Abubakar ya tabbatar da cewa rundunar na da cikakken niyyar kare sararin samaniyar Nijeriya da rayuka da dukiyoyi a faɗin ƙasar nan.

Ya kuma gode wa Shugaba Bola Ahmed Tinubu saboda irin goyon bayan da yake bai wa sojoji, musamman ta fannin kayan aiki da walwalar ma’aikata.

A makon da ya gabata, rundunar ta kashe aƙalla ‘yan ta’adda 20 a wani samame da aka kai Garin Mani, da ke ƙaramar hukumar Maru a Jihar Zamfara.

Wannan farmaki ya biyo bayan luguden wuta da aka riƙa yi wa ‘yan bindiga da ke cin karensu ba babbaka.

Shugaban sojin ya ce motsa jiki abu ne da ya zama dole ga dukkanin ma’aikata, kuma babu wanda zai samu ƙarin girma ba tare da cikakken lafiyar jiki da ƙwaƙwalwa ba.

Don haka, ya amince a gina sababbin wuraren motsa jiki a sansanonin rundunar Sojin Sama da kuma siyan sabbin kayan motsa jiki don raba wa sassan rundunar sama da 22.

Ya bayyana cewa aikin motsa jikin ba wai motsa jiki kawai ba ne, amma yana nuna karfi da daidaito da kuma ƙudirin rundunar wajen kare Nijeriya.

Ya buƙaci dakarun su kasance masu jajircewa da haƙuri domin cimma zaman lafiya.

Wannan aikin motsa jiki ana yin sa ne sau uku a shekara a dukkanin sassan rundunar Sojin Sama domin ƙarfafa jiki, haɗin kai da kuma nuna wa jama’a da maƙiya cewa rundunar Sojin Sama ta kasance cikin shiri, kuma za ta ci gaba da kare Nijeriya.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Yan bindiga Zamfara

এছাড়াও পড়ুন:

Sojojin Yemen Sun Kai Hari Kan Filin Jirgin Ben Gurium Na Haramtacciyar Kasar Isra’ila

Sojojin Yemen sun kai hari kan filin jirgin saman Ben Gurium a wani aiki na musamman na tallafawa al’ummar Gaza

Sojojin Yemen sun sanar da kai wani gagaruminj hari kan tashar jirgin saman Lod da ke yankin Jaffa da aka mamaye ta hanyar amfani da makami mai linzami kirar Falasdinu 2.

Hari ya gudana daidai inda aka tsara shi, kuma ya haifar da firgici da ya kai ga miliyoyin yahudawan sahayoniyya gudu tare da shigewa maboyar karkashin kasa kamar burage. Har ila yau, harin ya dakatar da dukkan ayyukan filin jirgin, tare da hana wani jirgin dakon kaya na sojan Amurka sauka a filin jirgin sama na Ben Gurium a rana ta biyu a jere.

A cikin wannan yanayi ne rundunar sojin Yemen ta jadadad cewa: Makiya yahudawan sahayoniyya masu laifi, ba za su taba samun sassauci ko rangwame daga sojojin Yemen ba, sai karin fuskantar hare-hare da makamai masu linzami da jiragen sama marasa matuka ciki, don mayar da martani kan laifukan da suke aikatawa kan al’ummar Falastinu.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sallar Layya: Gwamnan Zamfara Ya Buƙaci Musulmin Su Tuna Da Muhimmancin Sadaukarwa Da Halin Ƙwarai
  • Ministan Tsaro Ya Yi Gargadin Sake Dawowar Boko Haram Na Barazana Ga Nijeriya
  • Sojoji Sun Daƙile Harin Ƴan Ta’adda, Sun Kashe Wasu Da Yawa A Borno
  • Sojojin Yemen Sun Kai Hari Kan Filin Jirgin Saman Ben Gurion Na Haramtacciyar Kasar Isra’ila
  • Jami’an Tsaron A Nan Iran Sun Kama Yan Kungiyar ISIS Kafin Su Aiwatar Da Hare-Hare
  • Rundunar ‘Yan Sanda A Kano Ta Haramta Bukukuwan Hawan Sallah A Kano
  • DSS Da Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 45 A Neja
  • Sojojin Yemen Sun Kai Hari Kan Filin Jirgin Ben Gurium Na Haramtacciyar Kasar Isra’ila
  • Gwamnan Katsina Ya Bukaci Hadin Gwiwa Da ‘Yan Kasuwa Domin Cigaban Jihar