HausaTv:
2025-09-18@00:42:59 GMT

Araghchi zai fara ziyarar kwanaki biyu a kasashen Masar da Lebanon

Published: 2nd, June 2025 GMT

A wani lokaci yau Litini ne ministan harkokin wajen Iran Abbas Araghchi zai fara ziyarar kwanaki biyu a kasashen Masar da Lebanon.

Yayin ziyarar Araghchi zai gana da manyan jami’an Masar da na Lebanon domin tattauna dangantakar da ke tsakanin kasashen biyu dama rikicin yankin.

Ziyarar Araghchi a Masar za ta gudana ne bisa gayyatar takwaransa na Masar Badr Abdelatty.

Ana sa ran ministan harkokin wajen na Iran zai gana da shugaban Masar Abdel Fattah al-Sisi, da takwaransa Badr Abdelatty, da kuma wasu masu fada a ji a fannin tattalin arzikin Masar.

Da yake karin haske kan manufar ziyarar, mai kula da harkokin Iran a Alkahira ya ce, rikice-rikicen yankin da suka hada da hare-haren wuce gona da iri na Isra’ila a Gaza da kuma rikicin Sudan da Libya, na daga cikin batutuwan da bangarorin zasu musayar ra’ayi .

Dangane da alakar da ke tsakanin Tehran da Alkahira, ya ce ana ci gaba da samun ci gaba, tare da tuntubar juna da tattaunawa mai zurfi tsakanin ministocin harkokin wajen kasashen biyu.

Ya ce yana fatan Iran da Masar za su dauki mataki na karshe don kyautata alakarsu nan gaba kadan. Ban da haka kuma, Iran tana goyon bayan adawar Masar na tilastawa ‘yan Gaza gudun hijira.

A watan Disamba na shekarar 2024, shugaban kasar Iran Massoud Pezechkian ya ziyarci Masar, ziyarar farko da shugaban kasar Iran ya kai kasar Larabawar tun shekara ta 2013.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Yawan Hatsin Da Aka Girbe A Kasar Sin Tsakanin Shekarar 2021-2025 Ya Kai Wani Sabon Matsayi

 

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Chadi:  Majalisa ta amince a baiwa shugaban kasa  damar ci gaba da Mulki har karshen rayuwa
  • Yawan Hatsin Da Aka Girbe A Kasar Sin Tsakanin Shekarar 2021-2025 Ya Kai Wani Sabon Matsayi
  • Sin Ta Daga Zuwa Mataki Na 10 A Jadawalin GII Na Kasashen Dake Kan Gaba A Fannin Kirkire-Kirkire
  • An Fara Taron Hukumar Makamashin Nukliya Ta Duniya IAEA Karo Na 69 A Birnin Vienna
  • Pezeshkian: Ya kamata kasashen musulmi su yanke alaka da gwamnatin sahyoniya tare da kiyaye hadin kai
  • Tawagogin Sin Da Na Amurka Sun Sake Tattaunawa Game Da Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya A Rana Ta Biyu
  • Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Dakatar Da Shuka Kiyayya Da Tashin-Tashina A Tekun Kudancin Sin
  • Shugaban Kasar Iran Ya Gana Da Sarkin Kasar Qatar A Birnin Doha
  • Tattalin Arzikin Sin Ya Samu Ci Gaba Ba Tare Da Tangarda Ba A Watan Agusta
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Qatar, Turkiyya, Pakistan Da Labanon A Doha