Leadership News Hausa:
2025-06-07@02:15:58 GMT

Wajibi A Mayar Da Hankali Kan ‘Yancin Yara

Published: 6th, June 2025 GMT

Wajibi A Mayar Da Hankali Kan ‘Yancin Yara

Yawan Yaran da ba su zuwa makarantun boko a Nijeria wadanda suka kai kimanin su miliyan 18.3, hakan ya nuna cewa, wannan adadin na Yaran, kusan daidai yake da yawan alumomin da ke a kasashen Norway, Singapore, da Cuba.

Wannan ba wai batu ne, na matsalar da ake fuskanta a bangaren ilimin boko kadai ba, domin matsala ce, da ke bukatar a ayyana dokar ta baci tare da samar da daukin da ya kamata daga bangaren gwamnati da kuma sauran alomomin kasar.

Misali, wata kungiya mai kare rajin Yara, mai zaman kanta da ake kira da, Sabe the Children ta bayyana cewa, sama da Yara1,600 a shekarar 2014, aka sace a makarantun su, wadanda sace su din, ya zama tamkar, an dana masu wani tarkon mutuwa ne.

Kazalika, wani rahoto Daraktan Asusun tallafawa kannan Yara na UNICEF, da ke gudanar da aikinsa a kasar nan Dakta Tushar Raney a bayyana cewa, a shekarar 2023 kacal, a daukacin fadain Nijeriya, an tilasta garkame makarantu da suka kai adadin 439.

A wani lokacin rashin zabi ne, ke tilastawa wasu iyayen jefa rayuwar ‘ya’yansu, a cikin hatsari domin ‘ya’yan na su, samu ilimin zamani, wanda idan ba su samu ilimin ba, rayuwarsu, za ta kasance a cikin kangin jahilci, duba da cewa, kowanne dan kasa, na da hakkin a bai wa rayuwarsa kariya.

Bugu da kari, kalubalen rashin samun abinci mai gina jiki a tsakanin yaran kasar, na daga cikin abinda ya kara zama wata babbar annoba.

Ganin cewa, a kasar akwai yara kanana miliyan 5.4 da shekarun su suka fara daga watanni 0 zuwa watanni 59 da ke ci gaba da fuskantar kalubalen karancin abinci wadanda adadinsu ya karu zuwa kaso 23 cikin dari, hakan ya sanya, a nan gaba, Nijeriya za ta iya yin rashin samun karin alumma.

Rashin samun abinci mai gina jiki a tsakanin kananan yara hakan ya dashishe su, daga saurin fahintar ilimi tare da jefa rayuwarsu, a cikin kangin talauci da kuma rashin samun ci gaba.

Hakazalika, wasu alkaluman da UNICEF ta fitar sun bayyna cewa, a fadin duniya, an dora Nijeriya kan sikelin kasar da ta kai mataki na uku, wajen yiwa ‘ya’ya mata masu kananna shekaru aure, inda kasar ta kasance, tana da ‘ya’ya mata da suka kai miliyan 23.6 da aka yi masu are, suan da shekaru 18 da kuma wasun su, da suka kai sama da miliyan 10, da aka yi masu aure, su na da shekaru 15.

Irin wannan auren na wuri, ya janyo tauye hakkin irin wadannan ‘ya’yan mata, damar samun ilimin boko, wanda hakan ya kasance, tamkar take masu ‘yancin su ne, na rayuwa.

Hukumar kididdiga ta kasa NBS a cikin wani rahoto da ta fitar ta ce, akwai kuma batun sanya kananna yara aikin bauta, inda a Nijeriya, a 2022 ake kiyasta cewa, akwai yara sama da miliyan 24 da suke yin irin wannan aikin na kangin bauta, ciki har da wasu yara miliyan 14.3 da ake sanya wa, yin ayyuka masu hatsari.

Yaran suna yin aikin ne, a gurare da ban da ban da suka hada da, inda ake hakar ma’adanai da kuma a wasu masana’antu, inda ake biyansu, kudade, ‘yan kalilan.

Sai dai, a kwanukan baya, gwamnatin tarayya ta samar da wani shiri na samar da ilimin boko, inda ta zuba sama da Naira biliyan 263 a asusaun samar da ilimi na bai daya wato UBEC, amma wasu tsaiko da ake samu a shirin, hakan na ci gaba da janyo jinkirin yin aikin gadan-gadan.

