‘Abin da zai sa APC ba za ta taɓa mantawa da Ganduje ba’
Published: 9th, July 2025 GMT
Aminu Dahiru Ahmad, hadimin tsohon shugaban jam’iyar APC na kasa, Abudllahi Umar Ganduje, ya ce jam’iyyar za ta gane ta yi kuskure kan saukarsa daga shugabancin.
A wata doguwar wasika da ya wallafa a shafinsa na Facebook, ya bayyana takaicinsa kan rashin nuna wa Ganduje halasci, duk da irin ci gaban da ya kawo jam’iyar wanda ya ce ba a taba samun makamancinsa ba.
“Tarihin APC ba zai manta da Ganduje ba — Shi ya kai ta matsayin da take kai yanzu,” inji shi.
Gwamnatin Tinubu na shirya mana zagon ƙasa — ADC An ƙayyade maki da shekarun shiga jami’a a NijeriyaAminu ya ba da misali da yadda aka dinga tururuwar shiga APC a lokacin mulkin Ganduje da kuma yadda Gwamnoni suka dinga sauya sheka, wanda ya ce ko hakan ya isa ya nuna kwarewarsa a fagen siyasa.
“A lokacinsa ne karon farko da wata jam’iyyar siyasa a Najeriya ta ga cancantar samar da wata dama da nufin magance matsalar shigar matasa a harkokin siyasa.”
A wani sakon da ya wallafa kafin wasikar, ya ce za su rama biki idan lokaci ya yi, kuma a nan ne za a gane Ganduje shi ne rufin asirin APC.
“Tinubu ya mana rauni sau daya, sau biyu, har sau uku. Allah Ya kai mu ranar ramuwa, ranar da za su gane cewa shi ne rufin asirinsu,” in ji shi.
A bayan nan ne dai tsohon gwamnan na Kano, Ganduje ya ajiye muƙaminsa na shugabancin jam’iyyar APC.
Duk da yake Ganduje ya ce rashin lafiya ce ta sa ya yi murabus, wasu majiyoyi sun bayyana cewa rikicin siyasa a cikin jam’iyyar ne suka tilasta masa ajiye muƙamisa.
Ganduje ya zama Shugaban APC a watan Agustan 2023, a lokacin da jam’iyyar ke fama da rikicin cikin gida.
উৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
Mutane 8 Sun Mutu A Wani Mummunan Hatsari A Hanyar Lagos
Aƙalla mutane takwas ne suka mutu a wani mummunan hatsarin mota da ya faru a Atura Bus Stop, hanyar Lagos-Badagry, lokacin da wata motar haya ƙirar Mazda mai ɗaukar fasinjoji 16 ta yi taho-mu-gama da wata babbar mota ƙirar DAF. Hukumar LASTMA ta bayyana cewa hatsarin ya faru ne sakamakon gudun wuce sa’a da rashin iya sarrafa mota daga direban motar hayar.
A cikin wata sanarwa, Daraktan Hulɗa da Jama’a na LASTMA, Adebayo Taofiq, ya ce hatsarin ya kasance mai muni matuƙa, inda ya kashe direban motar, yaran moto da sauran fasinjoji shida. Ya ce hatsarin ya jefa al’ummar yankin cikin alhini da ɗimuwa. Jami’an LASTMA, da FRSC, da rundunar ƴansanda da Sojoji daga Ibereko sun gudanar da aikin ceto cikin gaggawa.
Ƴan Nijeriya 85 Za Su Iso Lagos Daga Amurka A Yau Jami’in LASTMA Na Bogi Da Ya Sato Mota Ya Shiga HannuAn ceto mutane takwas da suka jikkata, kuma aka garzaya da su Asibitin Gwamnati da ke Badagry don samun kulawar gaggawa. Adebayo ya bayyana cewa hatsarin ya zama darasi, yana mai jaddada cewa gudu, da rashin kiyayewa da sakacin direbobi na ƙara haddasa irin waɗannan hatsarin a tituna.
Babban Manajan LASTMA, Olalekan Bakare-Oki, ya kai ziyara wurin da hatsarin ya faru, inda ya gargaɗi direbobi su kiyaye gudu da bin dokokin hanya. Ya ce gwamnati ta fara shigar da kayan rage gudu a wuraren da ke da haɗari domin rage yawaitar hatsura. Ya ƙara da cewa dole ne direbobi su nuna kishin ƙasa ta hanyar yin tuƙi cikin hankali da kiyaye lafiyar al’umma.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp