Majalisar Dinkin Duniya ta jaddada wajabcin komawa kan Shirin tsagaita bude wuta a Gaza

Wakiliyar babban sakataren Majalisar Dinkin Duniya na musamman ta jaddada a yau Litinin cewa: Akwai tsananin bukatar komawa ga Shirin tsagaita bude wuta a Gaza.

A lokacin da take ba da shaida a zaman kotun kasa da kasa kan wajabcin da ya hau kan haramtacciyar kasar Isra’ila na kiyaye hakkokin mazaunan yankunan Falasdinawa, ta jaddada wajabcin isar da kayayyakin agajin na gaggawa ga Zirin Gaza, inda ta bayyana cewa: Babban sakataren Majalisar Dinkin Duniya António Guterres na yin duk wani kokari na kawo karshen matsalar jin kai da fararen hula ke fuskanta a yankunan Falasdinawa da aka mamaye da yankunan Falasdinawa da ba a mamaye ba amma suna fuskantar hare-haren wuce gona da iri.

Ta bayyana cewa kin bari a shigar da kayayyakin jin kai na yankunan Falasdinawa tun daga ranar 2 ga watan Maris ya kara ta’azzara wahalhalun jin kai a Gaza, tana mai bayanin cewa hukumomin Majalisar Dinkin Duniya na kokarin samar da muhimman abubuwan da ake bukata domin ci gaba da rayuwar al’ummar Falasdinu.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: Majalisar Dinkin Duniya yankunan Falasdinawa

এছাড়াও পড়ুন:

Farfesa Gumel Ya Zama Sabon Shugaban Jami’ar Tarayya Da Ke Dutse

Daga Usman Muhammad Zaria

Majalisar Gudanarwa ta huɗu ta Jami’ar Tarayya da ke Dutse (FUD) a Jihar Jigawa ta amince da naɗa Farfesa Ahmed Muhammed Gumel a matsayin shugabar jami’ar na huɗu.

Shugaban Majalisar Gudanarwar jami’ar, Farfesa Shuaibu Oba Abdulraheem, ya bayyana cewa an bi tsari mai tsauri da cikakken bincike wajen zaɓen sabon shugaban jami’ar.

A cewarsa, an tantance ’yan takara 2, inda a ƙarshe Farfesa Gumel ya fito a matsayin sabon Shugaban Jami’ar ta FUD.

Farfesa Uba ya taya sabon shugaban jami’ar murna,  tare da yi masa fatan Allah Ya mishi jagora da nasara wajen sauke nauyin da aka dora masa.

A nasa jawabin, sabon Mataimakin Shugaban Jami’ar, Farfesa Ahmad Muhammad Gumel, ya gode wa Allah Madaukakin Sarki bisa zaɓensa a matsayin sabon shugaban jami’ar.

Ya kuma miƙa godiyarsa ga kwamitin haɗin gwiwar zaɓe, Shugaban Majalisar Gudanarwa, shugaban jami’ar mai ci, da dukkan mambobin majalisar jami’ar bisa amincewa da suka nuna masa.

Ya ƙara da cewa zai yi iya ƙoƙarinsa wajen ci gaba da gina nasarorin da shugaban jami’ar mai barin gadi ya samar.

Gidan Rediyon Najeriya ya ruwaito cewa Farfesa Ahmad Mohammed Gumel tsohon ɗalibi ne na Jami’ar Malaya da ke ƙasar Malaysia, inda ya samu digiri na biyu (Master) a fannin Kimiyyar Halittu ta Biotechnology da kuma digiri na uku (Ph.D) a Industrial Biotechnology, tare da ƙwarewa a Biocatalysis da Bioprocess.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ECOWAS ta jaddada aniyar kare dimokuraɗiyya da inganta tsaro a yammacin Afirka
  • Farfesa Gumel Ya Zama Sabon Shugaban Jami’ar Tarayya Da Ke Dutse
  • Shirin kafa ‘Hisbar Ganduje’ ya tayar da ƙura a Kano
  • Sin Ta Yi Kira Da A Gaggauta Tsagaita Bude Wuta A Jamhuriyar Demokradiyyar Kongo 
  • Isra’ila Ta Kai Hari A Kudancin Labanon  A Ci Gaba Da Keta Yarjejeniyar Tsagaita Bude Wuta
  • Iran da Rasha sun jaddada aiwatar da yarjejeniyar hadin gwiwa a tsakaninsu
  • MDD ta amince da wani kuduri da ke neman Isra’ila ta bada damar shigar da agaji a Gaza   
  • Majalisar Dinkin Duniya Za ta Yi Zama Da Bangarorin Da ke Yaki A Sudan
  • Yadda APC Da ADC Ke Amfana Da Rikicin Jam’iyyar PDP
  • Nazarin CGTN: Fahimtar Matsayin Sin Cikin Yanayin Tattalin Arzikin Duniya Na Da Muhimmanci