Tinubu ba zai canza Kashim a matsayin mataimakinsa ba a 2027 – APC
Published: 6th, June 2025 GMT
Jam’iyyar APC mai mulki a Najeriya ta musanta labarin da ake ta yadawa cewa akwai yiwuwar Shugaban Kasa Bola Tinubu ya canza mataimakinsa, Kashim Shettima gabanin zaben 2027.
APC ta bakin mataimakin shugabanta na kasa na shiyya Kudu maso Gabas, Dr Ijeoma Arodiogbu, ta musanta zargin inda ta ce wasu ne suka kirkire shi domin su kawar da hankalin mutane.
Ijeoma ya ce, “Yanzu na fara jin labarin. Akwai kyakkyawar alaka da fahimtar juna tsakanin shugaba Tinubu da mataimakinsa Kashim.
Tsohon Alkalin Alkalan Najeriya, Lawal Uwais ya rasu Mun gurfanar da mutum 29 a kotu kan zargin kashe DPO a Kano – ’Yan sanda“Kashim babban jigo ne a wannan tafiya. Mutum ne mai kwakwalwa sosai, yana da alkibla kuma da shi ake yin komai a cikin wannan gwamnatin. Wannan jita-jitar kawai maganar siyasa ce da aka kirkire ta domin a raba kan mutane.,” in ji shi.
Mataimakin shugaban ya kuma ce ba abin mamaki ba ne don an ji irin wadannan maganganun a daidai lokacin da ake tunkarar kakar zabe ta 2027,.
Sai dai ya ce shugaban kasa da mataimakin nasa suna tare sannan suna da sahalewar jam’iyyarsu.
Jita-jitar dai ta fara ne jim kadan bayan gwamnonin APC 22 da shugabannin Majalisar Dokoki ta Kasa da ma sauran shugabannin jam’iyyar sun amince da Tinubu a matsayin dan takara daya tilo na jam’iyyar a zabe mai zuwa.
Gwamnan jihar Imo kuma shugaban Kungiyar Gwamnonin APC, Hope Uzodinma ne dai ya fara gabatar da bukatar, sannan gwamnan Kaduna, Uba Sani, ya goyi bayansa a yayin taron kasa na APC da aka gudanar a dakin taro na fadar shugaban kasa da ke Abuja a kwanakin baya.
উৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
Sulhu Da ‘Yan Bindiga Ya Fara Shan Ƙasa, Sun Yi Garkuwa Da Masallata A Zamfara
Yarjejeniyar, a cewar daukacin mahalarta taron, ta nuna wani gagarumin mataki na kawo karshen tashe-tashen hankula, garkuwa da mutane da satar shanu a Arewa maso Yamma, da kuma yankin Arewa.
Yarjejeniyar wacce Mai Maradin Katsina da Hakimin Kurfi, Alhaji Mansur Amadu Kurfi, da shugaban karamar hukumar, Babangida Abdullahi Kurfi suka shirya, ta gudana ne a dajin Wurma, inda ake fama da rashin tsaro.
Manyan jagororin ‘yan bindigan da suka hada da Alhaji Usman Kachalla Ruga da Sani Muhindinge da Yahaya Sani (Hayyu) da kuma Alhaji Shu’aibu duk sun yi alkawarin tsagaita wuta.
Daga baya suka sako mutanen da suka kama kuma suka bar manoma su koma gonakansu ba tare da wata barazana ba.
Sai dai kasa da wata guda da kulla yarjejeniyar, an tattaro cewa ‘yan bindigar sun sake kai hari a Zamfara inda suka yi awon gaba da masallata da dama.
Wata majiya ta cikin garin, ta shaida cewa, harin ya afku ne a lokacin sallar asuba da misalin karfe 5:30 na safe, inda ‘yan bindigar suka afkawa masallacin, suka kewaye shi, sannan suka tattara masallatan zuwa daji.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp