Aminiya:
2025-09-18@00:41:45 GMT

PDP ce kaɗai jam’iyyar adawa mai ƙarfi a Najeriya — Saraki

Published: 5th, June 2025 GMT

Tsohon Shugaban Majalisar Dattawa, Bukola Saraki, ya ce jam’iyyar PDP ce har yanzu jam’iyyar adawa mafi ƙarfi a Najeriya.

Ya ce PDP tana da ƙarfi kuma za ta iya ƙalubalantar jam’iyya mai mulki a zaɓen 2027.

Barazanar Yajin Aiki: Abuja da wasu jihohi 3 za su faɗa cikin duhu A shekara 25, na kashe tiriliyan 161 wajen inganta lafiya a Afirka – Bill Gates

Saraki, wanda ke jagorantar Kwamitin Sulhu na PDP, ya faɗi haka ne a wani taro da ya yi da shugabannin jam’iyyar a Ilorin.

Ya amince cewa wasu sun bar jam’iyyar, amma mutane da dama suna ci gaba da shigowa jam’iyyar.

“PDP ce kawai jam’iyyar adawa ta haƙiƙa,” in ji shi.

“Eh, muna fuskantar ƙalubale, amma muna samun ci gaba. Mutane suna dawowa cikin jam’iyyar, kuma sabbin mambobi suna shigows. Wannan yana nuna cewa har yanzu jam’iyyarmu tana da ƙarfi.”

Ya ce ana ci gaba da gyara jam’iyyar domin ta zama mai haɗin kai da ƙarfi.

Ya ce tarukan shugabannin jam’iyyar da sauran ayyukan sulhu suna nuna alamun nasara.

“Mun fara shiri tun da wuri, kuma muna da shekara biyu kafin zaɓe. Wannan zai ba mu isasshen lokaci mu shirya,” in ji Saraki.

“Ko da wasu za su bar jam’iyyar, da dama za su shigo cikinta.”

Saraki, ya kuma sabunta rajistarsa a matsayin mamba na PDP, kuma ya ce yana farin ciki da irin goyon bayan da ya gani daga ’ya’yan jam’iyyar a matakin ƙananan hukumomi da mazaɓu.

Ya ce wannan yana nuna cewa mutane har yanzu sun yi imani da PDP.

Ya danganta sabon goyon bayan da PDP ke samu da rashin jin daɗin mutane game da yadda ake mulki a matakin tarayya da na jihohi musamman game da rashin tsaro, rashin ayyukan yi, yunwa da kuma rashin shugabanci nagari.

“Mutane sun gaji da halin da ake ciki. Suna son ganin shugabanci na gaskiya ya dawo. Wannan shi ne abin da PDP ke wakilta,” in ji shi.

Saraki, ya tabbatar wa ’ya’yan jam’iyyar da magoya baya a faɗin ƙasa cewa PDP za ta ci gaba da yin sulhu da sake gina jam’iyyar don ta cika burin ‘yan Najeriya.

“Dimokuraɗiyya ba za ta yiwu ba idan babu adawa. Dole ne mu kasance a shirye mu sadaukar da kai da haɗin gwiwa don ƙarfafa tsarin dimokuraɗiyya. Wannan ne abin da PDP ta tsayawa a kai,” in ji shi.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: adawa Dimokuraɗiyya jam iyya Saraki Siyasa jam iyyar a

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnati ta ƙaddamar da jiragen ruwa na zamani 20 a Sakkwato

Gwamnan Sakkwato, Dakta Ahmad Aliyu, ya ƙaddamar da jiragen ruwa na zamani guda 20, tare da riguna ruwa (life jackets) 2,000, domin rage haɗurran da ke aukuwa sakamakon ambaliya da nutsewar jirage a sassan jihar.

An ƙaddamar da jiragen ne a ƙaramar hukumar Wamakko a ranar Laraba, inda gwamnan ya bayyana cewa wannan mataki na daga cikin shirin gaggawa na tallafa wa al’ummar da ke fama da illar ambaliya da haɗurra a ruwa.

