Tawagar Jami’ai Da ‘Yan Kasuwar Ta Tunusiya Ta Gana Da Mataimakin Shugaban kasar Iran
Published: 28th, April 2025 GMT
Tawagar jami’ai da ‘yan kasuwan kasar Tunisiya ta gana da mataimakin shugaban kasar Iran
A yayin ganawarsa da ministan kasuwanci da fitar da kayayyaki na kasar Tunisiya Samir Ben Salem Obeid, mataimakin shugaban kasar Iran na farko na Jamhuriyar Musulunci ta Iran Mohammad Reza Aref ya jaddada cewa: Lokaci ya yi da za a dauki kwararan matakai wajen fadada dangantakar tattalin arziki tsakanin Iran da Tunusiya.
A yayin taron, wanda aka gudanar a ofishinsa tare da halartar jakadan kasar Tunisiya a Iran Imed Rahmouni da tawagar da ke tare da shi, Aref ya bayyana cewa, dangantakar siyasa da ke tsakanin al’ummar Iran da Tunisiya na tafiya cikin wani yanayi mai ma’ana, amma hadin gwiwar tattalin arziki da cinikayya ya kasance kasa da abin da ake bukata, bisa la’akari da dama da karfin da bangarorin biyu ke da shi.
A yayin ganawar, Aref ya tunatar da ziyarar da ya kai birnin Qairawan na kasar Tunusiya shekaru ashirin da suka gabata, lokacin da ya rike mukamin mataimakin shugaban kasar na farko na Jamhuriyar. Ya kara da cewa a lokacin yana jin kamar ya ratsa daya daga cikin garuruwan Khorasan na kasar Iran, yana daukar birnin Qairawan wata alama ce ta hadin kan al’ummar musulmi da alakar al’adu da addini tsakanin Iran da Tunisiya.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Sudan: Makaman ‘Drones’ Sun Kashe Ma’aikatan MDD 6 A Kadugli Na Kurdufan Ta Kudu
Jami’an tsaro na MDD wadanda suke aiki a rundunar (UNISFA) guda 6 ne suka rasa rayukansu a jiya Asabar a wani harin da aka kaiwa sansaninsu a lardin Kurdufan da kudu a kasar Sudan.
Shafin yanar gizo na Labarai ‘Sudan Tribune’ ya nakalto gwamnatin kasar Sudan tana aza laifin kai hare-haren kan kungiyar RSF ta yan tawaye a yankin. Amma RSF ta musanta zargin.
Dakarun MDD ta (UNISFA) dai suna tabbatar da zaman lafiya a yankin Abiea da sudan da kuma sudan ta kudu suke takaddama a kansu ne tun shekara ta 2011. Kuma wannan shi ne hari na farko kai tsaye kan dakarun MDD a yankin tun lokacinda aka fara yakin basabsa a kasar ta Sudan fiye da shekaru 2 da suka gabata. Wato tun wata Afrilun shekara ta 2023.
Labarin ya kara da cewa makaman Drones, watojiragen yakin da ake sarrafasu daga nesa guda uku ne suka kai hare-hare kan sansanin sojojin na MDD inda suka kashe mutane 6 daga kasar Bangladesh suka kuma lalata wata tashar ajiyar makamashi.
Labarin ya kara da cewa mutane biyu daga cikin wadanda suka ji rauni suna cikin mummunan hali. Ya zuwa yanzu dai Majalisar bata zargi wani bangare da kai hare-haren ba. Mazauna garin Kadugli inda aka kai harin, sun bayyana cewa mayakan kungiyar SPLM-N karkashin Abdulaziz Al-Hilu sun yi barin wuta a kan garin a jiya Asabar. Bayan yiwa garin kawanyana na watanni.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Eritrea Ta Fice Daga Kungiyar Raya Kasahsen Gabacin Afrika (IGAD) December 14, 2025 َA Yau Ne Za’a Gudanar Da Taron Koli Na Kungiyar ECOWAS A Birnin Abuja December 14, 2025 Iran Ta karbi Bakunci Taron Kasashen Dake Makwabtaka Da Afghanistan Da Rasha December 14, 2025 Isra’ilaTa Kashe Wani Bafalasdine Matashi A Wani Hari Da Takai A Arewacin Kogin Jodan. December 14, 2025 Shuwagabannin Majalisar Kasar Iran Da Na Ethiopia Sun Gudanar Da Taron Manema Labarai December 14, 2025 Ghana Ta Kori Wasu Yahudawa Guda 3 Don Mayar Da Martani December 14, 2025 Araghchi ya bukaci Amurka ta girmama al’ummar Iran da gwamnatinta December 14, 2025 Dan bindiga ya kashe sojojin Amurka biyu da wani farar hula a Siriya December 14, 2025 Mutum biyu sun mutu a harbin bindiga a Jami’ar Brown ta Amurka December 14, 2025 Shugabannin kasashen (ECOWAS) na taro a Abuja December 14, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci