Kotun kasa da kasa ta ICC ta yi tir da gwamnatin kasar Amurka wacce ta kakabawa al-kalan kotun guda hudu saboda hannu da suke da shi wajen fidda sammacin kama fray ministan HKI Benyamin Natanyahu.

Kotun ta kara da cewa tana goyon bayan alkalanta kuma zata ci gaba da aikinta na tabbatar da adalci a duniya duk tare da abinda suke faskanta.

Kotun ta bayyana cewa tana aikinta ne bisa goyon bayan kasashen duniya 125 wadanda suka fito daga dukkan kusruwowin duniya.

Takunkuman dai ya shafi wadannan alkalai su 4 kuma mata. Kuma sun hana ko wanne daga cikinsu, shiga kasar Amurka kuma idan suna da kadarori ko kudade gwamnatin Amurka ta kwace su.

A cikin watan Nuwamban shekara ta 2024 ne dai kotun ta ICC wacce take zama a birnin Haque ta fidda sammacin kama Firay ministan HKI Benyamin Natanyahu da kuma tsohon ministan yakin kasar Yoav Galant saboda zargin aikata laifukan yaki a Gaza.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Gargadi Kasashen Turai Kan Fuskantar Martani Daga Kasar Iran

Ministan harkokin wajen Iran yayi kashedi ga kasashen Turai cewa: Iran za ta mayar da martani ga duk wani matakin kare hakkinta

Ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Araqchi ya gargadi kasashen Turai kan daukar duk wani mummunan mataki kan Iran a hukumar kula da makamashin nukiliya ta duniya IAEA, yana mai jaddada cewa; Iran za ta mayar da martani mai karfi kan duk wani keta hakkinta.

Abbas Araqchi ya rubuta a ranar Juma’a a cikin wani sakon da ya wallafa a dandalin X cewa: “Maimakon yin aiki da kyakkyawar niyya, Tawagar Turai ta zaɓi ɗaukar munanan matakai kan Iran a kwamitin alkalan hukumar IAEA.” Ya kara da cewa: “Lokacin da wadannan kasashe uku suka rungumi dabi’ar kuskure iri daya a shekara ta 2005, sakamako ne na sabbin al’amura suka fito a fuskoki da dama, ciki har da kai Iran ga gagarumin matsayin inganta sinadarin Uranium a cikin kasarta. Shin har yanzu tawagar kasashen Turai ba su koyi wani darasi ba cikin shekaru ashirin da suka gabata a mu’amalarsu da Iran?” Ya ci gaba da cewa: Zarge-zargen da ake yi kan Iran da tuhumarta da karya yarjejeniyar tsaro – bisa ga rahotanni masu rarrafe da siyasa – a fili yana nufin haifar da neman rikici ne. Turai na gab da sake fuskantar wani babban kuskuren dabarun.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Gargadi Kasashen Turai Kan Fuskantar Martani Daga Kasar Iran
  • Kwamishina ya yi murabus saboda sauya sheƙar Gwamnan Akwa Ibom
  • Tsohon Alkalin Alkalan Najeriya, Lawal Uwais ya rasu
  • Beirut: HKI Ta Kai Hare-hare A Unguwar Dhahiya Dake Birnin Beirut
  • Lambar “-1.5” Gargadi Ce Da Al’ummar Duniya Ke Yi Ga Azzaluma 
  • Ali Shamkhani: Iran Ba Zata Taba Saryar Da Hakkinta Na Makamashin Nukliya Ba
  • Farfesa Jibril Amin Tsoho Ministan Ilim Da, Manfetur A Najeriya Rasu Yana Dan Shekara 85 A Duniya
  • Maniyyata na hawan Arfa a kasar Saudiyya
  • Trump ya haramtawa ‘yan kasashen duniya 12 shiga Amurka