HausaTv:
2025-05-31@10:13:01 GMT

HKI Ta Kai Hare-hare A Falasdinu Da Kasar Lebanon

Published: 26th, March 2025 GMT

Sojojin mamayar HKI sun kai sabbin hare-hare a wasu yankuna na gabashin kasar Lebanon, adaidai lokacin da take ci gaba da kai wa yankin yammacin kogin Jordan wasu gare-haren.

Kafafen watsa labarun HKI sun ambaci cewa; Sojojin mamayar sun kame Falasdinawa 5 a garin al-Khalil dake kudancin yammacin kogin Jordan.

Haka nan kuma sun kama wasu Falasdinawa 8 a garin Nablus.

A garin Bireh da wasu yankuna na Ramallah, sojojin mamayar sun kai wasu hare-haren a yau Laraba.

A cikin watannin bayan nan, sojojin HKI sun rushe gidajen Falasdinwa 79 a cikin yankin yammacin kogin Jordan, tare da tilastawa mazaunan gidajen kusan 40,000 yin hijira.

A ranar 22 ga watan Maris ne dai jiragen yakin HKI su ka kai hare-hare a gargruwan Lebanon da su ka hada, Nabi Shit, Hermel, da wasu garuruwan da suke a yankin Bika. Haka nan kuma sun kai wasu hare-haren a garin Deir Qanun.

Tun daga fara yaki akan Gaza, sojojin HKI sun kashe Falasdinawan da sun haura 50,000, yayin da wani adadin da ya kai mutane113,000 su ka jikkata.

A can yankin Gaza ma, sojojin na HKI suna cigaba da kai hare-hare wanda ya yi sanadiyyar samun shahidai da dama.

Hare-haren na sojojin mamaya ya shafi garin Khan-yunus dake kudancin Gaza, haka nan kuma a garin Rafaha dake kan iyaka da kasar Masar.

Da safiyar yau Laraba kadai Falasdinawa 11 ne su ka yi shahada, daga cikinsu da akwai kananan yara 5.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

 Fiye Da Falasdinawa 60 Ne Su Ka Yi Shahada A Jiya Laraba

A ci gaba da tafka laifukan yakin da HKI take yi a Gaza,Fiye da Falasdinawa 60 ne su ka yi shahada a jiya Laraba.

A wani harin da sojojin mamayar su ka kai a yankin Jabaliya, Falasdinawa 5 sun yi shahada, yayin da wani adadi mai yawa su ka jikkata.

Wani jirgin sama maras matuki ya kai wani harin a unguwar “Shuja’iyya” wnada ya yi sanadin shahadar mutum daya, sai kuma wasu shahidan 4 a unguwar “Shari’u 5”, da kuma wasu shahidan 4 a garin “Bani-Suhaila”.

Wasu rahotannin sun ce, ‘yan sahayoniyar sun kai wasu hare-haren a garin ‘Abasan al-kabira’ da ya yi sanadin shahadar mutum daya da kuma jikkatar wasu masu yawa.

A yankin Qizan kuwa, ‘yan sahayoniyar sun kai hari akan mutanen da suke kokarin isa wurin da za su sami kayan agaji, tare da kashe 5 daga cikinsu a yankin kudu maso yammancin garin Khan-Yunus.

Ita kuwa hukumar yankin na Gaza ta sanar da cewa; ‘yan sahayoniyar sun kashe fararen hula 10 wadanda yunwa ci karfinsu, sannan kuma ta jikkata wasu 62 a wurin da aka ware na raba kayan agaji.

Sanarwar ta hukumar Gaza ta kuma ce; Yankunan da aka ware domin raba kayan agaji a karkashin Amurka da Isra’ila’ ya zama tarkon da ake kashe mutane a wurin.

A gefe daya ma’aikatar kiwon lafiya ta Gaza ta sanar da cewa; Sojojin mamaya sun kai wa asibitin tafi da gidanka na  “Red-Cross” hari dake “Mawasi, a gundunar Khan-Yunus. “Yan mamayar sun kai harin ne adaidai lokacin da ake yi wa wadanda su ka jikkata magani.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Cutar Kwalara Ta Yadu A Sudan Baya Ga Matsalar Tashe-Tashen Hankulan Da Suke Ci Gaba Da Yuduwa A Kasar
  •  DRC: Joseph Kabila Ya Bayyana A Yakin Dake Karkashin Kungiyar M23
  • Sojojin Mamayar Isra’ila Sun Aiwatar Da Kisan Kiyashi Kan Falasdinawa A Yankin Zirin Gaza
  • Falasdinawa 23 Suka Yi Shahada A Farmakin Da Sojojin Mamayar Isra’ila Suka Kai Kan Sansanin Al-Bureij
  • ‘Yan Tawayen Sudan Sun Kashe Fararen Hula 10 A Hare-Haren Da Suka Kai Kan Birnin Kordofan
  • Duniyarmu A Yau: Wasikar Lawyoyi 800 Ga Firay Ministan Kasar Burtaniya Kan Gaza
  •  Fiye Da Falasdinawa 60 Ne Su Ka Yi Shahada A Jiya Laraba
  •  Yemen: Wuce Gona Da Irin HKI Ba Zai Sauya Mana Ra’ayi Akan Ci Gaba Da Taimaka Wa Gaza Ba
  • Gaza : EU ba ta gamsu da sabon tsarin raba agaji na Amurka da Isra’ila ba  
  • An Fitar Da Sanarwar Hadin Gwiwa Ta Taron Kolin ASEAN-Sin-GCC