Kotun ICC Ta Yi Tir Da Amurka Saboda Takunkuman Da Ta Dorawa Alkalan Kotun Don Hanata Aikinta Da Yenci
Published: 6th, June 2025 GMT
Kotun kasa da kasa ta ICC ta yi tir da gwamnatin kasar Amurka wacce ta kakabawa al-kalan kotun guda hudu saboda hannu da suke da shi wajen fidda sammacin kama fray ministan HKI Benyamin Natanyahu.
Kotun ta kara da cewa tana goyon bayan alkalanta kuma zata ci gaba da aikinta na tabbatar da adalci a duniya duk tare da abinda suke faskanta.
Takunkuman dai ya shafi wadannan alkalai su 4 kuma mata. Kuma sun hana ko wanne daga cikinsu, shiga kasar Amurka kuma idan suna da kadarori ko kudade gwamnatin Amurka ta kwace su.
A cikin watan Nuwamban shekara ta 2024 ne dai kotun ta ICC wacce take zama a birnin Haque ta fidda sammacin kama Firay ministan HKI Benyamin Natanyahu da kuma tsohon ministan yakin kasar Yoav Galant saboda zargin aikata laifukan yaki a Gaza.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Sheikh Qasem: Nuna Halin Ko In-Kula Na Duniya Ne Ya Jawo Kisan Kiyashi A Gaza
Sakatare-janar na kungiyar Hizbullah Sheikh Naim Qasem ya fitar da wata sanarwa inda ya yi kakkausar suka da Allah wadai da abin da ya bayyana a matsayin yakin kisan kare dangi da Amurka da Isra’ila ke yi wa al’ummar Palasdinu a Gaza, yana mai zargin kasashen duniya da yin shiru a kan laifukan da suka zarce dukkan matakan jin kai da kuma kyawawan dabi’u na ‘yan adataka.
“Abin da al’ummar Falasdinawan da ake zalunta ke jurewa a Gaza, tun daga cin zarafi na Amurka da Isra’ila, zuwa ta’addanci, kisan kiyashi, jefa su a cikin yunwa, da kashe jama’a, ya wuce duk wani mataki na lamirin dan adam,” in ji Sheikh Qassem.
Ya kuma yi kakkausar suka ga gazawar manyan kasashen duniya da gaza aiwatar da dokokin kasa da kasa, yana mai cewa, “Shiru da kasashen duniya suka yi, abin Allah wadai ne ga gwamnatocin kasashen duniya, musamman na kasashen musulmi da larabawa.
Da yake ishara da kiraye-kirayen baya-bayan nan da kasashe sama da ashirin suka yi na a dakatar da yakin, Sheikh Qassem ya yi ishara da cewa irin wadannan kalamai da cewa ba su isa ba ko kadan, Ya ce, “bai isa ba a ce kasashe 25 sun yi kira da a dakatar da yakin Gaza, wannan furucin kadai bai wadatar ba.
Sheikh Qassem ya yi kira da a kakaba takunkumi kan “Isra’ila”, da gurfanar da su a gaban shari’a, da kuma dakatar da duk wani nau’i na hadin gwiwa da ita.