Sojojin kasar Yeman sun bada sanarwan cilla makamai masu linzami kan tashar jiragen sama ta Bengerion a birnin Tel’aviv na HKI a daren jiya laraba don tallafawa falasdinawa a gaza wadanda sojojin HKI suke kashewa bayan yi masu kofar rago ta shigo da abinci da abinsha cikin yankin na kimani wata guda.

Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto Burgedia Janar Yahya Saree, kakakin sojojin kasar na fadar haka a safiyar yau Alhamis ya kuma kara da cewa sojojin sun yi amfani da makami mai linzami samfurin Falasdin-2 mai saurin fiye da saurin sauti, wato Hypersonic don kai wannan harin.

Tashar jiragen sama mafi girma a HKI dai ita ce ta Bengerion dake tazarar kilomita 20 daga birnin Tel’aviv. Saree ya kara da cewa makamin ya fada kan inda aka nufa da shi a tashar tare da nasara.

A wani labarin kuma sojojin kasar ta Yemen sun bada labarin kakkabo jirin leken asiri da kuma yaki na kasar Amurka wanda ake kira MQ-9 a sararin samaniyar kasar Yemen , kuma shi ne 20 da suka sauke tun bayan fara yakin Tufanul Aksa a cikin watan Octoban shekara ta 2023.

Har’ila yau tun ranar Abasar da ta gabata ne sojojin kasar ta Yemen suna maida martani kan sojojin Amurka da suke tekun red sea da irin wadannan makamai.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: sojojin kasar

এছাড়াও পড়ুন:

Hukumar DSS Ta Kama Wani Kan Zargin Ƙerawa Da Rarraba Makamai A Filato

 

“An kama Abubakar da hannu dumu-dumu da wasu abubuwan fashewa, sinadarai, da kayan aiki, waɗanda jami’an DSS suka kwace,” in ji majiyar.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Labarai A Zamanantar Da Tsarin Karatu A Makarantun Koyar Da Ilimin Addinin Musulunci – ECOWAS November 16, 2025 Labarai APOSUN Ta Jaddada Aniyarta Na Daƙile Hada-hadar Haramtattun Kuɗaɗe November 16, 2025 Labarai NNPP Tana Da Ƙwarin Gwiwar Riƙe Kano Da Lashe Jihohin Arewa A Zaɓen 2027 – Ajuji November 16, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Lebanon: Mutum Daya Ya Yi Shahada Sanadiyyar Harin Sojojin “Sahayoniya A Garin Bint-Jubail
  • Sojojin Najeriya Sun Karyata Cewa “ISWAP” Ta Kashe Wani Babban Jami’i Mai Mukamin  Birgediya
  • An Sanya Hannu Kan Yarjejeniyoyin Cinikayya Na Biliyoyin Kudi Yayin Baje Kolin CHTF Na Kasar Sin
  • Masu ibadar Umara 42 sun mutu a hatsarin mota a hanyar zuwa Makka
  • Sojojin HKi Sun Kashe Wasu Falasdinawa Guda 2 A Sansanin Yan Gudun Hijira
  • Ansarullah Ta Yi Allah Wadai Da Sabunta Takunkumin MDD Kan Yemen
  • Isra’ila Ta Kai Wa Sojojin MDD Hari A Kasar Lebanon
  • Hukumar DSS Ta Kama Wani Kan Zargin Ƙerawa Da Rarraba Makamai A Filato
  • Meke Kawo Yanke Hukunce-hukunce Masu Karo Da Juna Daga Kotuna?
  • Iran : kasantuwar sojojin Amurka a yankin Caribbean barazana ce ga zaman lafiyar duniya