Rundunar ‘yan sandan Jihar Gombe ta cafke mutane biyu da ake zargi da satar babura wadanda ta ƙwato babura biyu a hannunsu hadi da wani wanda aka tsinta a lokacin sintiri.
Kakakin rundunar, DSP Buhari Abdullahi, ya ce an gudanar da samamen ne bisa bayanan sirrin da aka samu daga wani mai kishin ƙasa, wanda ya kai jami’an Operation Hattara har zuwa wata maɓoyar ɓata gari a Tudun Hayin Kwarin-Misau, da ke yankin Ƙaramar Hukumar Akko
An ƙayyade maki da shekarun shiga jami’a a Nijeriya An ceto mutum 6 daga hannun masu garkuwa a KebbiRundunar ta ce an kama Misba’u Adamu mai shekaru 25 dan asalin garin Alkaleri na Jihar Bauchi da Adamu Ibrahim mai shekaru 28, daga Karamar Hukumar Garko ta Jihar Kano.
A lokacin binciken, waɗanda ake zargin sun amsa laifin satar babura guda biyu a gidan wani Mohammed Usman da misalin karfe 4 na Asuba a ranar 6 ga Yuli, 2025.
Baburan sun haɗa da Qlink Cassie mai lamba ABC 484 WN da Hero Hunter mai lamba GME 36 QL.
A sanarwar, rundunar ’yan sandan ta kiyasta darajar baburan kan Naira miliyan 1.8 wadanda aka gano a gidan wani abokin huldarsu da ake kira Babangida.
A wani labarin na daban, rundunar ta ce wani mutum ya tsere ya bar babur kirar Jincheng Kasea mai lamba DKU 099 UK a Wuro Birji yayin da ‘yan sanda ke sintiri da misalin karfe 1 na dare.
Rundunar ta ce tana ci gaba da kokarin gano masu laifin da kuma mamallakin babur ɗin da aka tsinta.
Ta kuma jaddada kudirinta na kare rayuka da dukiyoyin jama’a tare da kira da su ci gaba da ba da bayanai masu amfani.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Babura Barayi jihar Gombe
এছাড়াও পড়ুন:
Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar
“Sauran motocin da ke cikin ayarin, ciki har da wacce ke ɗauke da shugaban majalisar, da ƙyar suka iya tsayawa wanda tsakaninsu mitoci kaɗan ne daga wurin da haɗarin ya afku,” in ji wani ganau.
Majiyoyin tsaro sun tabbatar da cewa, an garzaya da jami’an ‘yansandan da suka samu raunuka zuwa babban asibitin Gumel a sume amma daga baya sun farfaɗo.
Da yake magana kan lamarin, mataimakin shugaban majalisar, Aqeel Akilu, ya yi godiya ga Ubangiji cewa, ba a rasa rayuka ba.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp