Aminiya:
2025-09-18@01:09:56 GMT

An raba wa ma’aikatan gona babura 200 a Yobe

Published: 1st, March 2025 GMT

Gwamnatin Yobe ta raba wa ma’aikatan gona babura guda 200 domin gudanar da ayyukan kula da harkokin noma a jihar.

Kwamishinan ma’aikatar gona da albarkatun kasa, Ali Mustapha Goniri ne ya bayyana haka a lokacin da yake miƙa baburan ga waɗanda suka rabauta.

Yadda farashin kayan abinci ya sauka a kasuwannin Arewa Yadda ake ‘Spring rolls’

Ya ce an yi rabon baburan ne domin tallafa wa ayyukan ma’aikatan da kuma bunƙasa noman zamani a jihar ta hanyar sabbin dabaru da kayan aiki.

Goniri ya ce ma’aikatar gona za ta sa ido kan yadda ma’aikatan da ke aikin faɗaɗa ayyukan noma ke yi domin tabbatar da cewa manoma a kowane lungu da saƙo na jihar suna noman amfanin gona da iri masu inganci.

A cewarsa, an horas da ma’aikatan da za su yi aiki domin kyautata alaƙa tsakanin masu bincike da manoma, don haɓaka samar da kayayyaki, tabbatar da samar da abinci, da kuma inganta rayuwar manoma.

A nasa jawabin, babban sakataren ma’aikatar, Muhammad Inuwa Gulani, ya ce jami’an ma’aikatar aikin gona za su taimaka wa manoma wajen yanke shawara kan kirkire-kirkire da fasaha kan harkokin noma na zamani.

Ya ce ma’aikatan za su kuma taimaka wa manoma wajen samun sabbin bayanai da fasahohin zamani, inda ya ce shirin zai taimaka wa manoman wajen inganta sana’o’insu, da inganta rayuwar su, da tabbatar da samar da abinci ga al’umma.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Babura Jihar Yobe

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamna Namadi Ya Taya Malaman Makarantu Da Suka Yi Fice A Jihar Murna

Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya yabawa Hukumar Makarantun Kimiyya da Fasaha ta Jiha bisa ƙirƙirar Kyautar Malami Mafi Nagarta, yana mai bayyana hakan da ɗaya daga cikin manyan manufofin da za su ƙarfafa koyo da koyarwa a fadin jihar.

A cikin wata sanarwa da Babban Jami’in Yaɗa Labaran sa, Hamisu Mohammed Gumel, ya fitar, gwamnan ya bayyana cewa bikin na farko na bada lambar yabo da aka gudanar a Dutse ya dace domin girmama malamai da suka yi fice ta hanyar jajircewa da sadaukar da kai.

Ya ƙara da cewa wannan mataki zai ƙara kwarin gwiwa, ya samar da gasa mai kyau, tare da inganta darussa a makarantu.

Namadi ya jaddada cewa ingancin ilimi bai tsaya kan gina makarantu kawai ba, yana ta’allaka ne ga ingancin malamai, kayan koyarwa da kuma yanayin makarantu.

Ya bayyana cewa gwamnatinsa ta fara ɗaukar malamai tare da horas da su akai-akai domin rage cunkoson ɗalibai da malamai da kuma horar da su sabbin dabarun koyarwa.

“Wannan shiri ɗaya ne daga cikin mafi kyawu da muka gani. Idan wani ya yi kuskure, sai a hukunta shi, yayin da duk wanda ya yi fice, wajibi ne a yaba masa. Wannan shi ne yadda ake samun cigaba,” in ji gwamnan.

Ya bukaci sauran hukumomin ilimi kamar Hukumar Gudanar da Makarantun Sakandare, Hukumar Ilimin Addinin Musulunci, da Ma’aikatar Ilimin Firamare su yi koyi da wannan tsari domin ƙara ƙarfafa gwanintar malamai a dukkan matakai.

Gwamnan ya kuma sake jaddada  cewa gwamnatinsa za ta ci gaba da maida hankali wajen gina makarantu, horar da malamai, da walwalar su.

Ya tabbatar da cewa za a ci gaba da baiwa bangaren ilimi goyon baya don inganta sakamakon koyo a makarantu a fadin Jihar Jigawa.

 

Usman Muhammad Zaria 

 

 

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnati ta ƙaddamar da jiragen ruwa na zamani 20 a Sakkwato
  • Manyan Ma’aikatan FIRS 4 Sun Rasu Sakamakon Gobarar Da Ta Tashi A Ginin Afriland A Legas 
  • Gwamna Namadi Ya Taya Malaman Makarantu Da Suka Yi Fice A Jihar Murna
  • Gwamnatin Kano Ta Inganta Cibiyoyin Horas Da Sana’o’i Domin Dakile Aikata Laifuka Tsakanin Matasa
  • Ma’aikatar Shari’ar Iran Ta Sanar Da Rataye Dan Leken Asirin Hukumar Mossad Ta Isra’ila
  • Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo
  • ALGON ta karrama Gwamna Buni da lambar yabo kan kawo ci gaba a Yobe
  • Ɗan Majalisar Tarayya Ya Nuna Damuwa Kan Ƙaruwar Hare-haren Ta’addanci A Sakkwato 
  • Kundin Bajinta na Guinness ya taya Hilda Baci murna
  • KEDCO ya ƙaryata asibitin AKTH kan mutuwar majinyata saboda ɗauke wuta