Ma’aikatar Harkokin Wajen Iran ta bayyana cewa: Rahoton IAEA na nuna son kai kuma an shirya shi ne a karkashin tasirin wasu kasashe

Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran ya bayyana cewa: Rahoton da hukumar kula da makamashin nukiliya ta duniya ta fitar ya kunshi maimaici da wuce gona da iri, yana mai jaddada cewa, an shirya wannan rahoton ne karkashin tasirin wasu kasashen Turai.

Ya bayyana takaicinsa kan yadda kasashen yammacin duniya ke cutar da martabar wata kungiya ta duniya ta hanyar siyasantar da ayyukanta.

A farkon taron manema labarai na mako-mako, Baghaei ya yi la’akari da zagayowar ranar wafatin Imam Khumaini (Allah ya kara masa yarda) da shahidan juyin juya halin Musulunci. Ya kara da cewa: Ma’aikatar harkokin wajen kasar na ci gaba da gudanar da ayyukanta na bin diddigin batutuwan da suka shafi diflomasiyya, yana mai nuni da ziyarar da ministan harkokin wajen Iran ke yi a kasar Masar a halin yanzu, da ziyarar da zai kai kasar Lebanon gobe, da kuma gajeriyar ziyarar ministan harkokin wajen kasar Oman a birnin Tehran. Ya kuma bayyana ziyarar da mataimakin shugaban kasar Iran na farko ya kai kasar Tajikistan domin halartar taron kasa da kasa, da kuma ziyarar shugaban majalisar shawarar Musulunci ta Iran yake yi a kasashen Latin Amurka, inda ya jaddada cewa ayyukan sun hada da batun abubuwan dasuka shafi kasashen da na kasa da kasa.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: harkokin wajen

এছাড়াও পড়ুন:

Fira Ministan Kasar Senegal Yana Ziyarar Aiki A Kasashen Yammacin Afirka

A ranar Alhamis da ta gabata ce Fira ministan kasar Senegal Usman Sonko ya bude ziyarar aiki a kasashen yamamcin Afirka domin kara dankon zumunci da kasashen.

Daga cikin kasashen da ziyarar ta shafa dai akwai Cote-De Voire, Serra Lione, da Guinea Conakry .

A makon da ya gabata ne dai a yayin taron kira ga masu zuba hannun jari a kasar, senegak aka sanar da shirin ziyarar ta Fira ministan zuwa wadannan kasashe.

A Zangon farko na ziyarar a kasar Cote De Voire, fira ministan ya gana da Amadu Hot, wanda ya kasance dan takarar da Senegal ta tsayar, domin neman shugabancin Bankin Raya kasashen Afirka. Haka nan kuma ya gana da sabon shugaban Bankin na Raya kasashen Afirka, dan asalin kasar Mouritania Sidi Would Taha, ya kuma tattauna hanyoyin bunkasa dangantaka da bankin.

A kasar Guinea Conakri kuwa, fira minstan na Senegal ya gana da takwaransa  Amadu Bah, inda suka tattauna hanyoyin bunkasa dangantaka a tsakanin kasashensu.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Soki Rahoton Hukumar Kula Da Makamashin Nukiliya Ta Duniya Kan Kasarsa
  • Arakci: Cinikayya A Tsakanin Iran Da Masar Za Ta Kara Bunkasa
  • Fira Ministan Kasar Senegal Yana Ziyarar Aiki A Kasashen Yammacin Afirka
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Yana Ziyarar Aiki A Kasar Masar, inda Ya Gana Da Shugaban Kasar
  • Araghchi zai fara ziyarar kwanaki biyu a kasashen Masar da Lebanon
  • Nukiliya : Iran ta gargadi kasashen yamma akan daukar duk wani irin mataki kan ta
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Tattauna Darakta-Janar Na Hukumar Kula Da Makamashin Nukiliya Ta Duniya
  • Jamhuriyar Musulunci Ta Iran Ta Gargadi Hukumar Kula Da Makamashin Nukiliya Ta Duniya Da Wasu Kasashe
  • Nukiliya : Tehran ta soki rahoton IAEA da cewa bai da tushe