Aminiya:
2025-11-03@10:55:42 GMT

An kama ɓarayin babura a Gombe

Published: 9th, July 2025 GMT

Rundunar ‘yan sandan Jihar Gombe ta cafke mutane biyu da ake zargi da satar babura wadanda ta ƙwato babura biyu a hannunsu hadi da wani wanda aka tsinta a lokacin sintiri.

Kakakin rundunar, DSP Buhari Abdullahi, ya ce an gudanar da samamen ne bisa bayanan sirrin da aka samu daga wani mai kishin ƙasa, wanda ya kai jami’an Operation Hattara har zuwa wata maɓoyar ɓata gari a Tudun Hayin Kwarin-Misau, da ke yankin Ƙaramar Hukumar Akko

An ƙayyade maki da shekarun shiga jami’a a Nijeriya An ceto mutum 6 daga hannun masu garkuwa a Kebbi

Rundunar ta ce an kama Misba’u Adamu mai shekaru 25 dan asalin garin Alkaleri na Jihar Bauchi da Adamu Ibrahim mai shekaru 28, daga Karamar Hukumar Garko ta Jihar Kano.

A lokacin binciken, waɗanda ake zargin sun amsa laifin satar babura guda biyu a gidan wani Mohammed Usman da misalin karfe 4 na Asuba a ranar 6 ga Yuli, 2025.

Baburan sun haɗa da Qlink Cassie mai lamba ABC 484 WN da Hero Hunter mai lamba GME 36 QL.

A sanarwar, rundunar ’yan sandan ta kiyasta darajar baburan kan Naira miliyan 1.8 wadanda aka gano a gidan wani abokin huldarsu da ake kira Babangida.

A wani labarin na daban, rundunar ta ce wani mutum ya tsere ya bar babur kirar Jincheng Kasea mai lamba DKU 099 UK a Wuro Birji yayin da ‘yan sanda ke sintiri da misalin karfe 1 na dare.

Rundunar ta ce tana ci gaba da kokarin gano masu laifin da kuma mamallakin babur ɗin da aka tsinta.

Ta kuma jaddada kudirinta na kare rayuka da dukiyoyin jama’a tare da kira da su ci gaba da ba da bayanai masu amfani.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Babura Barayi jihar Gombe

এছাড়াও পড়ুন:

Majalisar Karamar Hukumar Bubura Ta Kai Tallafin Kayayyakin Abinci Cibiyar Gyaran Hali

Daga Usman Mohammed Zaria

 

Majalisar Ƙaramar Hukumar Babura ta Jihar Jigawa ta bayar da tallafin abinci ga fursunonin cibiyar gyaran hali ta Babura a matsayin wani ɓangare na ayyukan jin ƙai na majalisar.

Yayin ziyarar, Alhaji Hamisu Muhammad Garu ya bayyana cewa, wannan taimako ya biyo bayan lura da bukatun fursunonin yayin da ya kai ziyara ta duba cibiyar a baya.

A cewarsa, manufar bayar da tallafin ita ce don tallafa musu wajen kyautata rayuwarsu da kuma karfafa musu gwiwa su zama mutane nagari bayan sun fito daga gidan gyaran hali.

A nasa jawabin, jami’in da ke kula da cibiyar gyaran hali ta Babura, ASP Muhammad Ali, ya gode wa shugaban ƙaramar hukumar bisa wannan karamci, yana mai cewa taimakon ya zo ne a lokacin da ake matuƙar buƙata.

A yayin hudubarsa ga fursunonin, Babban Limamin Babura, Imam Salisu Aliyu, ya shawarce su da su nemi gafarar Allah, su kuma kara kusanci gare Shi, tare da rungumar canji mai kyau.

Kayan tallafin da aka bayar sun haɗa da buhunan masara, gero, shinkafa, garin rogo, man gyada, sinadaran dandano, gidan sauro da maganin kwari.

Manyan baƙin da suka raka shugaban ƙaramar hukumar a lokacin ziyarar sun haɗa da Hakimin Babura, Sarkin Bai Ringim, Alhaji Muhammad Nata’ala Mustapha, jami’in ‘yan sanda mai kula da yankin, CSP Abdu Jinjiri, da jami’in Hukumar Tsaro ta Civil Defence, CSC Sunusi Usman Chamo, da sauransu.

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Majalisar Karamar Hukumar Bubura Ta Kai Tallafin Kayayyakin Abinci Cibiyar Gyaran Hali
  • Kisan Kiristoci: Ba zan yaƙi ƙasar iyayena kan labaran ƙarya ba — Sojan Amurka
  • Gwamna Namadi Ya Bada Motocin Aiki Goma Ga Rundunar ‘Yan Sanda
  • ‘An Kashe Masu Zanga-zanga Akalla 500 a Tanzania’
  • Gwamnatin Jigawa Ta Bada Motocin Aiki Goma Ga Rundunar ‘Yan Sanda
  • Ministan Wajen Malawi: Tsarin Ci Gaban Kasar Sin Ya Samar Da Darussa Ga Kasashe Masu Tasowa
  • Rundunar Sojin Nijeriya Ta Shirya Wa Janar Musa Faretin Gama Aiki
  • Ƴansanda Sun Kama  Wani Mai Wasa Da Bindiga AK-47 A Cikin Wani Bidiyo A Adamawa
  • Kifewar Kwalekwale: Gwamnan Gombe Ya Jajanta Wa Al’ummar Nafada Kan Mutuwar Matasa Biyar
  • An raba wa iyalan jami’an ’yan sandan da suka rasu a bakin aiki a Borno N63.4m