Microsoft ya ƙwace shafukan wasu kamfanoni 340 a Najeriya An kama ɗaya daga cikin manyan kwamandojin IPOB

“Mun dauki wannan mataki bayan rahotannin da muke samu na yawaitar hatsarurruka da rasa rayuka da dukiya sakamakon jiragen katako da mutane ke amfani da su,” in ji Gwamna Ahmad Aliyu.

Gwamnan ya miƙa godiya ga shugabar hukumar bayar da agajin gaggawa ta ƙasa (NEMA), Hajiya Zubaida Umar, bisa hadin kai da goyon bayan da hukumar ke bayarwa domin tabbatar da tsaron rayuka da dukiya, tare da inganta ayyukan ceto da agaji a jihar.

Aminiya ta ruwaito cewa, an horar da direbobin jiragen ruwan da za su riƙa kula da su, kafin a raba su zuwa ƙananan hukumomi goma (10) da suka fi fuskantar barazanar ambaliya da suka haɗa da: Goronyo, Shagari, Sabon-Birni, Wurno, Rabah, Wamakko, Silame, Kebbe, Tambuwal da Isa.

Gwamnan ya kuma yi gargaɗin cewa za a hukunta duk wani da ya ɗauki lodi fiye da ƙima a cikin jiragen, yana mai cewa “wannan jirage da rigar ruwa na jama’a ne, kuma wajibi ne shugabannin ƙananan hukumomi su tabbatar da kula da su yadda ya kamata.”

Sai dai wasu daga cikin mazauna yankunan da za a rabawa jiragen sun bayyana ra’ayinsu dangane da lamarin, inda wani Tanimu Goronyo, daga karamar hukumar Goronyo, ya ce: “Gwamnatin Sakkwato ta kauce hanya.

“Abin da muke bukata a yanzu shi ne hanyoyin mota da magudanan ruwa. Ambaliya tana mamaye yankunan mu ne saboda babu hanya. Idan gwamnati ta kashe wannan kuɗi wajen gina hanya, sai an fi cin moriya.”

Shi ma wani Muhammad Kabiru, daga Silame, ya bayyana farin cikinsa da sayen jiragen, sai dai ya roƙi gwamnati da ta mai da hankali wajen gina hanyoyin mota saboda abin da suka fi buƙata ke nan.

“Mu a Silame jirgi yana da amfani, amma hanyar mota ita ce babbar buƙatar mu. Idan aka samar da ita, ambaliya ba za ta hana mu zirga-zirga ba.”

Yayin da gwamnatin Sakkwato ke ɗaukar matakan gaggawa don rage hatsarurruka da ambaliya ke haifarwa, al’umma na ci gaba da neman tsarin da zai magance tushen matsalar – musamman samar da ingantattun hanyoyi da magudanan ruwa a karkara.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnati ta ƙaddamar da jiragen ruwa na zamani 20 a Sakkwato
  • Microsoft ya ƙwace shafukan wasu kamfanoni 340 a Najeriya
  • Saudiyya ta saki ’yan Najeriya 3 da ta kama kan zargin safarar miyagun ƙwayoyi
  • Jihar Jigawa Ta Amince Da Karin Kasafin Kuɗi Na Naira Biliyan 75 Na Shekarar 2025
  • Mataimakin Shugaban Jam’iyyar APC Na Nasarawa, Aliyu Barde, Ya Rasu
  • DAGA LARABA: Dalilan Tashin Farashin Doya A Wasu Kasuwannin Najeriya
  • NAJERIYA A YAU: Matsayin Doka Kan Hawa Mumbari Ba Tare Da Izinin Gwamnati Ba
  • Gwamnatin Neja Ta Musanta Rahoton Hana Da’awa A Jihar
  • Sarki Sanusi II ya koka kan yawan cin bashin Najeriya
  • NAJERIYA A YAU: Yadda Wasu Al’ummomi Suke Kare Kansu Daga Barnar Ambaliyar Ruwa