’Yan Najeriya na iya fuskantar karin farashin man fetur bayan da Matatar Man Dangote ta bayyana cewa ta daina sayar wa ’yan kasuwa man fetur a kudin Naira.

Matatar, wacce ke siyan danyen mai da Naira bisa yarjejeniyar gwamnati, yanzu ta koma sayan danyen mai da dalar Amurka.

An kirkiro yarjejeniyar siyan danyen mai da Naira ne domin rage tsadar mai.

Bisa ga wannan yarjejeniya, Kamfanin Man Fetur na Kasa (NNPCL), yana da alhakin samar wa Matatar Dangote gangar danyen mai a kowace rana 385,000, domin ta tace ta kuma sayar da shi a farashin Naira.

Sai dai rashin cika alkawari daga NNPCL ya sa yarjejeniyar ta gaza dorewa.

Wata majiya ta bayyana cewa, “NNPCL bai cika alkawarin da ya dauka ba, hakan ya sa Dangote ba shi da wani zabi illa ya fara siyan danyen mai da dala.

“Yanzu matatun cikin gida sai sun samu dala kafin su iya ci gaba da aiki.”

Matatar Dangote ta ce, “Dole ne mu daidaita kudin sayar da kayayyakinmu da kudin da muke siyan danyen mai. Yarjejeniyar Naira ba ta samar da isasshen danyen mai da zai iya kula da aikinmu ba.”

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: siyan danyen mai

এছাড়াও পড়ুন:

NAJERIYA A YAU: Yadda Za A Dama Da Matan Arewa A Fannin Kimiyya

More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba

Mata a Arewacin Najeriya na fuskantar kalubale da dama a fannin karantar kimiyya.

Akwai darussan da a mafi yawan lokuta ba mata kadai ba, har da mazan na kaurace musu.

NAJERIYA A YAU: Matakan Da Muke Dauka Don Karfafawa ’Yan Najeriya Kwarin Gwiwar Kada Kuri’a —INEC DAGA LARABA: Abubuwan da ya kamata yara su yi yayin hutun makaranta

Shirin Najeriya a Yau ya yi nazari  ne kan dalilan da suka sa matan Arewacin Najeriya ke tsoron karantar ilimin kimiyya.

Domin sauke cikakken shirin, latsa nan

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • NNPCL ya sake haƙa sabbin rijiyoyin man fetur 4 a Kolmani
  • Kamfanin NNPCL ya sake haka sabbin rijiyoyin man fetur 4 a Kolmani
  • Dalilan Da Suka Sa Canada Ta Goyi Bayan Kafa Kasar Falasɗinu
  • NAJERIYA A YAU: Tinubu ya yi wa Arewa adalci a ayyuka da mukamai — Bayo Onanuga
  • Gwamna Namadi Ya Kaddamar da Tallafin Miliyoyin Naira Ga Ƴan NURTW da Mahauta a Jigawa
  • Matatar Mai Ta Fatakwal Ba Ta Siyarwa Ba Ce – NNPC
  • Amincewa Da Kasar Falasɗinu: Birtaniya Ta Gindaya Wa Isra’ila Sharuɗɗa
  • Nijar da Rasha sun ƙulla yarjejeniyar makamashin nukiliya
  • NAJERIYA A YAU: Yadda Za A Dama Da Matan Arewa A Fannin Kimiyya
  • Ana Ci Gaba Da Habaka Karfin Kudin Kasar Sin Tun Daga Shekarar 2021