PDP ce kaɗai jam’iyyar adawa mai ƙarfi a Najeriya — Saraki
Published: 5th, June 2025 GMT
Tsohon Shugaban Majalisar Dattawa, Bukola Saraki, ya ce jam’iyyar PDP ce har yanzu jam’iyyar adawa mafi ƙarfi a Najeriya.
Ya ce PDP tana da ƙarfi kuma za ta iya ƙalubalantar jam’iyya mai mulki a zaɓen 2027.
Barazanar Yajin Aiki: Abuja da wasu jihohi 3 za su faɗa cikin duhu A shekara 25, na kashe tiriliyan 161 wajen inganta lafiya a Afirka – Bill GatesSaraki, wanda ke jagorantar Kwamitin Sulhu na PDP, ya faɗi haka ne a wani taro da ya yi da shugabannin jam’iyyar a Ilorin.
Ya amince cewa wasu sun bar jam’iyyar, amma mutane da dama suna ci gaba da shigowa jam’iyyar.
“PDP ce kawai jam’iyyar adawa ta haƙiƙa,” in ji shi.
“Eh, muna fuskantar ƙalubale, amma muna samun ci gaba. Mutane suna dawowa cikin jam’iyyar, kuma sabbin mambobi suna shigows. Wannan yana nuna cewa har yanzu jam’iyyarmu tana da ƙarfi.”
Ya ce ana ci gaba da gyara jam’iyyar domin ta zama mai haɗin kai da ƙarfi.
Ya ce tarukan shugabannin jam’iyyar da sauran ayyukan sulhu suna nuna alamun nasara.
“Mun fara shiri tun da wuri, kuma muna da shekara biyu kafin zaɓe. Wannan zai ba mu isasshen lokaci mu shirya,” in ji Saraki.
“Ko da wasu za su bar jam’iyyar, da dama za su shigo cikinta.”
Saraki, ya kuma sabunta rajistarsa a matsayin mamba na PDP, kuma ya ce yana farin ciki da irin goyon bayan da ya gani daga ’ya’yan jam’iyyar a matakin ƙananan hukumomi da mazaɓu.
Ya ce wannan yana nuna cewa mutane har yanzu sun yi imani da PDP.
Ya danganta sabon goyon bayan da PDP ke samu da rashin jin daɗin mutane game da yadda ake mulki a matakin tarayya da na jihohi musamman game da rashin tsaro, rashin ayyukan yi, yunwa da kuma rashin shugabanci nagari.
“Mutane sun gaji da halin da ake ciki. Suna son ganin shugabanci na gaskiya ya dawo. Wannan shi ne abin da PDP ke wakilta,” in ji shi.
Saraki, ya tabbatar wa ’ya’yan jam’iyyar da magoya baya a faɗin ƙasa cewa PDP za ta ci gaba da yin sulhu da sake gina jam’iyyar don ta cika burin ‘yan Najeriya.
“Dimokuraɗiyya ba za ta yiwu ba idan babu adawa. Dole ne mu kasance a shirye mu sadaukar da kai da haɗin gwiwa don ƙarfafa tsarin dimokuraɗiyya. Wannan ne abin da PDP ta tsayawa a kai,” in ji shi.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: adawa Dimokuraɗiyya jam iyya Saraki Siyasa jam iyyar a
এছাড়াও পড়ুন:
Majalisar Dattawa ta amince Tinubu ya tura sojojin Najeriya zuwa Jamhuriyar Benin
Majalisar Dattawa a ranar Talata ta amince da bukatar Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ta tura sojojin Najeriya zuwa Jamhuriyar Benin domin tabbatar da dimokuradiyya a kasar.
Majalisar ta kuma ce tana goyon bayan matakin da shugaban ya ɗauka kwanaki kafin haka domin hana yunƙurin kifar da tsarin dimokuraɗiyya a makwabciyar kasar.
Gwamnan Jihar Ribas ya sauya sheka zuwa APC Juyin Mulki: ECOWAS ta ayyana dokar ta-baci a kasashentaBukatar dai na kunshe ne a cikin wata wasiƙa da Shugaban Majalisar, Godswill Akpabio, ya karanta a zauren majalisa yayin zamanta.
Tinubu ya umarci tura sojojin makon da ya gabata domin dakile yunƙurin karɓar mulki ba bisa ka’ida ba a Jamhuriyar Benin da kuma kaucewa rikicewar tsaro a yankin yammacin Afirka.
Sai dai Tinubu bai nemi amincewar majalisa ba kamar yadda kundin tsarin mulki ya tanada.
Bayan karanta wasiƙar, majalisar ta koma zaman kwamiti domin tantance bukatar. A yayin zaman, ’yan majalisa sun tattauna kan tasirin tsaro, jin‑ƙai da diflomasiyya da ke tattare da wannan mataki.
Babbar damuwar a cewarsu ta haɗa da yiwuwar kwararar ’yan gudun hijira zuwa Najeriya, tsaron iyaka da kuma tasirin matakin ga zaman lafiya da tsaro a yankin.
Bayan doguwar muhawara, majalisar ta koma zama a zaurenta, inda ta kada kuri’ar amincewa da matakin shugaban ƙasa cikin rinjaye.
Shugaban Majalisar, Akpabio, ya gabatar da rahoton kwamitin domin tabbatarwa, inda ’yan majalisa suka amince ba tare da wata adawa ba kafin su amince da tura sojojin ta hanyar kada kuri’ar murya karo na biyu.
A jawabin sa, Akpabio ya yabawa Shugaba Tinubu bisa ɗaukar matakan da suka tabbatar da zaman lafiya a yankin da kuma bin ka’idojin kundin tsarin mulki ta hanyar neman amincewar majalisa, ko da bayan tura sojojin cikin gaggawa.
“Wannan mataki ne da ya zama dole. Shugaban Ƙasa ya yi aiki ne domin kare tsaron ƙasa da kuma kare dimokuraɗiyya a yammacin Afirka. Barazana ga kasa ɗaya barazana ce ga kowa,” in ji shi.
Ya ƙara da cewa za a isar da kudurin majalisar ga Shugaban Ƙasa nan take.