PDP ce kaɗai jam’iyyar adawa mai ƙarfi a Najeriya — Saraki
Published: 5th, June 2025 GMT
Tsohon Shugaban Majalisar Dattawa, Bukola Saraki, ya ce jam’iyyar PDP ce har yanzu jam’iyyar adawa mafi ƙarfi a Najeriya.
Ya ce PDP tana da ƙarfi kuma za ta iya ƙalubalantar jam’iyya mai mulki a zaɓen 2027.
Barazanar Yajin Aiki: Abuja da wasu jihohi 3 za su faɗa cikin duhu A shekara 25, na kashe tiriliyan 161 wajen inganta lafiya a Afirka – Bill GatesSaraki, wanda ke jagorantar Kwamitin Sulhu na PDP, ya faɗi haka ne a wani taro da ya yi da shugabannin jam’iyyar a Ilorin.
Ya amince cewa wasu sun bar jam’iyyar, amma mutane da dama suna ci gaba da shigowa jam’iyyar.
“PDP ce kawai jam’iyyar adawa ta haƙiƙa,” in ji shi.
“Eh, muna fuskantar ƙalubale, amma muna samun ci gaba. Mutane suna dawowa cikin jam’iyyar, kuma sabbin mambobi suna shigows. Wannan yana nuna cewa har yanzu jam’iyyarmu tana da ƙarfi.”
Ya ce ana ci gaba da gyara jam’iyyar domin ta zama mai haɗin kai da ƙarfi.
Ya ce tarukan shugabannin jam’iyyar da sauran ayyukan sulhu suna nuna alamun nasara.
“Mun fara shiri tun da wuri, kuma muna da shekara biyu kafin zaɓe. Wannan zai ba mu isasshen lokaci mu shirya,” in ji Saraki.
“Ko da wasu za su bar jam’iyyar, da dama za su shigo cikinta.”
Saraki, ya kuma sabunta rajistarsa a matsayin mamba na PDP, kuma ya ce yana farin ciki da irin goyon bayan da ya gani daga ’ya’yan jam’iyyar a matakin ƙananan hukumomi da mazaɓu.
Ya ce wannan yana nuna cewa mutane har yanzu sun yi imani da PDP.
Ya danganta sabon goyon bayan da PDP ke samu da rashin jin daɗin mutane game da yadda ake mulki a matakin tarayya da na jihohi musamman game da rashin tsaro, rashin ayyukan yi, yunwa da kuma rashin shugabanci nagari.
“Mutane sun gaji da halin da ake ciki. Suna son ganin shugabanci na gaskiya ya dawo. Wannan shi ne abin da PDP ke wakilta,” in ji shi.
Saraki, ya tabbatar wa ’ya’yan jam’iyyar da magoya baya a faɗin ƙasa cewa PDP za ta ci gaba da yin sulhu da sake gina jam’iyyar don ta cika burin ‘yan Najeriya.
“Dimokuraɗiyya ba za ta yiwu ba idan babu adawa. Dole ne mu kasance a shirye mu sadaukar da kai da haɗin gwiwa don ƙarfafa tsarin dimokuraɗiyya. Wannan ne abin da PDP ta tsayawa a kai,” in ji shi.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: adawa Dimokuraɗiyya jam iyya Saraki Siyasa jam iyyar a
এছাড়াও পড়ুন:
Kotu ta tsige dan majalisar da ya sauya sheka zuwa APC
Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja ta tsige dan majalisar wakilai, Abubakar Gummi daga kujerarsa saboda sauya sheka daga jam’iyyar PDP zuwa APC.
Gummi yana wakiltar mazabar Gummi/Bukkuyum ta Jihar Zamfara a majalisar wakilai.
An raba wa iyalan jami’an ’yan sandan da suka rasu a bakin aiki a Borno N63.4m An sake kama shi a cikin ’yan fashi kwana 5 da fitowa daga kurkukuMai shari’a Obiora Egwuatu ne, ya yanke hukuncin, inda ya umarci kakakin majalisar wakilai, Tajudeen Abbas, da ya daina amincewa da Gummi a matsayin dan majalisar da ke wakiltar mazabar Gummi/Bukkuyum.
Haka kuma ya umarci hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) da ta shirya sabon zabe cikin kwanaki 30 domin cike gurbin kujerar dan majalisar.
Jam’iyyar PDP tare da shugaban ta na jihar Zamfara, Jamilu Jibomagayaki, ne suka shigar da karar dan majalisar.
Sun ce bai dace Gummi ya ci gaba da zama a kujerar ba bayan barin jam’iyyar da ta tsayar da shi takara.
Gummi, ta bakin lauyansa ya ce ya fice daga PDP ne saboda rikicin cikin gida da jam’iyyar ke fama da shi a matakin kasa da kuma a mazabarsa.
Amma kotu ta yi watsi da wannan hujjar, inda ta bayyana cewa babu takaddama da za ta ba shi damar ya sauya sheka.
A hukuncin da ya yanke, Mai shari’a Egwuatu ya ce ’yan siyasa dole su mutunta zabin jama’ar da suka kada musu kuri’a a karkashin jam’iyyar da ta tsayar da su takara.
Ya ce doka ba ta yadda da dan siyasa ya bar jam’iyyar da ta taimaka masa wajen lashe zabe sannan ya koma wata jam’iyya ba tare da ajiye mukaminsa ba.
Ya kara da cewa kuri’un da aka kada don dan takarar na jam’iyya ne, ba nasa ne na kashin kansa ba.
“Idan mutum yana son sauya sheka, ka da ya dauki amanar jama’ar da ta zabe shi ya tafi da ita,” in ji alkalin.
Kotu ta kuma umarci Gummi da ya daina karbar albashi da wasu hakkoki a matsayin dan majalisa, tare da mayar da duk kudaden da ya karba daga ranar 30 ga watan Oktoba, 2024, zuwa ranar da aka yanke hukuncin.
Haka kuma, ya gabatar da hujjar mayar da kudaden ga kotu cikin kwanaki 30.
Mai shari’a Egwuatu ya kuma ci Gummi tarar Naira N500,000, domin biyan PDP kudaden da ta kashe wajen shigar da kara.