Majalisar Dinkin Duniya ta jaddada wajabcin komawa kan Shirin tsagaita bude wuta a Gaza

Wakiliyar babban sakataren Majalisar Dinkin Duniya na musamman ta jaddada a yau Litinin cewa: Akwai tsananin bukatar komawa ga Shirin tsagaita bude wuta a Gaza.

A lokacin da take ba da shaida a zaman kotun kasa da kasa kan wajabcin da ya hau kan haramtacciyar kasar Isra’ila na kiyaye hakkokin mazaunan yankunan Falasdinawa, ta jaddada wajabcin isar da kayayyakin agajin na gaggawa ga Zirin Gaza, inda ta bayyana cewa: Babban sakataren Majalisar Dinkin Duniya António Guterres na yin duk wani kokari na kawo karshen matsalar jin kai da fararen hula ke fuskanta a yankunan Falasdinawa da aka mamaye da yankunan Falasdinawa da ba a mamaye ba amma suna fuskantar hare-haren wuce gona da iri.

Ta bayyana cewa kin bari a shigar da kayayyakin jin kai na yankunan Falasdinawa tun daga ranar 2 ga watan Maris ya kara ta’azzara wahalhalun jin kai a Gaza, tana mai bayanin cewa hukumomin Majalisar Dinkin Duniya na kokarin samar da muhimman abubuwan da ake bukata domin ci gaba da rayuwar al’ummar Falasdinu.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: Majalisar Dinkin Duniya yankunan Falasdinawa

এছাড়াও পড়ুন:

Majalisa ta amince da buƙatar Tinubu na karɓo rancen N1.15bn

Majalisar Dattawa ta amince da buƙatar Shugaba Bola Tinubu na karɓo rancen Naira tiriliyan 1.15 domin cike giɓin kasafin kuɗin 2025.

Amincewar ta biyo bayan rahoton da Kwamitin Majalisar Dattawa kan Lamunin Cikin Gida da na Ƙasashen Waje, ƙarƙashin jagorancin Sanata Manu Haruna, ya gabatar.

Matasa 12 sun mutu a turmutsutsun neman aikin soja a Ghana Super Falconets ta lashe gasar WAFU ta ’yan ƙasa da shekaru 20

Ya bayyana cewa kasafin kuɗin 2025 na Naira tiriliyan 59.99 ya bar giɓin naira tiriliyan 1.15 wanda dole ne a cike ta hanyar nemo rancen a cikin gida.

Sanatoci sun amince cewa rancen ya zama dole domin ci gaba da aiwatar da muhimman ayyukan gwamnati da tabbatar da nasarar kasafin kuɗin 2025, musamman ɓangaren manyan ayyuka.

Sai dai sun jaddada muhimmancin yin gaskiya da bayyana bayani kan yadda za a yi amfani da kuɗin.

Wasu sanatocin sun shawarci Ma’aikatar Kuɗi da Ofishin Kula da Lamuni (DMO), da su riƙa bai wa Majalisar Dattawa rahoto lokaci-lokaci kan yadda ake kashe kuɗin da kuma yadda za a biya bashin.

Sun ce hakan zai taimaka wajen kauce wa almundahana da kuma tabbatar da ɗorewar tsarin lamuni na cikin gida.

Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Barau Jibrin, ya yaba wa kwamitin kan yadda suka gudanar da aikinsu a kan lokaci.

Ya tabbatar wa ’yan Najeriya cewa Majalisar Dattawa za ta ci gaba da sanya idanu kan yadda za a yi amfani da rancen domin tabbatar da cewa an yi amfani da shi wajen ci gaban ƙasa.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Jakadan Iran A Majalisar Dinkin Duniya Yace Iran Ba za Ta Taba Mika Wuya Ga Duk Wata Barazana Ba
  • Gaza: Amurka na matsin lamba ga kwamitin tsaro don amincewa da shirin zaman lafiya na Trump
  • AU da MDD, sun karfafa dabarun tabbatar da zaman lafiya da tsaro
  • Kalubalantar Ka’idar “Kasar Sin Daya Tak A Duniya” Tamkar Wasa Da Wuta Ne
  • Wasu kasashen duniya sun nuna damuwa game da tsarin mulkin bayan yakin Gaza
  • Tehran da Ankara sun jaddada muhimmancin zaman lafiya da kwanciyar hankali a yankin
  • Yahudawa sun banka wa masallaci wuta a Yammacin Kogin Jodan
  • Jihar Kwara Ta Jaddada Kudirin Tallafa wa Wadanda Suka Tsira Daga Cin Zarafin Jinsi
  • UNICEF da Abokan Hulɗa Sun Kaddamar da Shirin Wayar da Kai Kan Rijistar Haihuwa a Yankin Gwarzo
  • Majalisa ta amince da buƙatar Tinubu na karɓo rancen N1.15bn