Ministan harkokin wajen Iran ya bayyana cewa: Ci gaba da killace Gaza da kuma kashe mutanen da ba su ji ba ba su gani ba, laifi ne da ba a taba yin irinsa ba a tarihin dan Adam

A wata tattaunawa ta wayar tarho da takwaransa na Masar Badar Abdel Ati a yammacin jiya Lahadin da ta gabata, Araqchi ya bayyana ci gaba da killace yankin Gaza da rashin abinci da magunguna, tare da kashe mutanen da ba su ji ba ba su gani ba, a matsayin wani laifi da ba a taba ganin irinsa ba a tarihin dan Adam.

Ya dauki Amurka da sauran masu goyon bayan ‘yan sahayoniyya a matsayin masu hannu a kisan kiyashi da laifukan yaki da ake aikatawa a Gaza.

Ministan harkokin wajen na Iran ya jaddada wajibcin tunkarar muggan manufofin yahudawan sahayoniyya na tilastawa al’ummar Gaza da yammacin kogin Jordan yin hijira daga muhallinsu, yana mai bayyana halin ko in kula da kasashen duniya suke nun awa kan wadannan laifuka a matsayin abin mamaki da damuwa.

Araghchi ya kuma yi wa takwaransa na Masar bayani kan ci gaban tattaunawar Iran da Amurka kan Shirin makamashin nukiliya na zaman lafiya da ake takaddama a kai tsawon shekaru.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Qalibaf : Dole ne Iran da Aljeriya su hada kai don saukaka kai kayan agaji zuwa Gaza

Shugaban Majalisar Dokokin Iran Mohammad Baqer Qalibaf ya ce kamata ya yi kasashen Iran da Aljeriya su hada kai wajen kai kayan agaji a zirin Gaza da yaki ya daidaita.

Qalibaf ya bayyana hakan ne a lokacin da yake ganawa da shugaban majalisar al’ummar kasar Aljeriya Ibrahim Boughali a ranar Laraba a birnin Jakarta na kasar Indonesiya, a gefen taron ‘yan majalisar dokokin na kungiyar hadin kan kasashen musulmi ta PUIC karo na 19.

Ya jaddada muhimmancin samar da hadin kai wajen tunkarar hare-haren wuce gona da iri da Isra’ila ke yi a Falasdinu da kuma maido da hakkokin al’ummar Falastinu da ake zalunta a zirin Gaza.

Qalibaf ya yi kira ga kasashen musulmi da su hada kai su nemo hanyoyin warware rikicin Falasdinu.

Ya kuma bukaci sauran kasashe da su ci gaba taimakawa al’ummar Falasdinu samun nasara ta karshe.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An Ziyarci Gidajen Tarihin Kasar Sin Sau Biliyan 1.49 A Shekarar 2024
  • Iran Ta Jaddada Kawo Karshen Bakar Siyasar gwamnatin ‘Yan Sahayoniyya Kan Al’ummar Falasdinu
  • Ayatullah Khamenei : “Ba inda Rundunar Amurka ta taba shinfida zaman lafiya “
  • Jamhuriyar Musulunci Ta Iran Ta Jaddada Hakkinta Na Tace Sinadarin Yuraniyom Don Aikin Cikin Gida
  • Tsohon Fira Ministan Gwamnatin Isra’ila Ya Bukaci A Tsige Netanyahu Daga Kan Fira Ministan Isra’ila
  •  Fira Ministan Spain: Ba Za Mu Yi Mu’amala Da Isra’ila  Mai Kisan Kiyash
  • Xi Jinping Ya Jaddada Wajibcin Koyi Da Nagartattun Halayen Wasu Mutane Masu Bukata Ta Musamman
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Jaddada Cewa: Karfin Tsaro Da Makamansu Masu Linzami Ne Suka Hana Makiya Kai Musu Hari
  • Jakadan Iran A Majalisar Dinkin Duniya Ya Ce Amurka Tana Da Hannu Dumu-Dumu A Kisan Kiyashin Gaza
  • Qalibaf : Dole ne Iran da Aljeriya su hada kai don saukaka kai kayan agaji zuwa Gaza