Kasashen Larabawa karkashin jagorancin Saudiyya sun bayyana rashin jin dadinsu ga Isra’ila, kan hana su ziyartar yankunan Falasdinawa

Ministocin harkokin wajen kasashen Larabawa sun bayyana rashin jin dadinsu ga gwamnatin Isra’ila, game da rashin amincewa da tawagar kungiyar kasashen ta ziyarci yankin da aka mamaye a Gabar Yamma da kogin Jordan don tattaunawa da shugaban Falasdinawa.

A wani taron manema labarai, ministan harkokin wajen Saudiyya, Yarima Faisal bin Farhan Al Sa’ud, ya ce matakin da Isra’ila ta dauka kamar watsi ne da tayin zaman lafiya.

A dai tsara a wannan Lahadi ne ministocin kasashen Saudiyya, Hadaddiyar Daular Larabawa, Masar, Jordan, Qatar, da Turkiyya, karkashin jagorancin ministan harkokin wajen Saudiyya Yarima Faisal bin Farhan za su isa birnin Ramallah domin ganawa da shugaban hukumar Falasdinu Mahmoud Abbas, a cewar Hussein al-Sheikh, mataimakin shugaban hukumar ta PA.

Wannan dai za ta kasance ziyara mafi girma da Saudiyya za ta kai yankin tun bayan da Isra’ila ta mamaya yankin a shekarar 1967.

Ziyarar ta zo ne a daidai lokacin da yarima mai jiran gado na Saudiyya Mohammed bin Salman ke kokarin ganin kasashen duniya su amince da Falasdinu a matsayin kasa.

Daga bisani Shugaban kungiyar kasashen Larabawa da ministoci hudu sun gana da shugaban Falasdinawa Mahmoud Abbas ta kafar Intanet.

Isra’ila dai ta ce ba za ta amince da tawagar ministocin kasashen Larabawa karkashin jagorancin Saudiyya su ziyarci yankin Isra’ila saboda ta lura hukumomin Falasdinawan na shirin yin amfani da ziyarar ne wajen farfado da kiran samar da kasar Falasdinawa.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: kasashen Larabawa

এছাড়াও পড়ুন:

Kasashen AES zasu kafa kotun hukunta manyan laifuka ta kungiyar

Ministocin shari’a na Burkina Faso, Mali da Nijar sun amince da kafa kotun hukunta laif  uka da kare hakkin bil’adama ta kungiyar tarayyar kasashen Sahel.

Haka kuma za a gina wani gidan yari mai cikakken tsaro a yankin, mai alaka da wannan kotun, domin karfafa hanyoyin yaki da ta’addanci da aikata laifuka a yankin.

Sun bayyana hakan ne bayan taron da suka gudanar a birnin Bamako a ranakun 29 da 30 ga watan Mayu.

Kotun hukunta manyan laifuka da kare hakkin bil’adama a yankin Sahel A cewar shafin labarai na APANews, za ta dauki nauyin “duba laifukan cin zarafin bil’adama, laifuffukan yaki, kisan kiyashi da ta’addanci, halatta kudaden haram da kuma cin zarafi mai tsanani na ‘yancin dan adam da sauran manyan laifuka masu alaka.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Mali: Kotu Ta Yi Watsi Da Neman Dage Haramcin Da Aka Yi Wa Jam’iyyun Siyasar Kasar
  • Iran Ta Yi Watsi Da Da’awar Kungiyar Hadin Kan Kasashen Larabawa Na Da’awar Mallakar Wasu Yankunan Iran
  • Turkiya: An Bude Tattaunawa A Tsakanin Rasha Da Ukiraniya
  • Hajji ta bayan fage: Saudiyya ta hana mahajjata 269,000 shiga Makka
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Yana Ziyarar Aiki A Kasar Masar, inda Ya Gana Da Shugaban Kasar
  • Sojojin Mamayar Isra’ila Sun Kai Hari kan Falasdinawa Masu Karban Agajin Jin Kai A Rafah
  • Kasashen AES zasu kafa kotun hukunta manyan laifuka ta kungiyar
  • Oman ta mika wa Iran takardun shawararin Amurka game da tattaunawar nukiliya
  • Isra’ila ta hana tawagar kasashen Larabawa shiga gabar yammacin kogin Jordan