Aminiya:
2025-06-06@16:06:18 GMT

PDP ce kaɗai jam’iyyar adawa mai ƙarfi a Najeriya — Saraki

Published: 5th, June 2025 GMT

Tsohon Shugaban Majalisar Dattawa, Bukola Saraki, ya ce jam’iyyar PDP ce har yanzu jam’iyyar adawa mafi ƙarfi a Najeriya.

Ya ce PDP tana da ƙarfi kuma za ta iya ƙalubalantar jam’iyya mai mulki a zaɓen 2027.

Barazanar Yajin Aiki: Abuja da wasu jihohi 3 za su faɗa cikin duhu A shekara 25, na kashe tiriliyan 161 wajen inganta lafiya a Afirka – Bill Gates

Saraki, wanda ke jagorantar Kwamitin Sulhu na PDP, ya faɗi haka ne a wani taro da ya yi da shugabannin jam’iyyar a Ilorin.

Ya amince cewa wasu sun bar jam’iyyar, amma mutane da dama suna ci gaba da shigowa jam’iyyar.

“PDP ce kawai jam’iyyar adawa ta haƙiƙa,” in ji shi.

“Eh, muna fuskantar ƙalubale, amma muna samun ci gaba. Mutane suna dawowa cikin jam’iyyar, kuma sabbin mambobi suna shigows. Wannan yana nuna cewa har yanzu jam’iyyarmu tana da ƙarfi.”

Ya ce ana ci gaba da gyara jam’iyyar domin ta zama mai haɗin kai da ƙarfi.

Ya ce tarukan shugabannin jam’iyyar da sauran ayyukan sulhu suna nuna alamun nasara.

“Mun fara shiri tun da wuri, kuma muna da shekara biyu kafin zaɓe. Wannan zai ba mu isasshen lokaci mu shirya,” in ji Saraki.

“Ko da wasu za su bar jam’iyyar, da dama za su shigo cikinta.”

Saraki, ya kuma sabunta rajistarsa a matsayin mamba na PDP, kuma ya ce yana farin ciki da irin goyon bayan da ya gani daga ’ya’yan jam’iyyar a matakin ƙananan hukumomi da mazaɓu.

Ya ce wannan yana nuna cewa mutane har yanzu sun yi imani da PDP.

Ya danganta sabon goyon bayan da PDP ke samu da rashin jin daɗin mutane game da yadda ake mulki a matakin tarayya da na jihohi musamman game da rashin tsaro, rashin ayyukan yi, yunwa da kuma rashin shugabanci nagari.

“Mutane sun gaji da halin da ake ciki. Suna son ganin shugabanci na gaskiya ya dawo. Wannan shi ne abin da PDP ke wakilta,” in ji shi.

Saraki, ya tabbatar wa ’ya’yan jam’iyyar da magoya baya a faɗin ƙasa cewa PDP za ta ci gaba da yin sulhu da sake gina jam’iyyar don ta cika burin ‘yan Najeriya.

“Dimokuraɗiyya ba za ta yiwu ba idan babu adawa. Dole ne mu kasance a shirye mu sadaukar da kai da haɗin gwiwa don ƙarfafa tsarin dimokuraɗiyya. Wannan ne abin da PDP ta tsayawa a kai,” in ji shi.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: adawa Dimokuraɗiyya jam iyya Saraki Siyasa jam iyyar a

এছাড়াও পড়ুন:

Tsohon Ministan Ilimi, Farfesa Jibril Aminu, ya rasu

Tsohon malamin makaranta, dan siyasa kuma ambasada, Farfesa Jibril Aminu ya rasu yana da shekara 85.

Wata majiya daga iyalan mamacin ta tabbatar da rasuwar, kuma Kwamishinan Gidaje da Raya Birane na jihar Adamawa, Hon Abdullahi Prambe ma ya tabbatar da haka.

Ya ce, “Ba za a taba mantawa da gudunmawar shi ba musamman a bangaren ilimi da kiwon lafiya da kuma shugabanci.”

Wata majiya da ke da kusanci da mamacin ta ce za a yi jana’izarsa da misalin karfe 2:00 na rana a Masallacin Kasa da ke Abuja.

Sai dai kawo yanzu, iyalai da ’yan uwan mamaci bas u fid da cikakken bayani kan yadda za a yi jana’izar mamacin ba ko kuma musabbabin rasuwarsa.

An haifi Farfesa Jibril Aminu a garin Song na jihar ta Adamawa a shekara ta 1939, kuma ya rike mukamai da dama a Najeriya.

Daga cikin mukaman da ya rike akwai Ministan Ilimi da Ministan Man Fetur da Jakadan Najeriya a Amurka sannan ya taba zama Sanatan Adamawa ta Tsakiya.

Bugu da kari, Farfesa Jibril kwararren likitan zuciya ne da ya jima yana bayar da gudunmawa wajen ci gaban kasa a fannoni daban-daban.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnan Akwa Ibom ya sauya sheƙa daga PDP zuwa APC
  • Tinubu ba zai canza Kashim a matsayin mataimakinsa ba a 2027 – APC
  • Saudiya Ta Yi Amfani Da Fasahar AI Don Sauwaka Ayukan Hajjin Shekara ta 2025
  • NAJERIYA A YAU: Abubuwan Da Suka Fara Bacewa Yayin Bukukuwan Sallah
  • Bukola Saraki Ya Tallafawa Al’ummar Mokwa Da Gudunmawar Kuɗi
  • Farfesa Jibril Amin Tsoho Ministan Ilim Da, Manfetur A Najeriya Rasu Yana Dan Shekara 85 A Duniya
  • Tsohon Ministan Ilimi, Farfesa Jibril Aminu, ya rasu
  • NAJERIYA A YAU: Yadda Mayar Da Unguwa Mayanka Ke Shafar Lafiyar Al’umma
  • Kotu ta aike da ɗan Tiktok gidan yari kan yin shigar mata a Kano