Shugaban Majalisar Shawarar Musulunci Ta Iran Ya Ce: Akwai Babbar Damar Bunkasa Alakar Tattalin Arziki Da Kasashen Latin Amurka
Published: 6th, June 2025 GMT
Shugaban Majalisar Shawarar Musulunci ta Iran ya jaddada cewa; Akwai babbar damar bunkasa dangantakar tattalin arziki da kasashen Latin Amurka
Shugaban Majalisar Shawarar Musulunci ta Iran Muhammad Baqir Qalibaf wanda ya yi tafiye-tafiye tun a ranar Asabar din da ta gabata a ziyarar da ya kai kasashen Latin Amurka da Brazil don halartar taron BRICS karo na 11, ya dawo inda ya iso filin jirgin saman Mehrabad na Tehran da yammacin yau Juma’a, bayan kammala ziyarar tasa, inda ya samu tarba daga jami’an gwamnati da na sojin kasar Iran.
Ziyarar na dauke da nufin fadada huldar tattalin arziki da karfafa hadin gwiwa ta hanyar diflomasiyyar majalisar dokoki, kuma ta hada da ganawa da manyan jami’ai a Venezuela, Cuba, da Brazil.
Shugaban majalisar shawarar ta Musulunci ya yi ishara da hadin gwiwa tsakanin gwamnatocin kasashen Latin Amurka da kasashen musulmi, yana mai cewa: “Akwai babbar dama ga raya huldar tattalin arziki, musamman a fannin makamashi da kuma sha’awar fannonin ilmi.”
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Nukiliya : Iran za ta bayar da amsa ga shawarar Amurka cikin kwanaki masu zuwa
Ministan harkokin wajen kasar Abbas Araghchi ya sanar da cewa, nan da kwanaki masu zuwa Iran za ta mayar da amsa kan shawarar da Amurka ta gabatar kan shirin nukiliyar kasar na zaman lafiya.
A cewarsa, shawara da Amurka ta gabatar tana bukatar zurfafa bincike.
M. Araghchi, ya bayyana hakan ne ziyarar da yake a birnin Beirut, na kasar Lebanon inda ya jaddada cewa, amsar da Iran za ta mayar zata kasance bisa tsarin Jamhuriyar Musulunci ta Iran da manufofinmu da kuma kare muradun al’ummar Iran.
Ya nanata cewa inganta makamashin Uranium tamkar “jan layi” ne ga Iran, yana mai cewa Tehran ba ta bukatar neman izini daga kowa don ci gaba da ayyukanta da suka dace da shari’a kuma halaliyarta.
Ya ce inganta sinadarin Uranium ya zama abin alfahari ga al’ummar Iran kuma wannan nasara ta ilimi ta samo asali ne daga kokari da basirar masana kimiyyar Iran, kuma ba abu ne mai sauki da za a yi watsi da ita.
Araghchi ya kuma tunatar da cewa, Iran ta ta sha wahala sosai fiye sakamakon shekaru 20 na takunkumin tattalin arziki mai tsanani da Amurka ta kakaba, da kuma kisan wasu masana kimiyyar nukiliyarta tun farkon shekarun 2010, wanda jami’an gwamnatin Isra’ila suka shirya.
Ministan harkokin wajen na Iran ya kara da cewa sama da Iraniyawa miliyan daya ne ke bukatar magunguna da cibiyar bincike ta Tehran ta samar, don haka ci gaba da sarrafa sinadarin Uranium a Iran ya zama wajibi.