Mahajjata aikin hajjin bana suna ci gaba da tururuwa zuwa tsayiwar Arafat a yau Alhamis

Mahajjata na ci gaba da tururuwa zuwa Arafat domin gudanar da muhimmin rukunnan aikin Hajji.

Mahajjata suna gudanar da ranarsu tun daga ketowar alfijir har zuwa bayan sallar isha’i a filin Arafat, bayan sun gudanar da ibadar ranar Tarwiyah, wadda mahajjaci ya yi a Mina, yana taqaita salloli ba tare da hada su ba.

A safiyar rana ta goma, mahajjata za su sake komawa Mina don jifan Jamarat al-Aqaba, kafin su yi aski ko saisaye, su yanka dabbar layya, Sannan su nufi dakin Ka’aba domin yin Tawafin Hajji.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Direbobi sun toshe babbar hanyar Kogi sakamakon harbe abokan aikinsu

Wasu direbobin manyan motoci sun rufe hanyar Lokoja zuwa Ajaokuta da ke Jihar Kogi domin nuna fushinsu bayan jami’an tsaro sun harbi ɗaya daga cikinsu da kuma mataimakinsa.

Rahotanni sun ce lamarin ya faru ne lokacin da jami’an tsaro suka harbi mutanen biyu saboda sun ƙi tsayawa a wajen binciken da aka tsayar da su.

Ambaliyar Mokwa: An gano gawar yara 7, jama’a na neman agaji Kotu ta aike da ɗan Tiktok gidan yari kan yin shigar mata a Kano

Sai dai, babu wanda ya mutu sakamakon harbin.

An garzaya da su asibiti domin ba su kulawar gaggawa.

Hakan ne, ya sa sauran direbobin suka fusata, suka toshe bakin gadar Ganaja da ke babbar hanyar Lokoja zuwa Ajaokuta.

Sun ƙi ɗauke motocinsu har sai da sojoji suka iso wajen domin kwantar da tarzomar.

Rufe hanyar ta haddasa cunkoso mai yawa, inda matafiya da ma’aikata suka kasa zuwa wuraren aikinsu.

Wasu ma’aikata sun yi tafiya mai nisa a ƙafa, yayin da wasu suka koma gida suka haƙura da zuwa wajen ayyukansu.

Aliyu Dansabe, wani ma’aikaci, ya ce: “Na yi tafiya mai nisa daga rukunin gidaje na Governor Idris Wada har zuwa ofishina, kimanin kilomita bakwai.

“Lamarin ya gajiyar da ni sosai kuma ya tayar min da hankali. Muna godiya da zuwan sojoji da suka shawo kan lamarin.”

Kakakin Rundunar ‘Yan Sandan Jihar Kogi, SP William Aya, ya tabbatar da cewa an shawo kan lamarin.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Saudiya Ta Yi Amfani Da Fasahar AI Don Sauwaka Ayukan Hajjin Shekara ta 2025
  • Yadda Manzon Allah (SAW) Ya Yi Aikin Hajji (3)
  • Sakon Jagoran Juyin Juya Halin Musulunci Ga Mahajjatan Aikin Hajjin Bana A Kasa Mai Tsarki
  • Hajjin Bana: Falalar Tsayuwar Arfa
  • Maniyyata na hawan Arfa a kasar Saudiyya
  • Direbobi sun toshe babbar hanyar Kogi sakamakon harbe abokan aikinsu
  • Sojojin HKI Suna Ci Gaba Da Kashe Falasdinawa Wadanda Suke Jin Yunwa A Gaza
  • Hukumar Alhazai Ta Jihar Jigawa Ta Yi Tanadi Na Musamman Ga Alhazanta A Mina
  • Yanzu-yanzu: JUSUN Ta Dakatar Da Yajin Aikin Da Fara A Faɗin Ƙasa Baki Ɗaya