Ali Shamkhani: Iran Ba Zata Taba Saryar Da Hakkinta Na Makamashin Nukliya Ba
Published: 5th, June 2025 GMT
Mai bawa jagoran Juyin juya halin musulunci shawara kan al-amuran siyasa Ali Shamkhani ya sake tabbatar da cewa kasar Iran ba zata dakatar da aikin tace makamacin Uranium kamar yadda gwamnatin Amurka take so ba. Sannan ya kara da cewa kasar tana kokarin sake gabatar da wata shawara daban ga kasar Amurka.
Ali shamkhani ya fadawa tashar talabijin ta Al-Mayadeen ta kasar Lebanon a wata hira da ta hadasu a jiya Laraba. Ya kuma kara da cewa, a halin yanzu suna rubutun wata shawagara ga gwamnatin Amurka dangane da hakan.
Shamkhani ya kara da cewa wasikar da Amurka aikawa Tehran bata ambaci batun daukewa kasar takunkuman tattalin arziki ko kadan ba. Ya kuma soki kasar ta Amurka a wasikar da ta aikowa Tehran ba tare da ambatun daukewa kasar takunkuman tattalin arziki ba, duk da cewa ta san hakan yana da muhimmanci ga JMI.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Iran: Sojojin Ruwan Iran Sun Kori Jirigin Yakin Amurka Daga Tekun Oman
Sojojin ruwan Iran sun sanar da cewa, wani jirgin ruwan Amurka na yaki da ya yi kokarin shiga tekun Oman, ya fuskanci gargadi daga sojojin ruwan Iran tare da tilasta masa janyewa.
Da saiyar yau Laraba ne dai jirgin sama mai saukar angulu mallakin sojojin ruwa, ya yi gargadi ga jirgin ruwan na Amurka da a karshe ya tilasta masa janyewa.
Da fari, jirgin ruwan yakin na Amurka ya yi wa jirgin sama mai saukar angulu na Iran barazanar kai masa hari, said ai duk da haka sojojin ruwan na Iran sun ci gaba da yin gargadi ga Amurkawan da su kar su shiga cikin ruwan tekun Oman.
Bayan wannan barazana ne aka aikewa jirgin ruwan Amurkan sako daga dakarun tsaron sararyin samaniyar Iran akan cewa, wannan jirin mai saukar angulu yana da cikakkiyar kariya, don haka wajibi ne ga jirgin ruwan na Amurka mai suna “DDG Fitzgerald ya janye.