Birtaniya da Sin mista John Mclean, ya bayyana yayin da yake hira da wakilin CMG cewa, kasuwar kasar Sin tana cike da damammaki, don haka dole ne ya shiga a dama da shi a cikinta. A ganinsa, yayin da ake tinkarar tashe-tashen hankula da rashin tabbaci a duniya, babbar baiwar da Sin take da ita, da muhalli mai aminci da bude kofa ga kowa, sun samarwa kamfanonin Birtaniya da ma duniya baki daya damammaki.

Tun bayan kafuwarsa a shekarar 2000 zuwa yanzu, taron ya kasance dandali da kasar Sin ke tattaunawa da kasashen duniya. A yayin taron bana, wakilai fiye da 6000 daga sassan siyasa, da kasuwanci, da ilimi da suka fito daga kasashe da yankuna fiye da 40 sun halarta. A lokacin gudanar da taron, wasu mahalartansa sun yi nuni da cewa, kasar Sin na da babbar juriya wajen raya tattalin arziki, da kuma babbar baiwar raya kasa. Haka kuma, gwamnatin Sin ta gaggauta raya sabon karfin samar da hajoji da hidimomi masu karko, lamarin da ya zuba sabon kuzari ga kamfanonin kasashen waje, ta yadda suke shiga a dama da su wajen yin ciniki a kasar Sin.

A yayin bikin bude taron, mahalartansa sun yi kira da a gina duniya mai tsabta, da kyawu, da dorewa cikin hadin gwiwa, duba da ganin kasar Sin ta ba da babbar gudummawa, ta kuma yi iyakacin kokari a fannin raya kasa ba tare da gurbata muhalli ba, da kuma rage fitar da sinadarin carbon. Alkaluma sun nuna cewa, yanzu haka kasar Sin tana daya daga cikin kasashen da suka fi saurin rage yawan makamashi mai dumama yanayi da suke amfani da shi da samun kyautatuwar iska, ta kuma dasa yawan bishiyoyi, da ciyayi da fadinsu ya kai rubu’i bisa jimillar fadin sabbin bishiyoyi da ciyayi na duniya baki daya, tare da kafa tsarin makamashin da ake sake amfani da shi mafi girma, kuma mafi saurin ci gaba a duniya, baya ga kafa tsarin masana’antu na sabbin makamashi mafi girma kuma cikakke a duniya. (Tasallah Yuan)

 

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Masana Ilimin Nukiliyar Iran Sun Yi Shahada
  • Jagoran Juyin Musulunci Na Iran Ya Nada Sabbin Kwamandojin Soja Da Dakarun Kare Juyin Musulunci
  • Na’im Kassim: Harin HKI Akan Iran Ba Abinda Zai Jawo Mata Sai Kaskanci
  • An Kaddamar Da Bikin Gabatar Da Jerin Shirye-shiryen Telebijin Da Fina-finai Na CMG A Birnin Astana
  • Kamfanonin Waje Sun Ce Dole Ne Su Shiga A Dama Da Su A Cikin Kasuwar Kasar Sin
  • Nijeriya Ce Ta 3 A Manyan Kasashe Masu Karfin Masana’antu 10 Na Afirka
  • Iran tana da hakkin mayar da martani ga Isra’ila : Sanarwar Ma’aikatar harkokin waje
  • Hamas : Ziyarar ministan Isra’ila Ben-Gvir a masallacin al-Aqsa kan iya tayar da yakin addini
  •  Iran Za Ta Kara Yawan Sanadarin Urani’um Da Take Tacewa A Wuri Na Sirri
  • NAJERIYA A YAU: 12 Ga Yuni: Me Ranar Dimokuraɗiyya Ke Nufi Ga Talakan Najeriya?