Gwamnatin Tarayya Za Ta Tallafa Wa Yekuwar Rigakafin Cutar Ƙyandar Jamus
Published: 5th, June 2025 GMT
Ministan ya bayyana gabatarwar da C-WINS ta yi a matsayin mai motsa zuciya kuma mai cike da ƙarin haske.
Ya ce: “A yau na koyi abubuwa da dama. Yawancin ’yan Nijeriya, kamar ni kai na, sun san cutar masassarar cizon sauro amma ba su san da ƙyandar jamus da mummunan tasirin ta ba.
“Gaskiya batun cewa za a iya haihuwar yara makafi, kurame ko kuma masu nakasar zuciya sakamakon kamuwa da ƙyanda daga uwa a lokacin ɗaukar ciki babbar masifa ce da ya kamata mu haɗa kai mu daƙile ta.
Ya ƙara da cewa ma’aikatar za ta haɗa hannu da sauran hukumomin da suka dace wajen tsara saƙonnin faɗakarwa da shirye-shiryen ilimantar da al’umma.
Ya kuma shawarci tawagar da su nemi haɗin kan Majalisar Tarayya domin samun cikakken goyon baya na doka.
Ya ce: “Ba ma so wannan zama ya tsaya nan kawai. Mu mayar da wannan haɗin gwiwa abin da zai ɗore, mai amfani, kuma mai faɗi da tasiri. Rigakafi ya fi magani — kuma wannan fannin ne inda bayani ke ceton rayuka ainun.”
A cikin nata jawabin, jagorar tawagar C-WINS, Dakta Nihinlola Mabogunje, ta jaddada gaggawar wayar da kan jama’a kafin lokacin fara kamfen ɗin.
Ta gabatar da cikakken bayani kan muhimmancin rigakafin daga cututtukan ƙyandar jamus fata, musamman a matsayin da Nijeriya ke da shi wajen yawaitar waɗannan cututtuka.
Dakta Mabogunje ta bayyana cewa Nijeriya tana da kusan kashi 20 cikin ɗari na dukkan cututtukan ƙyandar da ake samu a duniya, inda yankin Arewa-maso-gabas yake ɗauke da fiye da kashi 60 cikin ɗari na waɗanda abin ya shafa a ƙasar nan.
Dangane da ƙyandar jamus, ta bayyana cewa cutar tana barazana musamman ga mata masu juna biyu, domin kamuwa da cutar a watannin farko na ɗaukar ciki yana iya janyo haihuwar jarirai masu nakasa kamar makanta, kurmancewa ko lalacewar zuciya.
Ta tabbatar da cewa rigakafin da za a yi amfani da shi yana da inganci kuma ba shi da wani haɗari ga lafiyar mutum, tana mai cewa tun tuni ake amfani da shi, fiye da shekaru 50 a duniya, kuma ya ceci rayuka sama da miliyan 94.
Ta kuma yaba da aikin Hukumar NAFDAC wajen tantancewa da amincewa da rigakafin domin amfani da shi a Nijeriya.
Ta roƙi Gwamnatin Tarayya da ta jagoranci faɗakarwar a matakin ƙasa domin kawar da ji-ta-ji-ta da ƙarfafa gwiwar jama’a.
Likita Mabogunje ta ce: “Don cimma burin kashi 95 na yawan masu karɓar rigakafi, muna buƙatar saƙonnin da suka dace, masu sahihanci da kuma daidaito, waɗanda za a isar ta hanyoyin da ’yan Nijeriya suke yawan dogaro da su a kullum.”
A martanin sa, Minista Idris ya umurci jami’an sashen sadarwa na ma’aikatar sa da su yi aiki tare da C-WINS domin ƙirƙirar kayan faɗakarwa da suka dace da al’adun jama’a, waɗanda za a yaɗa ta kafafen watsa labarai na gwamnati da masu zaman kan su a dukkan faɗin ƙasar nan.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Kashinku Ya Bushe: Sojoji Sun Lashi Takobin Kawo Ƙarshen ‘Yan Ta’adda A Zamfara Da Katsina
Abubakar ya tabbatar da cewa rundunar na da cikakken niyyar kare sararin samaniyar Nijeriya da rayuka da dukiyoyi a faɗin ƙasar nan.
Ya kuma gode wa Shugaba Bola Ahmed Tinubu saboda irin goyon bayan da yake bai wa sojoji, musamman ta fannin kayan aiki da walwalar ma’aikata.
A makon da ya gabata, rundunar ta kashe aƙalla ‘yan ta’adda 20 a wani samame da aka kai Garin Mani, da ke ƙaramar hukumar Maru a Jihar Zamfara.
Wannan farmaki ya biyo bayan luguden wuta da aka riƙa yi wa ‘yan bindiga da ke cin karensu ba babbaka.
Shugaban sojin ya ce motsa jiki abu ne da ya zama dole ga dukkanin ma’aikata, kuma babu wanda zai samu ƙarin girma ba tare da cikakken lafiyar jiki da ƙwaƙwalwa ba.
Don haka, ya amince a gina sababbin wuraren motsa jiki a sansanonin rundunar Sojin Sama da kuma siyan sabbin kayan motsa jiki don raba wa sassan rundunar sama da 22.
Ya bayyana cewa aikin motsa jikin ba wai motsa jiki kawai ba ne, amma yana nuna karfi da daidaito da kuma ƙudirin rundunar wajen kare Nijeriya.
Ya buƙaci dakarun su kasance masu jajircewa da haƙuri domin cimma zaman lafiya.
Wannan aikin motsa jiki ana yin sa ne sau uku a shekara a dukkanin sassan rundunar Sojin Sama domin ƙarfafa jiki, haɗin kai da kuma nuna wa jama’a da maƙiya cewa rundunar Sojin Sama ta kasance cikin shiri, kuma za ta ci gaba da kare Nijeriya.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp