Wani rahoton tsaro da hukumar Kididdiga (NBS) ta fitar a watan Disamban 2024, ta ce, yawan kudin fansa da jama’an Nijeriya suka biya ya zarce naira tiriliyan 2.23 ga masu garkuwa da mutane daga Mayun 2023 zuwa Afrilun 2024.

A cewar rahoton na CESPS, kusan kashi 65 cikin 100 na magidanta da suka fuskanci matsalar sace-sacen jama’a sun biya matsakaitan kudin fansa na naira miliyan 2.

67, wanda ya kai naira tiriliyan 2.23.

An fitar da rahoton ne kwana guda bayan rahoton hukumar kare kakkin Dan’adam na Nijeriya na shekarar 2024, ya nuna cewa akalla mutane 526 ne aka kashe a wasu munanan hare-hare tare da yin garkuwa da wasu 949 a wasu sassan kasar.

Duk da masana sun sha nusar da jama’a illar biyan kudaden fansa ga ‘yan fashin daji, mutane ko iyalai suna ganin biyan kudin shi ne mafita a garesu a duk lokacin da aka sace musu wani nasu, lamarin da ke kara nuna sakacin jami’an tsaro, a cewar mutane da dama in ba su biya kudin fansar ba suna iya rasa dan uwan nasu da aka sace.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Birgediya Janar Sabahi Fard Ya Jaddada Cewa: Duk Wani Sabon Hari Kan Iran Zai Fuskanci Martani Mai Gauni

Kwamandan rundunar hadin gwiwar hedikwatar tsaron saman Iran ya jaddada cewa: Duk wani sabon kuskure da ‘yan sahayoniyya suka aikata zai haifar da mummunan sakamako

Kwamandan rundunar hadin gwiwar hedikwatar tsaron saman Iran kuma  kwamandan bataliyar Khatam al-Anbiya (s.a.w) Birgediya Janar Alireza Sabahi Fard, ya jaddada cewa: Duk wani sabon kuskure da yahudawan sahayoniyya za su sake yi, zai haifar da mummunan sakamako.

Birgediya Janar Seyyed Majid Mousavi, kwamandan rundunar sararin samaniyar Iran na dakarun kare juyin juya halin Musulunci ta Iran ya ziyarci hedikwatar hadakar tsaron sojojin saman na Khatam al-Anbiya, inda ya tattauna da Birgediya Janar Sabahi Fard, kan sakamakon arangamar da sojoji suka yi a baya-bayan nan da kuma hanyoyin inganta hadin kan tsaro.

A zaman taron, Sabahi Fard ya ce, “Tsarin tsaron saman kasar Iran ya shiga cikin yakin kwanaki 12 na baya-bayan nan da jajircewa da himma, tare da yin nasara ta hanyar hadin gwiwa da daukar matakin jihadi wajen dakile manufofin makiya yahudawan sahayoniyya tare da tilasta musu ja da baya. Ya bayyana karara cewa ci gaba da ta’addancin yana kara ta’azzara halin da ake ciki a cikin yankunan da aka mamaye, musamman a Tel Aviv da Haifa.”

Ya kara da cewa, “Suna dogara da karfin kasa wajen bunkasa na’urar tsaronsu, kuma jinin shahidansu ko daga sojoji ne ko farar hula, ba zai zuba a banza ba. Zai haifar da mummunan tasiri kan ‘yan mamayar yahudawan sahayoniyya. Kisan gillar da aka yi wa masana kimiyyar nukiliya da shugabannin tsaron Iran ba zai hana kasar cimma nasarorin fasaha, soja, da tsaro ba. Maimakon haka, za su yi aiki a matsayin wani gagarumin shiri na yaki da makiya.”

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Al’ummar Fegin Mahe Sun Yi Zanga-zanga Kan Kisan Jama’a Da ‘Yan Bindiga Ke Yi
  • Cutar Amai Da Gudawa Ta Hallaka Mutane 13 A Neja
  • Dalilin da muka gaza biyan ma’aikata mafi ƙarancin albashi — Gwamnatin Borno
  • Jamhuriyar Musulunci Ta Iran Ta Jaddada Hakkinta Na Tace Sinadarin Uranium A Cikin Kasarta
  • ‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Ƙauyen Katsina, Sun Jikkata Mutane 2, Sun Sace Wasu
  • Kotu Ta Umarci Gwamnatin Bauchi Ta Biya Tsohon Akanta-Janar Naira Miliyan 100
  • Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP
  • Gwamnatin Zamfara Ta Kira Babban Taron Tsaro Tare Da Bayyana Sabbin Dabaru Na Yakar ‘Yan Bindiga.
  • Libya Ta Tasa Keyar Baƙin Haure Yan Kasar Sudan 700 Zuwa Kasarsu
  • Birgediya Janar Sabahi Fard Ya Jaddada Cewa: Duk Wani Sabon Hari Kan Iran Zai Fuskanci Martani Mai Gauni