Hakazalika, shugaban kasa Bola Tinubu, ya aminci da a yi amfani da asusun na UBEC, musamman domin a bunkasa ilimi a kasar a sama da jihohi 30, amma sai dai, shirin baya tafiya, yadda ya kamata.

Bugu da kari, daukin da ma’aikatar kula da walwalar mata da walwalar a karkashin ministar ma’aikatar Imaan Sulaiman-Ibrahim, ta samar da wani kyakyawan tsari na bai wa kananan yara kariya.

Misali, an karawa ma’aikatar karin kasafin kudi da ya dara sama da kaso 1000 a cikin dari, musamman domin a tabbatar da ana bai wa yaran kasar kariyar da ta kamata.

Sai dai, samar da daukin abu ne, dake bukatar a hada karfi da karfe, a tsakanin matakan gwamnati uku na kasar nan da kuma daukin sauran alumomin kasar.

Abin da Nijeriya ke bukata shi ne, kula da walwala da jin dadin yara tare da kuma samar masu da tsaron rayuwar su.

Kazalika, ya zama wajibi gwamnatin tarayya kafa cibiyoyin ilimi domin a samar da kariyar ta tsaro a shiyoyin kasa, musamman ta hanyar tura jami’an tsaro, domin su bai wa makarantu kariya.

Dole ne kuma gwamnatocin jihohi su tabbatar da sun samar da kudaden a cikin shirin ilimin, wanda hakan zai dakile duk wani jinkiri da ake samu, na wanzar da shirin.

Bugu da kari, ya sama wajibi gwamnati ta samar da kyawawan shirye-shiye na tallafawa iyaye wajen tsamo su, daga halin talaucin da ke addabar su

Ya kamata malaman addinai, su mayar da hankali wajen yin gangamin kan abubuwa da ke sanya wa, ake take wa kananan yara ‘yanci.

Hazalika, akwai bukatar a kara mayar da hankali, wajen kara horas da jami’an tsaro tare da samar masu da wadatattun kudade domin su rinka hukunta duk wanda ya take ‘yancin yara.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: rashin samun

এছাড়াও পড়ুন:

Shugaban Kasar Iran Ya Jaddada Cewa: Amurka Da Isra’ila Suna Da Mugun Nufi Kan Iran Da Kasashen Musulmi

Shugaban kasar Iran ya jaddada cewa: Amurka da haramtacciyar kasar Isra’ila suna da mugun nufi kan Iran da kasashen musulmi

Shugaban kasar Iran Masoud Pezeshkian ya jaddada cewa: Amurka da haramtacciyar kasar Isra’ila na da mugun nufi kan Iran da kasashen musulmi.

A yayin wani jawabi da ta gabatar a wajen juyayin tunawa da rasuwar Imam Khumaini {r.a}, Pezeshkian ya ce: Haramtacciyar kasar Isra’ila ba za ta iya aikata wani aiki hauka da wauta ba, idan kasashen musulmi suka hada kansu.

Pezeshkian ya kara da cewa: Wadanda ke da’awar kare hakkin bil’adama suna kare “haramtacciyar kasar Isra’ila” mai laifi, kuma suna ci gaba da adawa da shirin makamashin nukiliyar Iran na zaman lafiya.

Ya ci gaba da cewa: “Babu mutum mai ‘yanci da zai yarda da zalunci da girman kai, kuma Iran ba zata yarda da shi ba.”

Pezeshkian ya bayyana cewa: “Za su dakile duk wani makirce-makircen abokan gaba kuma ba za su taba yin watsi da ‘yancinsu na nukiliya da na kimiyya ba.”

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Afirka Tana Shirin Samar Da Maganin Kwalara Da Kanta
  • Gwamnatin Tarayya Za Ta Tallafa Wa Yekuwar Rigakafin Cutar Ƙyandar Jamus
  • A shekara 25, na kashe tiriliyan 161 wajen inganta lafiya a Afirka – Bill Gates
  • Sallah: ’Yan sanda sun yi alƙawarin tabbatar da tsaro a Gombe
  • Ambaliyar Mokwa: An gano gawar yara 7, jama’a na neman agaji
  • Sallah: Mun shirya samar da tsaro a Yobe — ’Yan Sanda
  • Ba zan yi musayar yawu da yara ba — Martanin Amaechi ga Wike
  • Shugaban Kasar Iran Ya Jaddada Cewa: Amurka Da Isra’ila Suna Da Mugun Nufi Kan Iran Da Kasashen Musulmi
  • Nukiliya : Iran za ta bayar da amsa ga shawarar Amurka cikin kwanaki masu zuwa