Ramadan: ’Yan sanda sun tsaurara tsaro saboda azumi a Borno
Published: 1st, March 2025 GMT
Rundunar ’Yan Sandan Jihar Borno, ta sanar da ƙarin matakan tsaro yayin da al’ummar Musulmi suka shiga watan azumin Ramadan.
Haka kuma, rundunar ta taya Musulmi murnar shigowar wannan wata mai alfarma.
Gobara ta hallaka mutum 2 a sansanin ’yan gudun hijira a Borno Ramadan: Ga arahar kayan abinci ga rashin kuɗin sayaKakakin rundunar, ASP Nahum Kenneth Daso, ya bayyana cewa an kammala shirin tsaurara tsaro domin tabbatar da zaman lafiya a cikin watan Ramadan.
“Mun san muhimmancin wannan wata ga ’yan uwanmu Musulmi,” in ji sanarwar.
“Saboda haka, mun ƙara sintiri da samar da jami’an tsaro a wurare masu muhimmanci a faɗin jihar.”
Kwamishinan ’yan sandan Borno, CP Yusufu Mohammed Lawal, ya tabbatar da cewa rundunar tana sadaukar da kai domin kare lafiyar jama’a a cikin wannan wata.
“Burinmu shi ne kowa ya samu damar gudanar da ibadarsa cikin kwanciyar hankali da tsaro,” in ji Kwamishinan.
Haka kuma, rundunar ta buƙaci jama’a da su kasance masu lura tare da kai rahoton duk wani abu da ba su yarda da shi ba ga ofishin ’yan sanda mafi kusa.
“Idan kun ga wani abu, ku sanar da hukuma,” in ji ASP Daso.
Rundunar ta kuma fitar da lambobin kiran kar ta kwana domin bayar da rahoto: 08068075581 da 08023473293.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Yan Sanda Ramadan Tsaro rundunar ta
এছাড়াও পড়ুন:
Sojoji sun harbe mayaƙan ISWAP 8 a Borno
Sojojin Najeriya sun kashe aƙalla mayakan ƙungiyar ISWAP 8, ciki har da manyan kwamandojinta biyu a Jihar Borno.
Wata majiyar leƙen asiri daga rundunar haɗin kai ta OPHK ta bayyana cewa an kashe ’yan ta’addan ne a wata arangama da suka yi da sojojin a kan hanyar Maiduguri zuwa Baga a safiyar ranar Litinin.
DSS ta maka Sowore da Facebook a Kotu kan cin zarafin Tinubu Gwamnatin Kano ta gayyaci Mai Dubun Isa da Shehi Tajul-Izzi kan shirya muƙabalaA cewar majiyoyin, an yi arangamar ce a kusa da Garin Giwa da ke gab da ƙauyen Kauwa, lokacin da ’yan ta’addan suka yi wa dakarun da ke sintiri kwanton ɓauna.
“A yayin wannan artabu, an kashe ’yan ta’adda takwas, ciki har da Munzirs biyu (kwamandojin filin daga na ƙungiyar) da kuma Qaid ɗaya (shugaban sashe).
“An kashe Modu Dogo, Munzir daga Dogon Chukun, wani Munzir da ba a bayyana ba, da Abu Aisha, shugaban sashe (Qaid) daga Tumbun Mota,” in ji wata majiya.
Majiyar ta ƙara da cewa wasu mayaƙa da dama sun samu raunuka, musamman waɗanda suka tsere da ƙafa bayan sun yi watsi da babura 14 da sojojin suka ƙwato.