Araghchi zai fara ziyarar kwanaki biyu a kasashen Masar da Lebanon
Published: 2nd, June 2025 GMT
A wani lokaci yau Litini ne ministan harkokin wajen Iran Abbas Araghchi zai fara ziyarar kwanaki biyu a kasashen Masar da Lebanon.
Yayin ziyarar Araghchi zai gana da manyan jami’an Masar da na Lebanon domin tattauna dangantakar da ke tsakanin kasashen biyu dama rikicin yankin.
Ziyarar Araghchi a Masar za ta gudana ne bisa gayyatar takwaransa na Masar Badr Abdelatty.
Ana sa ran ministan harkokin wajen na Iran zai gana da shugaban Masar Abdel Fattah al-Sisi, da takwaransa Badr Abdelatty, da kuma wasu masu fada a ji a fannin tattalin arzikin Masar.
Da yake karin haske kan manufar ziyarar, mai kula da harkokin Iran a Alkahira ya ce, rikice-rikicen yankin da suka hada da hare-haren wuce gona da iri na Isra’ila a Gaza da kuma rikicin Sudan da Libya, na daga cikin batutuwan da bangarorin zasu musayar ra’ayi .
Dangane da alakar da ke tsakanin Tehran da Alkahira, ya ce ana ci gaba da samun ci gaba, tare da tuntubar juna da tattaunawa mai zurfi tsakanin ministocin harkokin wajen kasashen biyu.
Ya ce yana fatan Iran da Masar za su dauki mataki na karshe don kyautata alakarsu nan gaba kadan. Ban da haka kuma, Iran tana goyon bayan adawar Masar na tilastawa ‘yan Gaza gudun hijira.
A watan Disamba na shekarar 2024, shugaban kasar Iran Massoud Pezechkian ya ziyarci Masar, ziyarar farko da shugaban kasar Iran ya kai kasar Larabawar tun shekara ta 2013.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Aragchi: Iran Tana Goyon Bayan Tattaunawa Saboda Hadin Kai Tsakanin Mutanen Lebanon
Ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Aragchi wanda yake ziyar aiki a kasar Lebanon bayyana cewa kasarsa tana goyon bayan hadin kan mutanen kasar Lebanon.
Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya nakalto ministan yana fadar haka bayan ganawarsa da shugaban majalisar dokokin kasar ta Lebanon a yau Talata a birnin Beirut babban birnin kasar.
Aragchi ya ce kasar Iran tana goyon bayan kasar Lebanon ta hanyar kungiyar Hizbullah. Kuma tana goyon bayanta kan HKI wacce take mamaye da wasu yankuna a kasar. Muna goyon bayan gwamnati da mutane a duk wani kokarin da zasu yi na kwato yankunan kasar wadanda HKI take mamaye da su.
Ministan kafin haka ya bayyana cewa JMI tana daga cikin kasashen da zasu taimakawa kasar Lebanon ta sake gina wuraren da HKI ta lalata a yankin shekarar da ta gabata. Kuma muna goyon bayan tattaunawa tsakanin yan kasa.