Majalisar wakilai ta amince da dokar ta-ɓaci a Ribas
Published: 20th, March 2025 GMT
Majalisar Wakilai ta amince da ayyana dokar ta-ɓaci da Shugaba Bola Tinubu ya yi a Jihar Ribas.
Majalisar ta yanke wannan shawara ne a ranar Alhamis, ta hanyar kaɗa ƙuri’a da baki, inda ’yan majalisa 243 suka halarta.
Muhimman ayyuka 8 a goman ƙarshe na Ramadan Fashewar Tanka: Asibitoci sun cika da mutane a AbujaA matsayin wani ɓangare na matakan dokar ta-ɓaci, majalisar ta bayar da shawarar kafa kwamiti domin dawo da zaman lafiya a jihar.
Hakazalika, majalisar za ta karɓi ragamar gudanar da ayyukan Majalisar Dokokin Jihar Ribas na tsawon watanni shida.
Me Ya Sa Aka Ayyana Dokar Ta-ɓaci?Matakin ya biyo bayan rikicin siyasa da ya ƙi ya ƙi cinyewa a Jihar Ribas.
Shugaba Tinubu ya yanke wannan shawara ne sakamakon tashe-tashen hankula da rikicin shugabanci a jihar.
Gwamna Siminalayi Fubara na takun-saƙa da Majalisar Dokokin Jihar da wasu jiga-jigan ’yan siyasa musamman waɗanda ke tsagin tsohon gwamnan jihar, Nyesom Wike, lamarin da ya jefa jihar cikin tashin hankali.
Domim shawo kan matsalar, Tinubu ya naɗa Tsohon Babban Hafsan Rundunar Sojin Ruwa, Vice Admiral Ibok-Ete Ibas (mai ritaya), a matsayin sabon mai kula da jihar.
Hakan ya sa Gwamna Fubara da wasu manyan jami’ai, ciki har da iyalansa, suka bar gidan gwamnatin jihar.
Ana ci gaba da sa ido kan halin da ake ciki a jihar, yayin da gwamnati ke ƙoƙarin tabbatar da doka da oda a jihar.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Amincewa Dokar Ta Ɓaci Goyon Baya Majalisar Wakilai
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamnatin Neja Ta Musanta Rahoton Hana Da’awa A Jihar
Rahoton rashin fahimtar da aka fara yadawar, ya biyo bayan taron kwamitin zaman lafiya da kwantar da tarzoma na jihar, wanda Darakta Janar ya jagoranta a ranar 4 ga watan Satumba.
Rashin fahimtar sahihin sakamakon taron ya sa wasu suka rahoto cewa, kwamitin ya dakatar da Malamai daga yin wa’azi.
Sanarwar ta kara da cewa, “Hukumar ba ta da hurumin haramtawa Malaman Addinin Musulunci yin wa’azi sai dai in ya bayyana a fili an taka ƙa’idojin hukumar da ta shimfiɗa”.
A cewar Hukumar, an kira taron ne domin gabatar da fom din rijistar yin wa’azi ko Da’awah da kuma bin tsarin tantancewa.
Ta bayyana shirin a matsayin wani yunkuri na wayar da kan jama’a don “hana rashin fahimtar juna da kuma daƙile yaɗuwar wa’azin yaudara” a faɗin jihar Neja.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp