Tsadar Rayuwa: Yadda Al’umma Suka Yi Sallah Cikin Kunci
Published: 6th, June 2025 GMT
An gudanar da sallah ne bayan da Mai Alfarma Sarkin Musulmi, Muhammad Sa’ad Abubakar III ya bayyana ranar Juma’a 06 ga Yuni a matsayin ranar 10 ga watan Zul-Hijja 1446 a matsayin ranar sallar layya kamar yadda ya bayyana a sanarwar da shugaban kwamitin lamurran addinin musulunci kana Wazirin Sakkwato, Farfesa Sambo Wali Junaid ya sanyawa hannu.
A ra’ayin jama’a da dama ba su da halin sayen dabbobin layya da za su yanka, wasu kuwa sun bayyana cewar ko da suna da halin yin layya to ba ita ce a gaban su ba domin a cewarsu za su shiga cikin gagarumar matsala a gidajen su domin mafi yawa ba su tanadi abincin da iyalansu za su ci ba don haka sayen abinci ne mafi muhimmanci.
Talakawa da daman gaske da kanana da matsakaitan ma’aikata da kananan ‘yan kasuwa sun shaidi sallar layya a wannan shekarar a halin da suke fatar kada Allah ya maimaita domin a ta bakin su ba a taba shaidar sallah a matsin tattalin arziki irin ta wannan shekarar ba.
Tashin gwauron- zabi da dabbobin layya suka yi, hauhawar farashin abinci, tsadar man fetur da halin kuncin da jama’a ke ciki duka abubuwa ne muhimmai da suka taru suka dabaibaye sallar ta hanyar hana mata karsashi.
Gagarumar matsalar tsaro ba dare ba rana daga Borno zuwa Sakkwato, tashin bama- bamai, garkuwa da mutane da kisan gillar da ‘yan ta’adda ke yi wa al’umma ba kakkautawa sun yi matukar tasiri wajen hanawa sallah karsashi.
Rahotanni sun tabbatar da cewar tsananin tsadar da dabbobin layya suka yi ya tilastawa jama’a da dama hakura da yin layya domin abincin da za su ci yana kokarin gagarar su wanda ya zama dalilin da ire-iren wadanda suka samu kudin layya to abinci suke siya wanda shine ya fi muhimmanci.
Auwal Balarabe wani matsakaicin ma’aikaci a Abuja ya bayyana cewar wannan layya ce ta farko a tarihin rayuwarsa da aka yi ba ya da halin yanka dabba wanda a cewarsa ya shiga cikin tarihin da ba zai manta ba a dalilin matsin rayuwa.
Wasu maigidanta a Kano sun bayyana cewar ba za su wahalar da kan su sayen ragon dubu 200 zuwa 250 ba, shanu kuwa sai dubu 500 zuwa miliyan daya don haka suka hakura suka zabi sayen kaji da nama.
Mabambantan al’umma sun bayyana halin rashin da aka fuskanta a wannan shekarar da hauhawar farashin raguna da sauran dabbobin layya ya tilastawa mutane da dama hada kudade domin yin hadakar layya ta hanyar sayen babbarn sa ko saniya wadanda suka kai adadin shekaru biyu na layya.
Wani magudanci Isna’il Abubakar a Sakkwato ya bayyana cewar ragon da ya saya a 2024 a dubu 150 a yanzu sai 260, don haka da shi da makwabta hudu sun hada dubu 800 domin sayen saniya su raba.
Bincike a mabambantan kasuwannin karar dabbobi ya nuna an samu karancin masu sayen raguna, shanu da sauran nau’ukan dabbobi sama da shekarun baya kamar yadda masu sayar da raguna a Abuja, Kano, Bauchi, Kaduna, Neja, Gusau, Sakkwato da Birnin- Kebbi suka bayyanawa manema labarai.
“Ba mu taba ganin sallar da jama’a suka kasa yin tururuwar zuwa sayen dabbobi ba irin wannan shekarar, ko kadan babu ko irin rabin hada-hadar da muka saba samu a shekarun baya.”
A cewar Hassan Mahe ko kadan kasuwar dabbobi a bana ta bambanta da saura domin babu kasuwa, kuma duk da tsadar abincin dabbobi, farashin ya karu ne a dalilin hana shigowa da su daga Nijar da gwamnatin kasar ta yi wanda a kan hakan farashin dabbobin ya ninka.
