Shugaban Majalisar Shawarar Musulunci ta Iran ya jaddada cewa; Akwai babbar damar bunkasa dangantakar tattalin arziki da kasashen Latin Amurka

Shugaban Majalisar Shawarar Musulunci ta Iran Muhammad Baqir Qalibaf wanda ya yi tafiye-tafiye tun a ranar Asabar din da ta gabata a ziyarar da ya kai kasashen Latin Amurka da Brazil don halartar taron BRICS karo na 11, ya dawo inda ya iso filin jirgin saman Mehrabad na Tehran da yammacin yau Juma’a, bayan kammala ziyarar tasa, inda ya samu tarba daga jami’an gwamnati da na sojin kasar Iran.

Ziyarar na dauke da nufin fadada huldar tattalin arziki da karfafa hadin gwiwa ta hanyar diflomasiyyar majalisar dokoki, kuma ta hada da ganawa da manyan jami’ai a Venezuela, Cuba, da Brazil.

Shugaban majalisar shawarar ta Musulunci ya yi ishara da hadin gwiwa tsakanin gwamnatocin kasashen Latin Amurka da kasashen musulmi, yana mai cewa: “Akwai babbar dama ga raya huldar tattalin arziki, musamman a fannin makamashi da kuma sha’awar fannonin ilmi.”

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Nukiliya : Iran za ta bayar da amsa ga shawarar Amurka cikin kwanaki masu zuwa

Ministan harkokin wajen kasar Abbas Araghchi ya sanar da cewa, nan da kwanaki masu zuwa Iran za ta mayar da amsa kan shawarar da Amurka ta gabatar kan shirin nukiliyar kasar na zaman lafiya.

A cewarsa, shawara da Amurka ta gabatar tana bukatar zurfafa bincike.

M. Araghchi, ya bayyana hakan ne ziyarar da yake a birnin Beirut, na kasar Lebanon inda ya jaddada cewa, amsar da Iran za ta mayar zata kasance bisa tsarin Jamhuriyar Musulunci ta Iran da manufofinmu da kuma kare muradun al’ummar Iran.

Ya nanata cewa inganta makamashin Uranium tamkar “jan layi” ne ga Iran, yana mai cewa Tehran ba ta bukatar neman izini daga kowa don ci gaba da ayyukanta da suka dace da shari’a kuma halaliyarta.

Ya ce inganta sinadarin Uranium ya zama abin alfahari ga al’ummar Iran kuma wannan nasara ta ilimi ta samo asali ne daga kokari da basirar masana kimiyyar Iran, kuma ba abu ne mai sauki da za a yi watsi da ita.

Araghchi ya kuma tunatar da cewa, Iran ta ta sha wahala sosai fiye sakamakon shekaru 20 na takunkumin tattalin arziki mai tsanani da Amurka ta kakaba, da kuma kisan wasu masana kimiyyar nukiliyarta tun farkon shekarun 2010, wanda jami’an gwamnatin Isra’ila suka shirya.

Ministan harkokin wajen na Iran ya kara da cewa sama da Iraniyawa miliyan daya ne ke bukatar magunguna da cibiyar bincike ta Tehran ta samar, don haka ci gaba da sarrafa sinadarin Uranium a Iran ya zama wajibi.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Gargadi Kasashen Turai Kan Fuskantar Martani Daga Kasar Iran
  • Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4
  • Namibia Za Ta Karfafa Hulda Da Sin Yayin Baje Kolin Cinikayya Da Tattalin Arziki
  • Shugaban Kasar Iran Ya Tattauna Ta Wayar Tarko Da Tokwaransa Na Masar Da Saudiya
  • Ali Shamkhani: Iran Ba Zata Taba Saryar Da Hakkinta Na Makamashin Nukliya Ba
  • Qolibuf: Kungiyar BRICS Dama Ci Ta Kauda Danniyar Amurka A Kan Kudaden Kasashen Duniya
  • Babban Zauren MDD Ta Zabi Kasashen Congo Da Liberian Na Zama Mambobi A Kwamitin Tsaro
  • Shugaban Kasar Iran Ya Jaddada Cewa: Amurka Da Isra’ila Suna Da Mugun Nufi Kan Iran Da Kasashen Musulmi
  • Nukiliya : Iran za ta bayar da amsa ga shawarar Amurka cikin kwanaki masu zuwa