Yawan Mutanen Da Suka Rasa Rayukansu A Ambaliyan Ruwa A Jihar Niger Na Najeriya Ya Kai 151
Published: 31st, May 2025 GMT
Shugaban hukumar bada agajin gaggawa a jihar Naija na tarayyar Najeriya NSEMA ya basa sanarwan cewa yawan mutanen da suka rasa rayukansu sanadiyyar ambaliyar ruwa a ranar Alhamis data gabata a karamar hukumar Mokwa ya kai 151 bayan an sake gano karin gawakin mutane 36.
Jaridar Daily Trust ta Najeriya ta nakalto Abdullahi Arah yana cewa banda wadanda suka rasa rayukansu mutane 11 ne suka ji rauni.
Arah yace gidaje 503 ne suka rushe a jihar sannan wasu 265 suka lalace. Banda haka akwai gadoji biyu da hanyoyi biyu wadanda ruwan ya sharesu.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Jaridar Washington Post Ta Ce; Yeman Ta Gurguta Ayyukan Tashoshin Jiragen Ruwan Isra’ila
Jaridar Washington Post ta bayyana cewa: Cikakken gurgunta tashar jiragen ruwa na Eilat da ke haramtacciyar kasar Isra’ila ya bayyana tasirin ikon Yemen
Jaridar Washington Post ta Amurka ta tabbatar da cewa rufe tashar jiragen ruwa ta Umm al-Rashrash na karshe ya nuna tasiri da karfin hare-haren Yemen ke da shi.
A cikin wani babban rahoto da aka buga a ranar Litinin, jaridar ta lura cewa, bayanan da jami’an mamayar Isra’ila suka yi game da gurguncewar da tashar jiragen ruwa ta yi, sun bayyana a fili “cikakkiyar nasarar da ‘yan Yemen suka yi.”
Jaridar ta yi hasashen cewa: Kasar Yemen za ta iya aiwatar da sauye-sauyen dabarun yaki a yankin, inda ta yi nazari kan wasu ayyukan sojojin ruwan kasar Yemen da suka tilastawa jiragen yakin Amurka gudu daga yankin, tare da sanadin nutsewar jiragen ruwa da dama da suka sabawa umarninsu, lamarin da ya sa sojojin Amurka da na yammacin Turai suka kasa yin komai a kansu.
Jaridar ta lura cewa ayyukan Yemen sun sanya tasirin su tun farkon harin da suka kai ga jirgin ruwan jigilar gwamnatin mamayar Isra’ila a karshen shekara ta 2023, da ya tabbatar da cewa ayyukan sun ragu da kashi 90 cikin 100 cikin kankanin lokaci, kafin tashar ta kai ga barin aiki kwata-kwata.