Aminiya:
2025-07-09@01:54:43 GMT

Malaman firamare sun janye yajin aiki a Abuja

Published: 9th, July 2025 GMT

Malaman makarantun firamare da ke ƙarƙashin Hukumar Ilimin Ƙananan Hukumomi (LEA) a babban birnin tarayya Abuja sun janye yajin aikin da suka tsunduma watanni uku da suka gabata.

Ana iya tuna cewa, tun a watan Maris ne dai malaman da ke ƙarƙashin ƙungiyar malamai ta ƙasa NUT suka tsunduma yajin aikin kan abin da suka kira rashin byan haƙƙoƙinsu na mafi ƙarancin albashi da aka ƙayyade na Naira dubu 70.

An kama ɓarayin babura a Gombe An ƙayyade maki da shekarun shiga jami’a a Nijeriya

Aminiya ta ruwaito cewa, a ranar Alhamis din makon jiya ce Ministan Abuja, Nyesome Wike ya gana da shugabannin ƙungiyar malaman daga ƙananan hukomomi shida na Abuja da wasu masu ruwa da tsaki.

Bayan wannan ganawar ce gamayyar ƙungiyoyin malaman a yammacin wannan Talatar ta sanar da janye yajin aikin wanda ta ce zai fara ne daga gobe Laraba, 9 ga watan Yulin 2025.

Shugabannin ƙungiyoyin malaman da suka sanya hannu a takardar janye yajin aikin sun bayyana cimma wannan matsaya ce bayan sakin wani kaso da ya kai kusan naira biliyan 16 na bashin da za a biya malaman albashinsu na watannin da aka dokar sabon mafi ƙarancin albashin ta soma aiki.

Sanarwar ta ambato ƙungiyar malaman tana yi wa mambobinta godiya bisa haƙuri da jajircewa da kuma hadin kan da suka bayar tsawon lokacin da aka shafa ana yajin aikin.

Haka kuma, ƙungiyoyin malaman sun miƙa godiya ta musamman zuwa hedikwatar ƙungiyar malamai ta ƙasa NUT da ƙungiyar ƙwadago NLC reshen Abuja, da sarakunan gargajiya da ƙungiyoyin fararen hula da duk wadanda suka tsaya tsayin daka wajen ganin gwamnati ta waiwayi buƙatunsu.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: malaman firamare Yajin aiki janye yajin yajin aikin

এছাড়াও পড়ুন:

Taron Ashura Ya Zama Lamari Mafi Girma Da Cinkoson Jama’a, Inda Masu Ziyara Daga Sassan Duniya Suka Isa Karbala

Gangamin Ashura ya zama lamarin mafi girma da cunkoson jama’a inda tattakiin Tuwairij yake gudana tare da faɗaɗa da ba a taɓa ganin irinsa ba

Tattakin Tuwairij na bana zuwa birnin Karbala na fuskantar hallara da cunkoson jama’a da ba a taba ganin irinsa ba, inda dimbin masu ziyara  daga sassan duniya ke tururuwa zuwa hubbaren Imam Husaini da kuma titunan da ke kewaye.

Mai ba da shawara ga babban sakataren cibiyar Hubbaren Imam Husain {a.s} Fadel Oz a cikin wata sanarwa da ya aikewa kafafen watsa labarai ya bayyana cewa: “A shirye-shiryen wannan juyayi, babban Sakatariyar Haramin Imam Husain (a.s) da haramin Abbas sun samar da dukkan sharuddan da suka dace don kula da masu ziyara da kuma tabbatar da jin dadinsu.

Ya kara da cewa, “Yankin da aka kebe domin gudanar da juyayin Ashura  ya samu gagarumin ci gabata hanyar fadada shi, domin a shekarun da suka gabata ana ci gaba da gudanar da ayyukan da suka yi na mallakar wuraren da ke kewaye da fadada titunan da ke zuwa gare su da nufin daukar saukaka wa masu halartar taron.

Oz ya ci gaba da cewa “Hukumar ayyuka, ‘yan sanda, sassan jami’ai, da kuma cibiyoyin gwamnati sun kuma taka rawar gani wajen hada kai don tabbatar da gudanar da juyayin Ashura cikin kwanciyar hankali da lumana.”

Ya bayyana cewa, “wannan hadin gwiwa yana nuna irin kishin da hukumomin da abin ya shafa suke da shi wajen tabbatar da nasarar gudanar da juyayin Ashura a cikin yanayi na musamman na ruhi,” yana mai jaddada cewa “wadannan fadadawa da shirye-shirye suna tafiya tare da ci gaba da karuwar masu ziyara da kuma tabbatar da samun kwarewa da kwanciyar hankali a wannan babban taron addini.”

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ASUU Ta Janye Yajin Aiki Bayan Gwamnatin Tarayya Ta Biya Albashin Watan Yuni
  • Mata Da Matasa Dari Hudu Suka Amfana Da Tallafi A Gandun Albasa Kano
  • ASUU Ta Tsunduma Yajin Aiki A Faɗin Nijeriya
  • Ƙungiyar Al’ummar Igbo Ta Ohanaeze Ndigbo Ta Ce Tinubu Ya Fi Ƙarfin ‘Yan Jam’iyyar Haɗaka Ta ADC
  • Asibiti Mai Zaman Kansa A Kano Zai Fara Aikin Manyan Tiyatu Tare Da Rage Kuɗi Kaso 50%
  • Asibiti Mai Zaman Kansa A Kano Zai Fara Manya Manyan Tiyatu Tare Da Rage Kuɗi Kaso 50%
  • Sheikh Ibrahim Zakzaky Ya Taya JMI Murnar Nasara A Kan Mikiyanta
  • Mataimakin Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Sabbin Fasahohin Kimiyya A Fannin Aikin Gona Da Kiwon Lafiya
  • Taron Ashura Ya Zama Lamari Mafi Girma Da Cinkoson Jama’a, Inda Masu Ziyara Daga Sassan Duniya Suka Isa Karbala