Aminiya:
2025-06-22@17:17:25 GMT

PDP ce kaɗai jam’iyyar adawa mai ƙarfi a Najeriya — Saraki

Published: 5th, June 2025 GMT

Tsohon Shugaban Majalisar Dattawa, Bukola Saraki, ya ce jam’iyyar PDP ce har yanzu jam’iyyar adawa mafi ƙarfi a Najeriya.

Ya ce PDP tana da ƙarfi kuma za ta iya ƙalubalantar jam’iyya mai mulki a zaɓen 2027.

Barazanar Yajin Aiki: Abuja da wasu jihohi 3 za su faɗa cikin duhu A shekara 25, na kashe tiriliyan 161 wajen inganta lafiya a Afirka – Bill Gates

Saraki, wanda ke jagorantar Kwamitin Sulhu na PDP, ya faɗi haka ne a wani taro da ya yi da shugabannin jam’iyyar a Ilorin.

Ya amince cewa wasu sun bar jam’iyyar, amma mutane da dama suna ci gaba da shigowa jam’iyyar.

“PDP ce kawai jam’iyyar adawa ta haƙiƙa,” in ji shi.

“Eh, muna fuskantar ƙalubale, amma muna samun ci gaba. Mutane suna dawowa cikin jam’iyyar, kuma sabbin mambobi suna shigows. Wannan yana nuna cewa har yanzu jam’iyyarmu tana da ƙarfi.”

Ya ce ana ci gaba da gyara jam’iyyar domin ta zama mai haɗin kai da ƙarfi.

Ya ce tarukan shugabannin jam’iyyar da sauran ayyukan sulhu suna nuna alamun nasara.

“Mun fara shiri tun da wuri, kuma muna da shekara biyu kafin zaɓe. Wannan zai ba mu isasshen lokaci mu shirya,” in ji Saraki.

“Ko da wasu za su bar jam’iyyar, da dama za su shigo cikinta.”

Saraki, ya kuma sabunta rajistarsa a matsayin mamba na PDP, kuma ya ce yana farin ciki da irin goyon bayan da ya gani daga ’ya’yan jam’iyyar a matakin ƙananan hukumomi da mazaɓu.

Ya ce wannan yana nuna cewa mutane har yanzu sun yi imani da PDP.

Ya danganta sabon goyon bayan da PDP ke samu da rashin jin daɗin mutane game da yadda ake mulki a matakin tarayya da na jihohi musamman game da rashin tsaro, rashin ayyukan yi, yunwa da kuma rashin shugabanci nagari.

“Mutane sun gaji da halin da ake ciki. Suna son ganin shugabanci na gaskiya ya dawo. Wannan shi ne abin da PDP ke wakilta,” in ji shi.

Saraki, ya tabbatar wa ’ya’yan jam’iyyar da magoya baya a faɗin ƙasa cewa PDP za ta ci gaba da yin sulhu da sake gina jam’iyyar don ta cika burin ‘yan Najeriya.

“Dimokuraɗiyya ba za ta yiwu ba idan babu adawa. Dole ne mu kasance a shirye mu sadaukar da kai da haɗin gwiwa don ƙarfafa tsarin dimokuraɗiyya. Wannan ne abin da PDP ta tsayawa a kai,” in ji shi.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: adawa Dimokuraɗiyya jam iyya Saraki Siyasa jam iyyar a

এছাড়াও পড়ুন:

Jami’an tsaro sun ƙwato makamai da kama mutane 398 a Kaduna

Tawagar jami’an tsaron  haɗin gwaiwa ta musamman da Gwamnan Jihar Kaduna, Uba Sani ya kafa domin yaƙi da ayyukan ’yan daba da sace-sacen waya a jihar, ta samu nasarar ƙwato makamai tare da cafke mutane 398 da ake zargi a wurare daban-daban.

Wata sanarwa da jami’in hulɗa da jama’a na rundunar ’yan sanda (PPRO), DSP Hassan Mansir ne ya fitar, na bayyana cewa, an kai samamen ne  cikin gaggawa tare da wasu sahihan bayanan sirri.

Wani ya kashe mahaifiyarsa mai shekara 71 a Akwa Ibom Yin sulhu da ’yan bindiga dabara ce ba gazawa ba — Gwamnatin Sakkwato

Samamen ya sanya wasu da dama daga cikin masu aikata laifuka tserewa daga Jihar Kaduna saboda fargabar kama su.

Sanarwar ta kuma bayyana cewa, a cikin kwanaki tara na farko da rundunar take gudanar ayyukanta, ta kama wani mutum mai suna Mathew Adamu, wanda ya shahara wajen aikata ta’addancin cikin al’umma.

Sanarwar ta ce, rundunar ta ƙunshi rundunar ’yan sandan Najeriya ne a matsayin hukumar da ke jagorantar hukumar, tare da sojoji da Jami’an tsaron farin kaya DSS da Sibil defens da jami’an shige da fice na Najeriya da hukumar gyaran hali da hukumar hana sha da fataucin miyagun ƙwayoyi (NDLEA) da hukumar kiyaye haɗurra ta ƙasa (FRSC) da Hukumar Kwastam ta Najeriya, ciki har da hukumar ’yan banga ta Jihar Kaduna (KADVIS).

DSP Hassan ya bayyana cewa, an samu wata ƙaramar bindiga ƙirar gida daga hannun wani mutum mai suna Adamu Umar, wani fitaccen mai sayar da miyagun ƙwayoyi, wanda za a miƙa ƙararsa ga Hukumar NDLEA mai yaƙi da miyagun ƙwayoyi a Najeriya domin ci gaba da bincike da gurfanar da shi.

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Hikimar Yunƙurin Sake Farfaɗo Da Noman Filanten A Jihar Nasarawa
  • Matsalolin Rayuwa: Matasan Suleja Na Buƙatar Ƙarfafa Gwuiwa
  • Uba Sani ya yi jajen ’yan ɗaurin aure 12 da aka kashe a Filato
  • ’Yan Najeriya da suka maƙale a Isra’ila na neman ɗauki
  • Najeriya ta tura sojoji domin samar da zaman lafiya a Gambia
  • Atiku Da Wasu Sun Kafa Sabuwar Jam’iyya, Sun Nemi INEC Ta Musu Rajista
  • 2027: Manyan ’Yan adawa na neman rajistar sabuwar jam’iyya
  • Jami’an tsaro sun ƙwato makamai da kama mutane 398 a Kaduna
  • NAJERIYA A YAU: Yadda Tsarin Ilimi Ke Karya Gwiwar ’Yan Najeriya
  • Indomie Arewa Ta Ƙaddamar da AI Career Generator Domin Ranar Yara