Majalisar Dinkin Duniya Ta Jaddada Wajabcin Komawa Kan Shirin Tsagaita Bude Wuta A Gaza
Published: 28th, April 2025 GMT
Majalisar Dinkin Duniya ta jaddada wajabcin komawa kan Shirin tsagaita bude wuta a Gaza
Wakiliyar babban sakataren Majalisar Dinkin Duniya na musamman ta jaddada a yau Litinin cewa: Akwai tsananin bukatar komawa ga Shirin tsagaita bude wuta a Gaza.
A lokacin da take ba da shaida a zaman kotun kasa da kasa kan wajabcin da ya hau kan haramtacciyar kasar Isra’ila na kiyaye hakkokin mazaunan yankunan Falasdinawa, ta jaddada wajabcin isar da kayayyakin agajin na gaggawa ga Zirin Gaza, inda ta bayyana cewa: Babban sakataren Majalisar Dinkin Duniya António Guterres na yin duk wani kokari na kawo karshen matsalar jin kai da fararen hula ke fuskanta a yankunan Falasdinawa da aka mamaye da yankunan Falasdinawa da ba a mamaye ba amma suna fuskantar hare-haren wuce gona da iri.
Ta bayyana cewa kin bari a shigar da kayayyakin jin kai na yankunan Falasdinawa tun daga ranar 2 ga watan Maris ya kara ta’azzara wahalhalun jin kai a Gaza, tana mai bayanin cewa hukumomin Majalisar Dinkin Duniya na kokarin samar da muhimman abubuwan da ake bukata domin ci gaba da rayuwar al’ummar Falasdinu.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: Majalisar Dinkin Duniya yankunan Falasdinawa
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamnatin Kano Ta Haramta Sabuwar Hisbah Da Ganduje Ke Shirin Ƙirƙirowa
Gwamnatin Jihar Kano ta fitar sanarwar umarnin haramta kafa wa, da ɗaukar aiki da gudanar da duk wata ƙungiyar Hisbah mai zaman kanta a jihar, inda ta dakatar da ƙungiyar Independent Hisbah Fisabilillahi da tsohon gwamnan Kano Abdullahi Umar Ganduje ke shirin Ƙirƙirowa.
Kwamishinan yaɗa labarai ne ya sanar da hakan a taron manema labarai a Kano, yana mai cewa Gwamna Abba Kabir Yusuf ya rattaba hannu kan umarnin ne domin kare zaman lafiya da kuma kare sahihancin Hukumar Hisbah ta Jihar Kano da doka ta kafa.
Dalilin Da Suka Sa Hisbah Ta Dakatar Da Auren Ƴan TikTok A Kano Ƙirƙirar Hisbah Mai Zaman Kanta: Kungiyar Lauyoyi ‘Yan Kano Ta Shigar Da Tinubu ƘaraUmarnin ya bayyana cewa duk wani yunƙuri na ɗaukar aiki, da horarwa ko tura mutane don kafa wata Hisbah ta daban haramun ne, kuma ba shi da inganci a doka. Gwamnati ta umurci jami’an tsaro su dakatar da duk wani motsi da kuma bincikar masu ɗaukar nauyin ƙungiyar.
ADVERTISEMENTGwamnatin ta kuma gargadi jama’a da su guji shiga ko tallafa wa ƙungiyar da aka haramta, tana mai cewa duk wanda ya bin umarnin zai fuskanci hukunci bisa dokokin jihar kuma umarnin ya fara aiki nan take.
ShareTweetSendShare MASU ALAKA