Sojojin kasar Yeman sun bada sanarwan cilla makamai masu linzami kan tashar jiragen sama ta Bengerion a birnin Tel’aviv na HKI a daren jiya laraba don tallafawa falasdinawa a gaza wadanda sojojin HKI suke kashewa bayan yi masu kofar rago ta shigo da abinci da abinsha cikin yankin na kimani wata guda.

Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto Burgedia Janar Yahya Saree, kakakin sojojin kasar na fadar haka a safiyar yau Alhamis ya kuma kara da cewa sojojin sun yi amfani da makami mai linzami samfurin Falasdin-2 mai saurin fiye da saurin sauti, wato Hypersonic don kai wannan harin.

Tashar jiragen sama mafi girma a HKI dai ita ce ta Bengerion dake tazarar kilomita 20 daga birnin Tel’aviv. Saree ya kara da cewa makamin ya fada kan inda aka nufa da shi a tashar tare da nasara.

A wani labarin kuma sojojin kasar ta Yemen sun bada labarin kakkabo jirin leken asiri da kuma yaki na kasar Amurka wanda ake kira MQ-9 a sararin samaniyar kasar Yemen , kuma shi ne 20 da suka sauke tun bayan fara yakin Tufanul Aksa a cikin watan Octoban shekara ta 2023.

Har’ila yau tun ranar Abasar da ta gabata ne sojojin kasar ta Yemen suna maida martani kan sojojin Amurka da suke tekun red sea da irin wadannan makamai.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: sojojin kasar

এছাড়াও পড়ুন:

Ribadu ya jagoranci tawaga zuwa Amurka don ƙaryata zargin yi wa Kiristoci kisan ƙare dangi

Mai Bai Wa Shugaban Ƙasa Shawara kan Harkokin Tsaro, Nuhu Ribadu, ya jagoranci wata tawagar gwamnati zuwa Amurka domin mayar da martani kan zargin yi wa Kiristoci kisan ƙare dangi a Najeriya.

Wannan zargi ya samo asali ne bayan mataimakin shugaban ƙasa Kashim Shettima, ya nuna goyon bayansa wajen kafa ƙasashe biyu tsakanin Isra’ila da Gaza.

Wardley ya zama zakaran damben boksin na duniya Hakimi ya lashe kyautar gwarzon ɗan ƙwallon Afirka na bana

A farkon wannan watan ne Shugaban Amurka, Donald Trump, ya ayyana Najeriya cikin jerin ƙasashen matsala ta musamman.

Sannan Trump ya umarci wasu ’yan majalisar Amurka, ciki har da Ɗan Majalisa Riley Moore da su binciki lamarin.

Duk da ƙoƙarin da Najeriya ta yi na bayyana haƙiƙanin abin da ke faruwa bai sa wasu jami’an Amurka sun sauya ra’ayi ba.

Daga cikin tawagar akwai: Bianca Ojukwu, Ƙaramar Ministar Harkokin Waje; Kayode Egbetokun, Sufeto Janar na ’Yan Sanda; Lateef Olasunkami Fagbemi, Antoni-Janar na Ƙasa; Janar Olufemi Olatunbosun Oluyede, Shugaban Ma’aikatan Tsaro; da Laftanar Janar E.A.P. Undiendeye, Shugaban Leƙen Asirin Tsaro na Ƙasa.

Sauran sun haɗa da Idayat Hassan, Jakada Ibrahim Babani, Daraktan Hulɗar Ƙasashen Waje a ONSA; Jakada Nuru Biu, Mai Riƙe da Muƙamin CDA na Ƙasashen Waje a Ma’aikatun Jakadancin Najeriya; da Paul Alabi, daga Sashen Siyasa da Tattalin Arziƙi a Ofishin Jakadancin Najeriya.

A ranar Talata, an gayyaci fitacciyar mawakiyar Amurka, Nicki Minaj zuwa zauren Majalisar Ɗinkin Duniya domin gabatatar da jawabi, inda ita ma ta nemi a kai wa Kiristocin Najeriya ɗauki.

Sai dai ba a bai wa Najeriya damar halartar taron ba wanda ya gudana a Birnin New York, lamarin da ya ƙara tayar da ƙura.

Wakilin Najeriya a Majalisar Ɗinkin Duniya, Syndoph Endoni, ya ce hakan tamkar “aske mana kai ba tare da mu ba.”

A ranar Laraba, tawagar Najeriya ta gana da Ɗan Majalisar Amurka Moore domin tattaunawa kan matsalolin tsaro a ƙasar da ƙoƙarin gwamnati ke yi na shawo kan tashe-tashen hankula.

Bayan ganawa da wakilan gwamnatin Najeriya, Moore ya ce ya fahimci yadda abubuwan suke.

Moore ya ce: “Yau na yi magana ta gaskiya, a buɗe kuma mai amfani da manyan jami’an gwamnatin Najeriya game da mummunan tashin hankali da bazaranar da Kiristoci ke fuskanta a faɗin Najeriya.

“Na bayyana a fili cewa dole Amurka ta ga an ɗauki ƙwararan matakai da za su tabbatar da cewa Kiristoci ba su fuskanci tashin hankali, zalunci, ko kisa saboda ba saboda sun gaskata Yesu Almasihu.”

Ya kara da cewa: “Mun shirya mu yi aiki tare da ’yan Najeriya domin taimaka musu su yaƙi ta’addancin da Boko Haram, ISWAP, da makiyaya Fulani ke aikatawa musamman a kan Kiristoci a yankin Arewa maso Gabas da Kudancin Kaduna da sauran yankunan Najeriya.”

Haka kuma Moore ya ce: “Gwamnatin Najeriya na da damar ƙarfafa dangantakarta da Amurka.

“Shugaba Trump da Majalisa sun haɗa kai kuma suna da niyyar kawo ƙarshen tashin hankalin da Kiristoci ke fuskanta da kuma karya ƙungiyoyin ta’addanci a Najeriya.

“Ina kira ga ’yan Najeriya su yi aiki tare da mu cikin haɗin kai domin magance wannan babban lamari.”

Har zuwa lokacin haɗa wannan rahoto, tawagar Najeriya ba ta fitar da sanarwarta kan wannan ziyara ba.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  •  Madagascar: An Bayyana Jadawalin Farko Na Gwamnatin Rikon-Kwarya Da Kuma Manyan Zabuka
  • Yan Majalisar Dokokin Amurka Sun Sami Rarrabuwar Kai Dangane Da ‘Keshe Kiristoci A Najeriya’
  • Kasar Ukraine Ta Ki Amincewa Da Sabon Shirin Amurka Na Kawo Karshen Yaki A Kasar
  • Sojoji sun bar makarantar Maga kafin ’yan bindiga su kai hari — Gwamna Kebbi 
  • CORET, ECOWAS Sun Hada Matasa Da Wasu Abokan Hulda Don Inganta Kiwo Da Madara
  • Najeriya ta ɗora alhakin taɓarɓarewar harkokin tsaronta kan Amurka
  • Hukumar Kula Da Jiragen Sama Ta Najeriya Ta ci Tarar Kamfanin Jiragen Sama Na Qatar
  • Amurka ta Shawarci Ukraine ta amince da yankunan da Rasha ta mamaye mata
  • Sudan ta yaba da kokarin Amurka da Saudiyya na kawo karshen rikicin kasar
  • Ribadu ya jagoranci tawaga zuwa Amurka don ƙaryata zargin yi wa Kiristoci kisan ƙare dangi