Tawagar Jami’ai Da ‘Yan Kasuwar Ta Tunusiya Ta Gana Da Mataimakin Shugaban kasar Iran
Published: 28th, April 2025 GMT
Tawagar jami’ai da ‘yan kasuwan kasar Tunisiya ta gana da mataimakin shugaban kasar Iran
A yayin ganawarsa da ministan kasuwanci da fitar da kayayyaki na kasar Tunisiya Samir Ben Salem Obeid, mataimakin shugaban kasar Iran na farko na Jamhuriyar Musulunci ta Iran Mohammad Reza Aref ya jaddada cewa: Lokaci ya yi da za a dauki kwararan matakai wajen fadada dangantakar tattalin arziki tsakanin Iran da Tunusiya.
A yayin taron, wanda aka gudanar a ofishinsa tare da halartar jakadan kasar Tunisiya a Iran Imed Rahmouni da tawagar da ke tare da shi, Aref ya bayyana cewa, dangantakar siyasa da ke tsakanin al’ummar Iran da Tunisiya na tafiya cikin wani yanayi mai ma’ana, amma hadin gwiwar tattalin arziki da cinikayya ya kasance kasa da abin da ake bukata, bisa la’akari da dama da karfin da bangarorin biyu ke da shi.
A yayin ganawar, Aref ya tunatar da ziyarar da ya kai birnin Qairawan na kasar Tunusiya shekaru ashirin da suka gabata, lokacin da ya rike mukamin mataimakin shugaban kasar na farko na Jamhuriyar. Ya kara da cewa a lokacin yana jin kamar ya ratsa daya daga cikin garuruwan Khorasan na kasar Iran, yana daukar birnin Qairawan wata alama ce ta hadin kan al’ummar musulmi da alakar al’adu da addini tsakanin Iran da Tunisiya.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Yadda na hannun daman ’Yar’Adua ya yi tuggun hana ni zama shugaban ƙasa — Jonathan
Tsohon Shugaban Ƙasa, Goodluck Jonathan, ya bayyana wasu abubuwan da suka faru biyo bayan rashin lafiyar marigayi Shugaba Umaru Musa ’Yar’Adua, waɗanda suka haddasa ruɗani a faɗin Najeriya.
Jonathan, ya ce ya shirya ya mutu a fadar shugaban ƙasa maimakon ya bar muƙaminsa a lokacin da aka shiga ruɗani saboda rashin dawowar ’Yar’Adua.
HOTUNA: Yadda aka yi jana’izar Aminu Ɗantata a Kano Za a binne Aminu Ɗantata a Madina — IyalansaA wata hira da aka yi da shi a Rainbow Book Club, Jonathan ya bayyana cewa Yar’Adua ya rubuta wasiƙa don miƙa masa mulki, amma wani na hannun damar shugaban ƙasa ya ɓoye wasiƙar, bai miƙa ta ga majalisa ba.
“Wannan wasiƙar an rubuta ta. Amma wanda aka bai wa, ba zan faɗi sunansa ba, ya ƙi ya miƙa ta ga majalisar ƙasa,” in ji Jonathan.
A ƙarshen shekarar 2009, ’Yar’Adua ya tafi ƙasashen waje neman magani ba tare da sanar da majalisa ba ko kuma miƙa mulki ga Jonathan kamar yadda doka ta tanada.
Wannan lamari ya jefa ƙasar cikin rikicin siyasa da na kundin tsarin mulki.
Jonathan, wanda shi ne mataimakin shugaban ƙasa a lokacin, ya ce ƙasar ta shiga wani mawuyacin hali da rabuwar kai.
“Ƙasar ta shiga tashin hankali. Rikicin Arewa da Kudu, Kirista da Musulmi ya yi tsanani. Kowace rana ina jin jita-jitar juyin mulki,” in ji shi.
Ya kuma bayyana cewa akwai fahimtar juna amma ba a rubuta cewa Arewa za ta ci gaba da mulki na tsawon shekaru takwas bayan Obasanjo daga Kudu ya kammala mulkinsa.
Amma rashin lafiyar ’Yar’Adua ya kawo cikas.
“Rashin lafiyar ce matsala. Wannan ne ya sa har ba su so a bar ni na riƙe muƙamin shugaban ƙasa na wucin gadi,” in ji shi.
Ya ce duk da yake yana gudanar da wasu ayyuka na mataimaki, rashin wasiƙar miƙa mulki ya hana shi zama cikakken shugaban ƙasa.
“Shugaban ƙasa na da manyan nauyi guda biyu. Na farko, kai ne babban jami’in gwamnati, kamar Firaminista, wanda mataimakin shugaban ƙasa zai iya maye gurbinsa.
“Amma ba a samu kwamandan rundunar soji ba, kuma babu wani abu da ake kira kwamanda na wucin gadi,” in ji shi.
Wannan rashin tabbas ne ya sa Majalisar Ƙasa ta yi amfani da “Ƙa’idar Dole” (Doctrine of Necessity) don ba shi ikon zama shugaban ƙasa na wucin gadi a watan Fabrairun 2010.
Jonathan ya tuna irin matsin lambar da ya sha.
Ya ce wasu daga cikin abokansa sun shawarce shi da ya bar fadar shugaban ƙasa saboda tsoron ka da a kashe shi.
“Na tuna wata rana, ina mataimakin shugaban ƙasa, wani abokina ya ce ce, ‘Ka bar gidan gwamnati, ka zo ka kwana a gidan baƙina.’
“Na ce, ‘A’a. Zan kwana a fadar gwamnati. Idan akwai wanda zai kashe ni, to su kashe ni a gidan gwamnati domin ’yan Najeriya su sani an kashe ni a fadar shugaban ƙasa.’”
“Sun san ban aikata laifi ba. Idan na je na kwana a gidanka, a can aka kashe ni, za su fara cewa wasu ’yan Indiya ne suka kawo tuffa suka kashe ni. Ban so a ƙirƙiri irin wannan labari,” in ji shi.
Wannan lokaci na daga cikin mafi muhimmanci a tarihin dimokuraɗiyyar Najeriya.
Daga bisani, Jonathan ya zama cikakken shugaban ƙasa bayan rasuwar ’Yar’Adua a watan Mayun shekarar 2010.