Darakta mai kula da al-amuran mata da kuma kare hakkin bil’adama a ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran, Forouzandeh Vadiati, ta hadu da jakadan kasar Jamus a nan Tehran da kuma mataimakin jakadan kasar Burtania a Tehrana a ma’aikara. Inda ta bayyana masu bacin ranta da yadda kasashen biyu suka shigar da wata daftari ta tuhumar Iran da abinda ya shafi hakin mata da a hukumar kare hakkin bil’adama ta MDD.

Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto Vadiati yana zargin Berlin da kuma London na shiga cikin al-amuran cikin gida na JMI. Sannan ta tunanatar da kasar Jamus kan abinda ta aikata na bawa Sadam Hussain makaman guba a yakin shekaru 8 da suka fafata da kasar ta Iraki.

Sannan ta bayyana yadda kasar Burtania ta dade tana adawa da JMI, daga ciki har da goyon bayan da kasashen biyu suke bawa HKI a kissan kiyashin da take wa falasdinawa a gaza.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Shugabar IOC: Gasar Wasanni Ta Kasar Sin Tana Da Babbar Ma’ana

Shugabar kwamitin shirya wasannin Olympics na duniya (IOC), Kirsty Coventry, ta halarci bikin bude gasar wasannin kasa ta Sin karo na 15 a lardin Guangdong da yammacin ranar 9 ga Nuwamba. A ranar 12 ga wata kuma, Coventry ta yi wata hira ta musamman da ‘yar jarida daga babban rukunin gidajen rediyo da talabijin na Sin wato CMG a nan birnin Beijing.

Yayin hirar, Coventry ta bayyana cewa, gasar wasannin kasar Sin ta wannan karo tana da babbar ma’ana. Ta ce yayin da take ziyarar aiki a Sin, ta yi tattaunawa da dama, ciki kuma har da ganawa da shugaba Xi Jinping. Shugaba Xi ya ce mokamar bunkasuwar yankin gabar tekun Guangdong-Hong Kong-Macao, ba tsara manufofin da za a iya cimmawa kadai ya yi ba, har ma da gabatar da alkiblar da za ta tabbatar da cimma hakan a karshe. Ta ce tana fatan wasannin za su iya taka rawa mai tasiri da inganci a cikin wannan tsari.

Ta kara da cewa, a yanzu, wasanni sun zama masana’antar duniya mai daraja sosai. Inda ta ce tana matukar farin cikin ganin jari mai yawa ya shiga cikin harkokin gina al’ummomi. Kuma saka hannun jari a bangaren wasanni, a zahiri saka hannun jari ne a cikin al’umma, kuma yana da muhimmanci ga gina zamantakewa mai kuzari.(Safiyah Ma)

ADVERTISEMENT ShareTweetSendShare MASU ALAKA Daga Birnin Sin Ayyukan Kirkire-kirkire Na Kamfanonin Sin Na Kara Zama Babbar Kadara Ga Duniya November 13, 2025 Daga Birnin Sin An Gudanar Da Taro Mai Taken “Shugabancin Duniya: Ayyukan Matasa” A Johannesburg Dake Afirka Ta Kudu November 13, 2025 Daga Birnin Sin Xi Ya Bukaci Matasa Masanan Harkokin Sin Su Kasance Gada Tsakanin Sin Da Duniya November 13, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ɗan Najeriya ya kashe mahaifinsa, ya yanki ƙannensa da wuƙa a Amurka
  •  Kasar Afghanistan Na Kokarin Karkata Akalar Kasuwancinta Zuwa Iran
  • Rundunar Sojin Nijeriya Ta Bayyana Dalilan Hana Jami’anta Auren ‘Yan Kasashen Waje
  • Iran ta bukaci duniya ta gaggauta daukar mataki a Sudan
  • Ana Samun Kwararar ‘Yan Hijira Daga Mali Zuwa Kasar Cote De Voire
  • Sin Ta Yi Tsokaci Kan Kalaman Da Firaministar Japan Takaichi Sanae Ta Yi A Kanta
  • Kalubalantar Ka’idar “Kasar Sin Daya Tak A Duniya” Tamkar Wasa Da Wuta Ne
  • Ronaldo Na Fuskantar Dakatarwar Wasanni Biyu Bayan Samun Jan Kati
  • Majalisar Wakilai ta dage lokacin fara yin jarabawar WAEC a kwamfuta zuwa 2030
  • Shugabar IOC: Gasar Wasanni Ta Kasar Sin Tana Da Babbar Ma’ana