Babatun Lai Ching-Te Ba Zai Taba Girgiza Kasancewar Sin Day Tak A Duniya Ba
Published: 9th, July 2025 GMT
Kwanan baya, jagoran yankin Taiwan na kasar Sin Lai Ching-te ya gabatar da jawabai masu taken wai “jawabai 10 game da hadin kan al’umma”, da nufin ba da ingantacciyar hujja ga ra’ayinsa mai shirme game da ballewar Taiwan daga kasar Sin, tare da yaudarar jama’ar yankin da kuma yaudarar jama’ar duniya.
Ko Lai ya manta da cewa, a ran 19 ga watan Mayun da ya shude, shekaru 9 a jere ne babban taron hukumar lafiya ta duniya WHO ya ki yarda da shirin da wasu kasashe tsirraru suka gabatar na halartar Taiwan taron. Yawancin kasashen duniya sun nanata matsayinsu kan kiyaye kudurin babban taron MDD mai lamba 2758, da nace wa ga bin ka’idar kasar Sin daya tak a duniya, da kin yarda da halartar yankin Taiwan babban taron WHO, lamarin da ya shaida cewa, manufar kasar Sin daya tak a duniya ta samu amincewa daga al’ummun duniya.
Ya zuwa yanzu, adadin kasashen da suka kulla huldar diplomasiyya da kasar Sin ya kai 183, kuma dukkansu sun nace ga bin manufar kasar Sin daya tak a duniya, inda wasu suka bayyana a fili rashin jin dadinsu game da yunkurin ballewar yankin Taiwan daga kasar Sin da kuma goyon bayan dinkewar kasar baki daya. Matakin da ya bayyana cewa, al’ummun duniya sun kai ga matsaya daya kan wannan batu har ya zama ka’idar huldar kasa da kasa.
Idan muka duba sakamakon binciken jin ra’ayin jama’a da jaridar Formosa Post ta yankin Taiwan ta gudanar, tuni gamsuwar jama’ar yanki game da ayyukan da Lai Ching-te ya yi, ta ragu zuwa kashi 44.7%, adadin da ya kai matsayi mafi kankanta tun bayan da ya hau kujerar mukaminsa a watan Mayun bara. Kowa ya san yankin Taiwan wani bangare ne da ba za a iya ware shi daga kasar Sin ba, kuma wannan shi ne matsaya daya da al’ummun Sinawa da yawansu ya kai biliyan 1.4 ciki hadda jama’ar yankin Taiwan da yawansu ya kai miliyan 23 suka dauka, wanda kuma ra’ayi daya ne da kasa da kasa suka cimma. Maganar Lai kamar tururuwa ne a gaban giwa, za a taka ta ta mutu, abin da zai kawo karshen ra’ayin baraka. (Amina Xu)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: yankin Taiwan kasar Sin da
এছাড়াও পড়ুন:
Ci Gaba Da Killace Gaza Bayan Tsagaita Bude Wuta Ya Janyo Mutuwar Mutane 1000 A Yankin
Killace Gaza da gwamnatin mamayar Isra’ila take ci gaba da yi tun bayan tsagaita bude wuta ya yi sanadiyyar mutuwar masara lafiya 1000 a yankin
Majiyoyin lafiya na Falasdinawa sun tabbatar a yau Alhamis, 30 ga watan Oktoban shekara ta 2025 cewa: Tun bayan tsagaita bude wuta, gwamnatin mamayar Isra’ila ta hana shigar da kayan aikin likita da kayayyakin bukatu cikin Gaza, yayin da marasa lafiya dubu suka mutu sakamakon tsauraran matakan tsaro da kuma rufe hanyoyin shiga cikin yankin.
Majiyoyin sun bayyana cewa kashi 10% ne kawai na bukatun lafiya suka shiga yankin Gaza, kuma babu na’urorin MRI masu aiki a yankin Gaza.
Dr. Muhammad Abu Salmiya, Darakta Janar na Al-Shifa Medical Complex, ya bayyana cewa tun bayan karshen yakin, kashi 10% ne kawai na bukatun suka shiga yankin, kuma Gaza na rasa adadi mai yawa na marasa lafiya a kowace rana saboda hana kayayyakin magunguna shiga yankin.
Dr. Abu Salmiya ya bayyana fargabarsa game da yaduwar ƙwayoyin cuta a yankin, yana mai lura da cewa marasa lafiya 350,000 suna buƙatar magani don magance cututtuka masu tsanani, waɗanda magunguna an hana shigarsu Gaza, yayin da adadin masu fama da asma ya ƙaru saboda tarkace a yankin.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Kungiyar Rapid Support Forces Ta Sanar Da Kafa Kwamitin Bincike Kan Cin Zarafin Al’umma A El Fasher October 30, 2025 An Kafa Dokar Ta Baci A Darul-Salam Saboda Tarzoman Zaben Shugaban Kasa A Tanzania October 30, 2025 Rasha Da Amurka Sun Sake Dawo Da Gwaje-gwajen Makaman Nukiliya October 30, 2025 Kasar Czech Ta Hana Wa Wani Sojan HKI Shiga Kasar Bisa Gargadin Faransa October 30, 2025 Sojojin HKI Sun Kutsa Kudancin Lebanon October 30, 2025 Adadin Falasdinawan Da Su Ka Yi Shahada A Cikin Sa’o’i 24 Sun Haura 100 October 30, 2025 Amurka Ta Hana Marubuci Dan Nigeria Wole Soyinka Izinin Shiga Amurka October 30, 2025 Pakistan Tayi Barazanar Daukar Mataki Bayan Rushewar Yarjejeniyar Dakatar Da Bude Wuta Da Afghanistan. October 29, 2025 IRS: Sanya Sabbin Takunkumi Kan Kasar Iran Zai Haifar Da Mummunan Sakamakon A Yankin October 29, 2025 An saka dokar Ta Baci Bayan Barkewar Zanga-zanga A Zaben Shugaban Kasar Tanzaniya October 29, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci