Kotun kasa da kasa ta ICC ta yi tir da gwamnatin kasar Amurka wacce ta kakabawa al-kalan kotun guda hudu saboda hannu da suke da shi wajen fidda sammacin kama fray ministan HKI Benyamin Natanyahu.

Kotun ta kara da cewa tana goyon bayan alkalanta kuma zata ci gaba da aikinta na tabbatar da adalci a duniya duk tare da abinda suke faskanta.

Kotun ta bayyana cewa tana aikinta ne bisa goyon bayan kasashen duniya 125 wadanda suka fito daga dukkan kusruwowin duniya.

Takunkuman dai ya shafi wadannan alkalai su 4 kuma mata. Kuma sun hana ko wanne daga cikinsu, shiga kasar Amurka kuma idan suna da kadarori ko kudade gwamnatin Amurka ta kwace su.

A cikin watan Nuwamban shekara ta 2024 ne dai kotun ta ICC wacce take zama a birnin Haque ta fidda sammacin kama Firay ministan HKI Benyamin Natanyahu da kuma tsohon ministan yakin kasar Yoav Galant saboda zargin aikata laifukan yaki a Gaza.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Amurka Ta Rufe Ofishin Jakadancinta Da Ke Tel-Aviv Na Haramtacciyar Kasar Isra’ila

Gwamnatin Amurka ta rufe Ofishin Jakadancinta da ke haramtacciyar kasar Isra’ila

Jakadan Amurka a haramtacciyar kasar Isra’ila Mike Huckabee ya sanar a yau Litinin cewa: Wani makami mai linzami na Iran ya fado kusa da ofishin jakadancin Amurka da ke birnin Tel Aviv, wanda ya yi barna kadan amma ba a samu rauni a tsakanin ma’aikatan ba.

A cikin wata sanarwa da ya fitar, ya ce: Daga yau Litinin ofishin jakadancin da sauran ofisoshin Amurka da suke haramtacciyar kasar Isra’ila za su ci gaba da kasancewa a rufe a matsayin matakin riga-kafi.

Jakadan ya kara da cewa: Babban abin da ya sa a gaba shi ne kare lafiyar jami’an diflomasiyyar kasarsa, kuma za su ci gaba da sanya ido kan abubuwan da ke faruwa tare da hadin gwiwar hukumomin haramtacciyar kasar Isra’ila.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Amurka na iya kashe jagoran addini na Iran don mun san inda yake — Trump
  • Ministan Waje: Kwakkwaran Zumunci Da Ake Sadawa Da Sin Ya Yi Tasiri Mai Kyau Ga Al’ummar Rwanda
  • Tinubu Ya Soke Ziyarar Kaduna, Zai Tafi Benuwe Saboda Rikice-Rikice
  • Amurka Ta Rufe Ofishin Jakadancinta Da Ke Tel-Aviv Na Haramtacciyar Kasar Isra’ila
  • Dakarun IRGC Sun Kakkabo Jirahen Yakin HKI Wadanda Ake Sarrafasu Daga Nesa A Lardin Zanjan
  • Ministan Harkokin Wajen Kasar Iran Ya Ce Ba’a Rufe Kofar Diblomasiyya Ba, Matukar HKI Ta Dakatar Da Kaiwa Kasar HKI
  • NAF Na Shirin Siyo Jiragen Yaki Masu Saukar Ungulu Daga Amurka
  • Iran Ta Sanar Da Dakatar Da Tattaunawa Da Amurka A Wannan Lokaci Da Take Fuskantar Yaki Daga Isra’ila
  • Kungiyar Abokan Yarjejeniyar M.D.D Ta Yi Allah Wadai Da Hare-Haren Da Isra’ila Ke Kai Wa Kan Iran
  • Dalilin da muka soke tattaunawar nukiliya da Amurka — Iran