HausaTv:
2025-06-07@05:15:07 GMT

Kasar Faransa Ta Jaddada Aniyarta Ta Amincewa Da Yantacciyar Kasar Falasdinu

Published: 6th, June 2025 GMT

Ministan harkokin wajen Faransa ya jaddada aniyar birnin Paris na amincewa da kasar Falasdinu

Ministan harkokin wajen Faransa Jean-Noel Barrot ya tabbatar da aniyar Faransa na amincewa da kasar Falasdinu, yana mai jaddada cewa wannan amincewa ba zai kasance na bai daya ba, sai dai a matsayin wani bangare na kokarin hadin gwiwa da sauran kasashe.

Hakan ya zo ne a wata hira da aka yi da shi a gidan rediyo kasa makonni biyu gabanin taron hadin gwiwa tsakanin Faransa da Saudiyya a Majalisar Dinkin Duniya.

Barrot ya bayyana cewa, makasudin taron shi ne hada kasashe da masu ruwa da tsaki da dama da suka hada da hukumar Falasdinawa da kasashen Larabawa don ciyar da shirin zaman lafiya gaba. Ya bayyana cewa, Faransa a matsayinta na mamba ta dindindin a kwamitin sulhu na Majalisar Dinkin Duniya, tana da wani nauyi na musamman a wannan fanni, kuma amincewar da ake sa ran na da nufin kara tabbatar da martabar kasar Falasdinu da samar mata da damammaki.

Barrot ya kuma jaddada muhimmancin tattaunawa kan batun kwance damarar kungiyar Hamas a matsayin wani bangare na duk wani hangen nesa na makomar zirin Gaza bayan yakin. Ya bayyana damuwarsa game da tsarin raba kayan agaji a yankin, wanda ya bayyana a matsayin “tsarin soja”, lura da hargitsi da tashe-tashen hankula da ya haifar, musamman bayan killace yankin da gwamnatin haramtacciyar kasar Isra’ila ta yi tun tsawon watan Maris din da ya gabata.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: kasar Falasdinu

এছাড়াও পড়ুন:

Ribadu Ya Kara Jaddada Gargadinsa Kan Biyan Kudin Fansa Ga Masu Garkuwa Da Mutane

Wani rahoton tsaro da hukumar Kididdiga (NBS) ta fitar a watan Disamban 2024, ta ce, yawan kudin fansa da jama’an Nijeriya suka biya ya zarce naira tiriliyan 2.23 ga masu garkuwa da mutane daga Mayun 2023 zuwa Afrilun 2024.

A cewar rahoton na CESPS, kusan kashi 65 cikin 100 na magidanta da suka fuskanci matsalar sace-sacen jama’a sun biya matsakaitan kudin fansa na naira miliyan 2.67, wanda ya kai naira tiriliyan 2.23.

An fitar da rahoton ne kwana guda bayan rahoton hukumar kare kakkin Dan’adam na Nijeriya na shekarar 2024, ya nuna cewa akalla mutane 526 ne aka kashe a wasu munanan hare-hare tare da yin garkuwa da wasu 949 a wasu sassan kasar.

Duk da masana sun sha nusar da jama’a illar biyan kudaden fansa ga ‘yan fashin daji, mutane ko iyalai suna ganin biyan kudin shi ne mafita a garesu a duk lokacin da aka sace musu wani nasu, lamarin da ke kara nuna sakacin jami’an tsaro, a cewar mutane da dama in ba su biya kudin fansar ba suna iya rasa dan uwan nasu da aka sace.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Limamin sallar Idi Al-Adha A Tehran Ya Jaddada Cewa: Imam Khomeini {r.a} Ya Kawo Sauyi Da Ci Gaba A Iran
  • Ribadu Ya Kara Jaddada Gargadinsa Kan Biyan Kudin Fansa Ga Masu Garkuwa Da Mutane
  • Wani Injin Jirgi Mai Saukar Ungulu Kirar Kasar Sin Ya Samu Shaidar Amincewa 
  • Shugaban Kasar Iran Ya Tattauna Ta Wayar Tarko Da Tokwaransa Na Masar Da Saudiya
  • Qolibuf: Kungiyar BRICS Dama Ci Ta Kauda Danniyar Amurka A Kan Kudaden Kasashen Duniya
  • Jagoran Juyin Juya Halin Musulunci Ya Jaddada Hakkin Iran Na Tace Sinadarin Uranium
  • Iran Ta Jaddada Hakkinta Na Mayar Da Martani Kan Bakar Siyasar Kwamitin Gwamnonin Hukumar IAEA
  • Shugaban Kasar Iran Ya Jaddada Cewa: Amurka Da Isra’ila Suna Da Mugun Nufi Kan Iran Da Kasashen Musulmi
  • Iran ta bukaci hadin kan al’ummar Lebanon wajen warware matsalolin kasar