HausaTv:
2025-06-04@11:09:24 GMT

Fira Ministan Kasar Senegal Yana Ziyarar Aiki A Kasashen Yammacin Afirka

Published: 2nd, June 2025 GMT

A ranar Alhamis da ta gabata ce Fira ministan kasar Senegal Usman Sonko ya bude ziyarar aiki a kasashen yamamcin Afirka domin kara dankon zumunci da kasashen.

Daga cikin kasashen da ziyarar ta shafa dai akwai Cote-De Voire, Serra Lione, da Guinea Conakry .

A makon da ya gabata ne dai a yayin taron kira ga masu zuba hannun jari a kasar, senegak aka sanar da shirin ziyarar ta Fira ministan zuwa wadannan kasashe.

A Zangon farko na ziyarar a kasar Cote De Voire, fira ministan ya gana da Amadu Hot, wanda ya kasance dan takarar da Senegal ta tsayar, domin neman shugabancin Bankin Raya kasashen Afirka. Haka nan kuma ya gana da sabon shugaban Bankin na Raya kasashen Afirka, dan asalin kasar Mouritania Sidi Would Taha, ya kuma tattauna hanyoyin bunkasa dangantaka da bankin.

A kasar Guinea Conakri kuwa, fira minstan na Senegal ya gana da takwaransa  Amadu Bah, inda suka tattauna hanyoyin bunkasa dangantaka a tsakanin kasashensu.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Mali: Kotu Ta Yi Watsi Da Neman Dage Haramcin Da Aka Yi Wa Jam’iyyun Siyasar Kasar

 Wata kotun kasar Mali ta kori karar da aka shigar a gabata, don neman soke matakin da majalisar soj0jin kasar ta dauka na rusa jam’iyyun siyasa gaba daya.

A ranar 13 ga watan Mayu ne da ya gabata ne majalsiar koli ta sojojin kasar Mali ta fitar da dokar haramta dukkan jam’iyyun siyasa a kasar wadanda yawansu ya kai 300, tare da manusar sake fasalinsu.

Wasu lauyoyi da kuma ‘yan siyasar kasar ne dai su ka shigar da karar a gaban kotu, daga cikinsu har da ‘Montagal Tal’ wanda ya kasance jagoran daya daga cikin jam’iyyun da aka majalisar sojojin ta soke.

Masu shigar da karar, sun bayyana matakin da majalisar sojan kasar ta dauka da cewa keta hurumin ‘yancin siyasa ne da kuma yencin yin taruka.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Shugaban Kasar Iran Ya Jaddada Cewa: Amurka Da Isra’ila Suna Da Mugun Nufi Kan Iran Da Kasashen Musulmi
  • Iran ta bukaci hadin kan al’ummar Lebanon wajen warware matsalolin kasar
  • Mali: Kotu Ta Yi Watsi Da Neman Dage Haramcin Da Aka Yi Wa Jam’iyyun Siyasar Kasar
  • Sabon Firay Ministan Sudan Ya Bukaci Kasashen Dake Taimaka Wa “RSF” Da Su Daina
  • Arakci: Cinikayya A Tsakanin Iran Da Masar Za Ta Kara Bunkasa
  • Sabon Fira Ministan Sudan Ya Bukaci Kasashen Dake Taimaka Wa “RSF” Da Su Daina
  • Kasar Iran Ta Soki Rahoton Hukumar IAEA Na Baya-Bayan Nan Shirinta Na Makamashin Nukiliya
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Yana Ziyarar Aiki A Kasar Masar, inda Ya Gana Da Shugaban Kasar
  • Araghchi zai fara ziyarar kwanaki biyu a kasashen Masar da Lebanon