Baya ga wannan matsalar tsaro wadda ta ki ci ta ki cinyewa gagarumar matsala ce wadda ta hanawa bukin sallah armashi a yankuna da dama da ke fama da matsalar tsaro a kasar nan a dalilin hare- haren ta’addanci.
Haka ma dinbin al’ummar da ke tsugune a sansanin ‘yan gudun hijira ko kadan babu maganar kayatarwar shagalin sallah ko yin layya a wajen su, hasalima ranar sallah kan tuna masu da lokutan baya da suka yi sallah cikin walwala da farin ci a muhallansu kuma a cikin iyalan su.
Kayan abinci kamar shinkafa, masara, gero, dawa, wake, fulawa, man gyada, man-ja da nau’ukan tumatur, albasa, attarugu, tattasai da sauransu sun yi matukar tsada lamarin da tsadar a kullum sai gaba-gaba take yi wanda hakan ya taimaka wajen kara rage armashin sallah domin jama’a da dama ba su da wadatar sayen kayan bukatu.
Maigidanta da dama a tattanawarsu da LEADERSHIP Hausa sun bayyana fatar samun saukin al’amurra ta yadda dabbobi da kayan abinci da na bukatu za su sauko kasa akasin shekaru biyu da suka gabata zuwa yanzu da al’amurra suka tabarbare har jama’a suka shiga cikin kunci maras misaltuwa.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: wannan shekarar dabbobin layya bayyana cewar sun bayyana
এছাড়াও পড়ুন:
An kama tsohon minista kan zargin kisan kai domin tsafi a Nijar
Antoni Janar na Kotun Ɗaukaka Ƙara da ke birnin Yamai a Nijar, ya bayyana cewa an kama tsohon Ministan Harkokin Waje, Ibrahim Yacoubou, bisa zargin hannunsa a cikin wata aika-aika ta kisan kai domin yin tsafi.
A cewar Maazou Oumarou, lamarin ya samo asali ne daga wani binciken ’yan sanda da aka fara gudanarwa tun a ranar 29 ga Yuli, 2025.
KEDCO ya ƙaryata asibitin AKTH kan mutuwar majinyata saboda ɗauke wuta Dole sai mun tantance wa’azi kafin a yi —Gwamnan NejaYa bayyana cewa, an soma gudanar da binciken ne dangane da yunƙurin kisa a wani yanki da ke wajen birnin Yamai, lamarin da ya kai ga cafke ababen zargin a garin Dosso.
Wani mutum mai suna Mahamadou Noura ne ya bayyana cewa shi ne ya yi yunƙurin kisan, tare da wasu kashe-kashe guda shida da ya aiwatar a baya, bisa umarnin wasu mutane, ciki har da tsohon ministan Ibrahim Yacoubou.
Mutumin ya shaida wa mahukunta cewa ya aikata hakan ne domin yin tsafi da gawarwakin, a madadin wasu mutane da suka haɗa da: Issa Ali Maiga da Ismael Morou Karama da Elhadji Bilya da kuma Issa Seybou Hama.
TRT ya ruwaito cewa tuni dai an cafke duk ababen zargin, yayin da Kotun Ɗaukaka Ƙarar ta umurci ’yan sanda da su ci gaba da bincike tare da ɗaukar ƙarin matakan da za su tabbatar da gaskiya.
Sanarwar ta ce: “Manufar wannan mataki na shari’a ita ce a tattara cikakken rahoto da ke ƙunshe da dukkan abubuwan da suka faru, sannan a miƙa shi ga ɓangaren gurfanarwa.”
Mai shigar da ƙara a ɓangaren gwamnati ya ce, la’akari da girman wannan lamari, wajibi ne a gudanar da bincike cikin gaggawa.
Haka kuma ya buƙaci al’umma da su mutunta ’yancin kotu tare da bayar da cikakken goyon baya domin fayyace gaskiya.
Ana iya tuna cewa, Ibrahim Yacoubou na daga cikin manyan jami’an da aka kama bayan juyin mulkin Nijar na ranar 26 ga Yuli, 2023, sai dai daga bisani an ba shi beli na wucin gadi a cikin watannin baya.