A cewar Kwamishinan, sojojin sun yi artabu da ‘yan ta’adda a kauyukan Malori da Matalawa, inda suka kara tura su cikin tsaunukan.

 

Mua’zu ya ci gaba da bayanin cewa, yayin da jami’an tsaron suka isa sansanin Sanusi Dutsin-Ma, sun yi nasarar tarwatsa jama’arsa tare da kashe ‘yan ta’adda uku, yayin da wasu da dama suka gudu da raunuka.

 

Bayan haka, sojojin sun ceto mutane 84 da aka yi garkuwa da su da suka hada da maza bakwai, mata 23, da kananan yara 54 da aka tsare a sansanonin ‘yan ta’addan.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnonin Arewa sun yi Allah-wadai da sace ɗalibai mata a Kebbi

Ƙungiyar Gwamnonin Arewa (NGF) ta bayyana matuƙar damuwa kan harin da aka kai Makarantar Sakandiren Mata da ke Maga a ƙaramar hukumar Danko/Wasagu ta Jihar Kebbi, wanda ya yi sanadin sace ɗalibai mata da dama tare da kashe jami’an makarantar.

Shugaban ƙungiyar, kuma Gwamnan Gombe, Muhammadu Inuwa Yahaya, ya bayyana lamarin a matsayin abin takaici da rashin hankali, yana mai cewa ci gaba da kai hare-hare kan makarantun Arewa barazana ce ga zaman lafiya da makomar ilimi a yankin.

Barau FC ta doke Enugu Rangers a Firimiyar Najeriya Anthony Joshua zai yi dambe da tauraron YouTube Jake Paul a Disamba

A madadin sauran gwamnonin Arewa, Gwamna Inuwa ya jajanta wa Gwamnatin Jihar Kebbi, iyalan waɗanda aka sace da kuma waɗanda suka rasa rayukansu, tare da tabbatar wa Gwamna Nasir Idris da cikakkiyar goyon bayan ƙungiyar.

A wata sanarwa da Babban Daraktan Yaɗa Labarai na Gwamnatin Jihar Gombe, Isma’ila Uba Misilli, ya fitar, ƙungiyar ta buƙaci a gaggauta haɗa kai tsakanin jami’an tsaro domin ceto ’yan matan da aka sace da kuma kamo waɗanda suka aikata laifin.

Gwamnonin Arewa sun jaddada aniyarsu ta yin aiki kafada da kafada da Gwamnatin Tarayya da hukumomin tsaro domin tabbatar da tsaron makarantun yankin.

Gwamna Inuwa ya yi addu’ar Allah Ya dawo da ’yan matan lafiya, tare da kira ga al’umma da su kasance masu sa ido da bayar da goyon baya ga jami’an tsaro.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tankin ruwa ya kashe mutum 4, wasu sun jikkata a Jigawa
  • DAGA LARABA: Hanyoyin Da Suka Kamata A Bi Wajen Ceto Daliban Kebbi Da Aka Sace
  • Sojojin Najeriya Sun Karyata Cewa “ISWAP” Ta Kashe Wani Babban Jami’i Mai Mukamin  Birgediya
  • Gwamnonin Arewa sun yi Allah-wadai da sace ɗalibai mata a Kebbi
  • Dole ku ceto daliban da aka sace a Kebbi Shugaban Sojoji
  • Ana Zargin ’Yan Ta’adda Sun Kashe Janar Ɗin Soji A Harin Kwanton-Ɓauna A Borno
  • Za mu ceto ’Yan Matan GGCSS Maga cikin ƙoshin lafiya — Gwamnan Kebbi
  • Rushewar Ramukan Hako Ma’adinai Ta Kashe Mutane 32 A Jamhuriyar Dimokaradiyyar Kwango
  • Sojojin HKi Sun Kashe Wasu Falasdinawa Guda 2 A Sansanin Yan Gudun Hijira
  • ’Yan ta’adda sun yi garkuwa da dalibai 25 a Kebbi