Aminiya:
2025-07-02@02:22:22 GMT

Gobara ta ƙone gidaje tare da asarar dukiya a Gombe

Published: 20th, March 2025 GMT

Wata gobara mai muni ta laƙume gidaje uku a unguwar New GRA, a birinn jihar Gombe, a ranar Laraba inda ta bar iyalai cikin rashin matsuguni tare da asarar dukiya ta miliyoyin Naira.

Waɗanda abin ya shafa sun koka kan rashin damar ceto komai daga kayan su, kuma yanzu haka suna neman tallafin gaggawa domin sake farfaɗowa daga wannan masifa.

‘Za a fara biyan Naira 77,000 ga masu yi wa ƙasa hidima daga Maris’ Gwamnan riƙon ƙwarya na Jihar Ribas ya isa gidan gwamnati

Gobarar wadda ta tashi da rana tsaka, ta yi saurin yaɗuwa zuwa gidaje uku, inda ta ƙone su kurmus.

Hukumomin yankin har zuwa yanzu ba su bayyana ainihin dalilin tashin gobarar ba, yayin da waɗanda abin ya shafa suke zaune ba tare da matsuguni ko abinci ko kayayyakin amfani na yau da kullum ba.

Malama Sakina, ɗaya daga cikin waɗanda abin ya shafa, cikin kuka tana mai bayyana cewa,  “Mun rasa komai. Babu wanda ya taimaka mana lokacin da gobarar ta tashi. Muna buƙatar taimako, musamman daga gwamnati da masu taimakon jama’a, domin mu sake tsayuwa. Kowa ya san halin ƙunci da ake ciki yanzu.”

Wani wanda gobarar ta shafa, Yakubu Baba Gombe, ya bayyana damuwa kan jinkirin da jami’an kashe gobara suka yi wajen isowa wurin. inda ya ce, “Lokacin da suka iso, komai ya riga ya ƙone.”

Iyalan da abin ya shafa yanzu haka sun dogara ne ga taimakon al’umma don samun tallafi na gaggawa. A halin yanzu kuma, mazauna yankin suna kira ga hukumomi da su gudanar da bincike kan lamarin tare da ɗaukar matakan kariya daga aukuwar irin wannan gobarar a nan gaba.

Wakilinmu ya yi ƙoƙarin ya ji ta bakin hukumar kashe gobara kan wannan gobarar amma lamarin ya citura

Wannan iftila’i ya bar mutane cikin baƙin ciki, yayin da iyalai ke roƙon taimako domin sake gina rayuwarsu. Ƙoƙarin jin ta bakin jami’an kashe gobara bai yi nasara ba.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: tashin gobara da abin ya shafa

এছাড়াও পড়ুন:

Iran Ta Ce: Ba Za Ta Koma Zaman Tattaunawa Da Amurka Ba Sai A Kan Wasu Sharudda

Dakatar da ayyukan wuce gona da iri kan Iran wani sharadi ne na ci gaba da tattaunawar makamashin nukiliya

Mataimakin ministan harkokin wajen kasar Iran mai kula da harkokin siyasa Majid Takht-e Ravanchi ya bayyana cewa: Sharadin ci gaba da gudanar da zaman shawarwarin makamashin nukiliyar Iran shi ne dakatar da duk wani matakin wuce gona da iri kan Iran, kuma har yanzu Amurka ba ta dauki wani mataki ba kan wannan batu.

A wata hira da tashar BBC game da batun tattaunawar makamashin nukiliyar Iran da Amurka: Takht-e Ravanchi ya ce: “Sun ji daga Amurka cewa a shirye take ta ci gaba da tattaunawar, amma har yanzu ba a tsayar da ranar ba, kuma Iran ba ta amince da tsarin shawarwarin ba.”

Ya kara da cewa: “A halin yanzu Iran tana neman amsoshi dangane da ko za ta sake fuskantar sabbin matakan wuce gona da iri yayin da aka fara tattaunawar.” Har yanzu dai Amurka ba ta bayyana matsaya ba kan wannan batu.

Da aka tambaye shi game da yiwuwar cimma yarjejeniya tsakanin bangarorin biyu, ciki har da dage takunkumin da aka kakabawa Iran, a madadin Iran ta dakatar da inganta sinadarin Uranium, Takht-e Ravanchi ya ce: “Me zai sa su amince da wannan shawara? Inganta sinadarin Uranium zuwa kashi 60 cikin 100 ana amfani da shi ne domin zaman lafiya. Tabbas za a iya tattaunawa kan matakinsa, amma maganarsu ta cewa dole ne Iran ta daina inganta Uranium gaba daya, in ba haka ba za ta fuskanci hari, wannan maganar hankali me? Wannan dokar daji ce.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Isra’ila na bincike kan harin dakarunta da ya kashe fararen hula a Gaza
  • Xi Jinping Ya Jaddada Niyyar Gina Babbar Kasuwar Kasa Ta Bai Daya, Tare Da Raya Tattalin Arziki Na Teku Mai Inganci
  • Iran Ta Ce Babu Batun Tattaunawa Duk Tare Da Amurkawa Sun Ce Za’a Yi
  • An Kashe ‘Yan Kungiyar Shabab 19  A Kasar Somaliya
  • Iran Ta Ce: Ba Za Ta Koma Zaman Tattaunawa Da Amurka Ba Sai A Kan Wasu Sharudda
  • Iran Ta Bawo Mayakan Huthi Fasahar Kera Makamai Masu Linzami Daga Cikin Ruwa
  • HKI Ta Kashe Falasdinawa 72 A Cikin Gaza A Yua Litinin
  •  Wani Dan Bindiga Dadi Ya Kashe Ma’aikatan Kashe Gobara 2 A Amurka
  • Har yanzu mun gaza gano dalilin ɓullar COVID-19 — WHO
  • Falasdinu: Sojojin HKI Suna Ci Gaba Da Kai Hare-hare A Yammacin Kogin Jordan