Sojojin Yamen Sun Cilla Makamai Masu Linzami Kan Tashar Jiragen Sama Na Bengerion A HKI
Published: 20th, March 2025 GMT
Sojojin kasar Yeman sun bada sanarwan cilla makamai masu linzami kan tashar jiragen sama ta Bengerion a birnin Tel’aviv na HKI a daren jiya laraba don tallafawa falasdinawa a gaza wadanda sojojin HKI suke kashewa bayan yi masu kofar rago ta shigo da abinci da abinsha cikin yankin na kimani wata guda.
Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto Burgedia Janar Yahya Saree, kakakin sojojin kasar na fadar haka a safiyar yau Alhamis ya kuma kara da cewa sojojin sun yi amfani da makami mai linzami samfurin Falasdin-2 mai saurin fiye da saurin sauti, wato Hypersonic don kai wannan harin.
Tashar jiragen sama mafi girma a HKI dai ita ce ta Bengerion dake tazarar kilomita 20 daga birnin Tel’aviv. Saree ya kara da cewa makamin ya fada kan inda aka nufa da shi a tashar tare da nasara.
A wani labarin kuma sojojin kasar ta Yemen sun bada labarin kakkabo jirin leken asiri da kuma yaki na kasar Amurka wanda ake kira MQ-9 a sararin samaniyar kasar Yemen , kuma shi ne 20 da suka sauke tun bayan fara yakin Tufanul Aksa a cikin watan Octoban shekara ta 2023.
Har’ila yau tun ranar Abasar da ta gabata ne sojojin kasar ta Yemen suna maida martani kan sojojin Amurka da suke tekun red sea da irin wadannan makamai.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: sojojin kasar
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamna Namadi Ya Gabatar da Kasafin Naira Biliyan 900 ga Majalisa
Daga Usman Muhammad Zaria
Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya gabatar da kasafin kuɗi na shekarar 2026 na sama da naira biliyan 900 ga Majalisar Dokokin jihar.
Yayin gabatar da kasafin da aka lakaba wa suna “Kasafin Kirkire-kirkire da Sauyi Don Cigaban Jigawa II,” Gwamna Namadi ya ce za a ware sama da naira biliyan 693.4, wanda ya kai kimanin kashi 76 cikin 100, don ayyukan raya kasa.
Gwamnan ya kuma ce sama da naira biliyan 208 za su tafi ne ga ayyukan yau da kullum.
A cewarsa, an ware sama da naira biliyan 310 ga bangaren ilimi da lafiya, yayin da kimanin naira biliyan 186 za su tafi ga hanyoyi da sufuri.
Malam Umar Namadi ya ƙara da bayyana cewa an ware sama da naira biliyan 74 ga bangaren noma da kiwo, sai naira biliyan 50.74 don wutar lantarki da makamashi, yayin da naira biliyan 12.68 za su tafi ga shirin ƙarfafa matasa.
Ya nuna cewa an tanadi naira biliyan 25.4 don ruwa da tsafta, sannan naira biliyan 35.4 don muhalli da sauyin yanayi.
Gwamna Namadi ya kuma gabatar da sama da naira biliyan 288 don ayyukan kananan hukumomi 27 na jihar.
Radio Nigeria ya ruwaito cewa kasafin shekarar 2026 ya fi na shekarar 2025 da kaso 19 cikin 100.