Aminiya:
2025-12-04@12:51:22 GMT

Gobara ta ƙone gidaje tare da asarar dukiya a Gombe

Published: 20th, March 2025 GMT

Wata gobara mai muni ta laƙume gidaje uku a unguwar New GRA, a birinn jihar Gombe, a ranar Laraba inda ta bar iyalai cikin rashin matsuguni tare da asarar dukiya ta miliyoyin Naira.

Waɗanda abin ya shafa sun koka kan rashin damar ceto komai daga kayan su, kuma yanzu haka suna neman tallafin gaggawa domin sake farfaɗowa daga wannan masifa.

‘Za a fara biyan Naira 77,000 ga masu yi wa ƙasa hidima daga Maris’ Gwamnan riƙon ƙwarya na Jihar Ribas ya isa gidan gwamnati

Gobarar wadda ta tashi da rana tsaka, ta yi saurin yaɗuwa zuwa gidaje uku, inda ta ƙone su kurmus.

Hukumomin yankin har zuwa yanzu ba su bayyana ainihin dalilin tashin gobarar ba, yayin da waɗanda abin ya shafa suke zaune ba tare da matsuguni ko abinci ko kayayyakin amfani na yau da kullum ba.

Malama Sakina, ɗaya daga cikin waɗanda abin ya shafa, cikin kuka tana mai bayyana cewa,  “Mun rasa komai. Babu wanda ya taimaka mana lokacin da gobarar ta tashi. Muna buƙatar taimako, musamman daga gwamnati da masu taimakon jama’a, domin mu sake tsayuwa. Kowa ya san halin ƙunci da ake ciki yanzu.”

Wani wanda gobarar ta shafa, Yakubu Baba Gombe, ya bayyana damuwa kan jinkirin da jami’an kashe gobara suka yi wajen isowa wurin. inda ya ce, “Lokacin da suka iso, komai ya riga ya ƙone.”

Iyalan da abin ya shafa yanzu haka sun dogara ne ga taimakon al’umma don samun tallafi na gaggawa. A halin yanzu kuma, mazauna yankin suna kira ga hukumomi da su gudanar da bincike kan lamarin tare da ɗaukar matakan kariya daga aukuwar irin wannan gobarar a nan gaba.

Wakilinmu ya yi ƙoƙarin ya ji ta bakin hukumar kashe gobara kan wannan gobarar amma lamarin ya citura

Wannan iftila’i ya bar mutane cikin baƙin ciki, yayin da iyalai ke roƙon taimako domin sake gina rayuwarsu. Ƙoƙarin jin ta bakin jami’an kashe gobara bai yi nasara ba.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: tashin gobara da abin ya shafa

এছাড়াও পড়ুন:

’Yan sandan Borno sun kama matashin da ake zargi da kashe makwabciyarsa da wuƙa

Rundunar ’yan sandan jihar Borno ta kama matashin nan da ake zargi da kashe makwabciyarsa a unguwar Shuwari II, a garin Maiduguri babban birnin jihar, ta hanyar daba mata wuka.

Kakakin rundunar ’yan sandan jihar, ASP Nahum Kenneth Daso, ya ce lamarin ya faru ne da misalin ƙarfe 11:00 na dare a ranar Talata.

Amurka za ta hana ’yan Najeriyar da ake zargi da yi wa Kiristoci kisan kiyashi biza Jirgin fadar shugaban ƙasa ya ƙi sayuwa wata 5 bayan saka shi a kasuwa

Ya ce ana zargin matashin ne mai shekaru 17 da aka fi sani da Amir, wanda makanike ne da kashe matar ta hanyar daba mata wuka.

Wani makwabcin wajen ya shaida cewa ana zargin matashin ne da shiga gidan ta hanyar tsallake katanga bayan ya jira ragowar mutanen gidan sun shiga ciki.

A cewar majiyar, matashin ya ɗauki wuƙa ya daba wa matar gidan, wadda ba a bayyana sunanta ba, a ƙirji da wuya, sannan ya tafi da wayarta da na’urar cajin hannu (power bank).

Majiyar ta ƙara da cewa bayan aikata laifin, wanda ake zargin ya koma gidansu ya wanke tufafinsa da kayan da ya yi amfani da su domin kauce wa bin sahunsa.

Rahotanni sun ce ƙanwar mijin wadda aka kashe ce ta fara sanar da jama’a bayan ta ji ihun matar tana neman taimako.

Lokacin da ta fito ta duba, sai ta ga wanda ake zargin yana gudu ya koma gidansu.

Majiyoyi sun tabbatar da cewa jami’an ’yan sanda sun kama matashin da misalin ƙarfe 2:30 na rana.

Sai dai kakakin rundunar, ASP Nahum Kenneth Daso, bai samu damar yin ƙarin bayani ba har zuwa lokacin hada wannan rahoto.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ’Yan sandan Borno sun kama matashin da ake zargi da kashe makwabciyarsa da wuƙa
  • ’Yan Najeriya suna da ƙwarin guiwa a kaina, ba zan ba su kunya ba — Ministan Tsaro
  • Gobara ta ƙone kasuwar katako a Abuja
  • Gobara ta kashe mata da miji da ’ya’yansu 3 a Katsina
  • Har yanzu ban bar yin waqa ba-Yusuf Lazio
  • An yi garkuwa da manoma 11 a Kudancin Kaduna
  • Lebanon: An Gudanar Da Taron Musulunci da Kiristanci a Beirut tare da halartar Paparoma
  • ’Yan ta’adda sun kashe ɗan sanda a gidan DPO a Jigawa
  • Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan (a) 165
  • Sarkin Musulmi ya buƙaci gwamnonin Arewa suke saurarar ƙorafin jama’a