Leadership News Hausa:
2025-12-04@09:18:51 GMT

Dangote Ya Sake Rage Farashin Man Fetur Zuwa Naira 820

Published: 9th, July 2025 GMT

Dangote Ya Sake Rage Farashin Man Fetur Zuwa Naira 820

Mai magana da yawun matatar Dangote, Mista Anthony Chiejina, ya tabbatar da rage farashin a Legas.

Ya ce, “Farashin man fetur ya ragu daga Naira 840 zuwa Naira 820 kan kowace lita.”

Ya bayyana cewa rage farashin da aka yi a baya zuwa Naira 840 ya faru ne sakamakon hauhawar farashin ɗanyen mai a duniya sanadiyyar rikicin da ya auku a Gabas ta Tsakiya.

Kamfanonin da ke haɗa kai da Dangote irin su MRS, Heyden, Ardova (AP), Hyde, Optima, da Techno Oil za su fara sayar da fetur a sabon farashin.

Haka kuma, wasu sabbin kamfanonin da ke dillancin mai sun shiga jerin masu rarraba man Dangote.

Kamfanonin sun haɗa da: TotalEnergies, Garima Petroleum, Sunbeth Energies, Sobaz Nigeria Ltd., Virgin Forest Energy, Sixxco Oil Ltd., N.U. Synergy Ltd., Soroman Nigeria Ltd., Jezco Oil Nigeria Ltd., Jengre, Cocean, Kifayat, Triumph Golden, Sifem Global, Riquest, da Mamu Oil da sauransu.

Matatar Dangote ita ce mafi girma a nahiyar Afirka kuma ɗaya daga cikin manya a duniya da ke tace ɗanyen mai.

Dangote ya kashe sama da Naira biliyan 720 wajen shigo da motoci 4,000 da ke amfani da iskar gas domin rarraba man fetur a faɗin Nijeriya.

Dangote ya ce zai ɗauki nauyin sama da Naira tiriliyan 1.07 na kuɗin jigilar mai a duk shekara.

Wannan shiri zai taimaka wa masu ƙanana da matsakaitan masana’antu miliyan 42 ta hanyar rage kuɗin makamashi da ƙara yawan ribarsu.

Haka kuma, zai rage yawan kuɗin dakon mai da dilallai ke biya, wanda hakan zai iya sa farashin mai ya sauka a gidajen mai tare da rage hauhawar farashin kayayyaki.

A baya, Dangote ya sanar da shirinsa na fara kai fetur da dizil kai-tsaye zuwa matatun mai da masana’antu daga ranar 15 ga watan Agusta.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Farashin Mai

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Gurfanar da Iyayen Yaran da Ba Sa Zuwa Makaranta

Daga Aliyu Muraki

Hukumar Ilimi Matakin Farko ta Jihar Nasarawa (NSUBEB) ta yi barazanar kamawa tare da gurfanar da iyayen da  ‘ya’yansu ba sa zuwa makaranta a jihar.

Shugaban Hukumar, Dr. Kasim Mohammed Kasim ne ya bayyana haka yayin ganawa da manema labarai a matsayin wani bangare na ayyukan babban  taron inganta ilimi da hukumar ta shirya.

Dr. Kasim Mohammed Kasim ya ce, ilimin boko matakin farko haƙƙin kowanne yaro ne, ba gata ba, kuma ya sha alwashin tabbatar da cewa ba a bar wani yaro a baya ba.

Shugaban Hukumar ya bayyana cewa hukumar ta yanke shawarar gudanar da gagarumin wayar da kan jama’a ta hanyar tarurrukan jin ra’ayoyin jama’a, da kafofin watsa labarai domin jaddada muhimmancin ilimin boko na a matakin farko ga kowane yaro a jihar.

Dr. Kasim Mohammed Kasim ya ce sun sayi motocin bas guda bakwai da za a gudanar da wayar da kan jama’a a dukkan sassan kananan hukumomi 13 na jihar, domin fadakar da iyaye  muhimmancin kai ‘ya’yansu makaranta.

Game da babban taron, Dr. Kasim Mohammed Kasim ya ce wannan taro zai hada manyan masu ruwa da tsaki ciki har da masana ilimi, jami’an gwamnati, sarakunan gargajiya, masu tsara manufofi, iyaye, malamai da sauransu.

Ya ce, mahalarta taron za su tattauna hanyoyin magance matsalolin ilimi, musayar kwarewa da sabbin dabaru domin kara inganta koyarwa da koyo a jihar.

Ya lissafo wasu daga cikin matsalolin da suka hada da ginin makarantu marasa inganci, karancin kujeru, karancin malamai, yawan rashin zuwa aiki daga ma’aikata, da rashin daidaitaccen tsarin tura malamai, da sauransu.

Ya ce hukumar ta maida malamai 1,900 wadanda a da ke aiki a ofis-ofis zuwa azuzuwa domin koyarwa, kuma nan ba da jimawa ba za a dauki sabbin malamai 1,000 domin cike gibi a makarantun jihar.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Mutum 6 sun rasu, 13 sun jikkata a hatsarin mota a Kogi
  • CBN ya kara yawan kudin da mutum zai iya cirewa a mako zuwa N500,000
  • Masar Ta Sanar Da Tattaunawa Da Amurka Don Shirya Sake Gina Gaza
  • Gwamnatin Nasarawa Za Ta Gurfanar da Iyayen Yaran da Ba Sa Zuwa Makaranta
  • Najeriya: Matatar Man Fetur ta Dangote Za Ta Mika Tataccen Mai Lita Biliyan 1.5 A Watan Disamba
  • Gwamnatin Jihar Kaduna Ta Gabatar Da Kasafin Kudin 2026 Na Kimanin Triliyan Daya
  • An kama ’yan bindiga 4 a Kano
  • ‘Yan Bindiga Sun Sake Kai Hari Garin Eruka Na Jihar Kwara