Aminiya:
2025-11-03@02:01:51 GMT

‘Abin da zai sa APC ba za ta taɓa mantawa da Ganduje ba’

Published: 9th, July 2025 GMT

Aminu Dahiru Ahmad, hadimin tsohon shugaban jam’iyar APC na kasa, Abudllahi Umar Ganduje, ya ce jam’iyyar za ta gane ta yi kuskure kan saukarsa daga shugabancin.

A wata doguwar wasika da ya wallafa a shafinsa na Facebook, ya bayyana takaicinsa kan rashin nuna wa Ganduje halasci, duk da irin ci gaban da ya kawo jam’iyar wanda ya ce ba a taba samun makamancinsa ba.

“Tarihin APC ba zai manta da Ganduje ba — Shi ya kai ta matsayin da take kai yanzu,” inji shi.

Gwamnatin Tinubu na shirya mana zagon ƙasa — ADC An ƙayyade maki da shekarun shiga jami’a a Nijeriya

Aminu ya ba da misali da yadda aka dinga tururuwar shiga APC a lokacin mulkin Ganduje da kuma yadda Gwamnoni suka dinga sauya sheka, wanda ya ce ko hakan ya isa ya nuna kwarewarsa a fagen siyasa.

“A lokacinsa ne karon farko da wata jam’iyyar siyasa a Najeriya ta ga cancantar samar da wata dama da nufin magance matsalar shigar matasa a harkokin siyasa.”

A wani sakon da ya wallafa kafin wasikar, ya ce za su rama biki idan lokaci ya yi, kuma a nan ne za a gane Ganduje shi ne rufin asirin APC.

“Tinubu ya mana rauni sau daya, sau biyu, har sau uku. Allah Ya kai mu ranar ramuwa, ranar da za su gane cewa shi ne rufin asirinsu,” in ji shi.

A bayan nan ne dai tsohon gwamnan na Kano, Ganduje ya ajiye muƙaminsa na shugabancin jam’iyyar APC.

Duk da yake Ganduje ya ce rashin lafiya ce ta sa ya yi murabus, wasu majiyoyi sun bayyana cewa rikicin siyasa a cikin jam’iyyar ne suka tilasta masa ajiye muƙamisa.

Ganduje ya zama Shugaban APC a watan Agustan 2023, a lokacin da jam’iyyar ke fama da rikicin cikin gida.

উৎস: Aminiya

এছাড়াও পড়ুন:

Kotu ta tsige dan majalisar da ya sauya sheka zuwa APC

Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja ta tsige dan majalisar wakilai, Abubakar Gummi daga kujerarsa saboda sauya sheka daga jam’iyyar PDP zuwa APC.

Gummi yana wakiltar mazabar Gummi/Bukkuyum ta Jihar Zamfara a majalisar wakilai.

An raba wa iyalan jami’an ’yan sandan da suka rasu a bakin aiki a Borno N63.4m An sake kama shi a cikin ’yan fashi kwana 5 da fitowa daga kurkuku

Mai shari’a Obiora Egwuatu ne, ya yanke hukuncin, inda ya umarci kakakin majalisar wakilai, Tajudeen Abbas, da ya daina amincewa da Gummi a matsayin dan majalisar da ke wakiltar mazabar Gummi/Bukkuyum.

Haka kuma ya umarci hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) da ta shirya sabon zabe cikin kwanaki 30 domin cike gurbin kujerar dan majalisar.

Jam’iyyar PDP tare da shugaban ta na jihar Zamfara, Jamilu Jibomagayaki, ne suka shigar da karar dan majalisar.

Sun ce bai dace Gummi ya ci gaba da zama a kujerar ba bayan barin jam’iyyar da ta tsayar da shi takara.

Gummi, ta bakin lauyansa ya ce ya fice daga PDP ne saboda rikicin cikin gida da jam’iyyar ke fama da shi a matakin kasa da kuma a mazabarsa.

Amma kotu ta yi watsi da wannan hujjar, inda ta bayyana cewa babu takaddama da za ta ba shi damar ya sauya sheka.

A hukuncin da ya yanke, Mai shari’a Egwuatu ya ce ’yan siyasa dole su mutunta zabin jama’ar da suka kada musu kuri’a a karkashin jam’iyyar da ta tsayar da su takara.

Ya ce doka ba ta yadda da dan siyasa ya bar jam’iyyar da ta taimaka masa wajen lashe zabe sannan ya koma wata jam’iyya ba tare da ajiye mukaminsa ba.

Ya kara da cewa kuri’un da aka kada don dan takarar na jam’iyya ne, ba nasa ne na kashin kansa ba.

“Idan mutum yana son sauya sheka, ka da ya dauki amanar jama’ar da ta zabe shi ya tafi da ita,”  in ji alkalin.

Kotu ta kuma umarci Gummi da ya daina karbar albashi da wasu hakkoki a matsayin dan majalisa, tare da mayar da duk kudaden da ya karba daga ranar 30 ga watan Oktoba, 2024, zuwa ranar da aka yanke hukuncin.

Haka kuma, ya gabatar da hujjar mayar da kudaden ga kotu cikin kwanaki 30.

Mai shari’a Egwuatu ya kuma ci Gummi tarar Naira N500,000, domin biyan PDP kudaden da ta kashe wajen shigar da kara.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • 2027: Yadda Gwamnoni Suka Yi Fatali Da Mataimakansu Wajen Zaɓo Waɗanda Za Su Gaje Su
  • IAEA : Babu wata shaida da ke nuna cewa Iran na kera makaman nukiliya
  • Rikicin PDP: Tsagin Wike ya dakatar da Damagum
  • PDP ta dakatar da Anyanwu da wasu ’yan tsagin Wike
  • PDP ta dakatar da Anyanwu da wasu da ke da alaƙa da Wike
  • Sharrin son auren Mai Wushirya aka yi min — Mansura Isa
  • Kofin kofi mafi tsada a duniya ya shiga kasuwa a kan Naira miliyan 1.5m
  • Za mu ci gaba da shirye-shiryen babban taronmu — PDP
  • Kotu ta tsige dan majalisar da ya sauya sheka zuwa APC
  • Allah Ya Kai Manzon Allah (SAW) Muƙami Na Babban Yabo A Cikin Komai