Firaministan kasar Sin Li Qiang, ya halarci taron mataki na 2 da na 3 na ganawar shugabannin BRICS karo na 17 da aka gudanar a Rio de Janeiro hedkwatar kasar Brazil, tsakanin ranakun 6 zuwa 7 ga watan nan da muke ciki, tare da gabatar da jawabi.

Li ya ce, hadin gwiwar kasashen BRICS dole ne ya nace ga matsayin kiyayewa da tabbatar da cudanyar bangarori daban-daban a duniya, da gaggauta kafa tsarin ciniki da tattalin arzikin duniya mai adalci da bude kofa, da hada kan kasashe masu tasowa, don taka rawar gani ga samun bunkasar duniya mai dorewa.

Ya kara da cewa, ya kamata a dukufa kan shimfida halayen tattalin arzikin duniya mai bude kofa, da daga matsayin hadin gwiwar kasa da kasa kan harkar hada-hadar kudi, da ma bullo da wata sabuwar hanyar samun bunkasar tattalin arziki. A nata bangare, Sin za ta samar da abun koyi dangane da hadin gwiwar yanar gizo tsakanin kasashe masu tasowa karkashin shawarar raya duniya, don gabatar da ayyukan ba da horo har 200 ga kasashe masu tasowa a shekaru 5 da suke tafe, a bangaren tattalin arzikin yanar gizo, da fasahar AI da sauransu.

Li ya kuma jadadda cewa, dole ne al’ummun duniya su hada hannunsu wajen tinkarar sauyin yanayi, da kara samun ingantaccen ci gaban kiyayen muhallin hallitu, da gaggauta karfin gudanar da ayyukan kiwon lafiyar jama’a. Kuma Sin za ta ci gaba da daukar nagartattun matakai, da sauke nauyin dake wuyanta, na kokarin ciyar da hadin gwiwar mabambantan bangarori don samun bunkasa mai kiyaye muhalli a dogon lokaci. (Amina Xu)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: hadin gwiwar

এছাড়াও পড়ুন:

’Yan bindiga sun sace fasto da matarsa  masu ibada a Kogi 

’Yan bindiga sun yi garkuwa da wani fasto da matarsa da mabiyansa a yayin da suke tsaka da ibada a coci da ke a  Jihar Kogi.

Wani ganau da ke cikin cocin a lokacin da aka kai harin, Adegboyega Ogun, ya ce misalin ƙarfe 9.30 na safe ’yan bindigar suka kai harin suna bude wuta.

“Mutane sun qarshe ta ko’ina, har da faston, wanda aka fi sani da Baba Orlando da matarsa da wasu masu ibada duk an yi garkuwa da su. Gaskiya harin ya yi muni, dukkanmu tserewa muka yi daga cocin.”

Sace masu ibadar a ranar Lahadi a Cocin Cherubim and Seraphim ya auku ne bayan a kwanan nan Gwamna Usman Ododo, ya koka da cewa wasu  manyan jagororin ’yan bindiga sun dawo jihar.

Kafin nan a ranar Asabar ’yan bindiga sun tare hanya, suka yi garkuwa da matafiya cikin motoci uku a kan hanyar Isanlu-MakutuIdofin da ke Ƙaramar Hukumar Yagba ta Gabas.

Wani mazaunin yankin, Enimola Daramola ya bayyana cewa, “mutum ɗaya ne kacal ya samu tserewa a motocin da aka tafi da su cikin daji.”

“Amma mun samu labari yau cewa sojoji da ’yan banga sun bi sawun ’yan bindigar inda suka yi musayar wuta suka ceto wasu daga cikin mutanen,”

A ranar Lahadi kuma aka samu rahoton cewa an kai wa wata motar haya hari.

“Matuƙin motar da fasinjojin sun tsallake rijiya da baya. Yanzu hanyar ta zama mai hatsari sosai,” in ji David Juwon, mazaunin yankin Isanlu.

Sabon harin Cocin Cherubim and Seraphim na zuwa ne makonni kaɗan bayan makarancinsa da ’yan bindiga suka sace mutane 38 a wani Cocin CAC da ke yankin Eruku na Karamar Hukumar Ekiti a Jihar Kwara.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Baqaei: Amurka Ce Babbar Barazana Ga Zaman Lafiya Da Tsaro A Duniya
  • ’Yan bindiga sun sace fasto da matarsa  masu ibada a Kogi 
  • NAJERIYA A YAU: Halayen Da Ambasadoji Ya Kamata Su Mallaka Kafin Tura Su Wasu Kasashe
  • An yi gangami a fadin duniya a zagayowar ranar Falasdinu
  • An sake zabar Eto’o a matsayin Shugaban Hukumar kwallon kafa ta Kamaru  
  • Dalilin da na koma jam’iyyar ADC — Atiku
  • Hizbullah Ta Bukaci Shugaban Cocin Katolika Na Duniya Yayi Tir Da Hare-haren Isra’ila
  • Iran Za ta Kauracewa taron fasalta kasashen da za su halarci  gasar cin kofin duniya na shekara ta 2026
  • CAF ta ƙara yawan ’yan wasan ƙasashe zuwa 28 a gasar nahiyar Afrika
  • Portugal ta lashe Kofin Duniya na ’yan ƙasa da shekaru 17 a karon farko