HausaTv:
2025-05-01@04:13:53 GMT

Nijar, Burkina Faso da Mali sun fice daga kungiyar kasashe renon Faransa

Published: 19th, March 2025 GMT

Kasashen Nijar da Burkina Faso da kuma Mali kowannensu sun sanar da ficewa daga kungiyar kasashe renon faransa ta (OIF).

Nijar ta sanar da ficewa daga kungiyar a ranar Litini, yayin da Mali ta bi sahu a ranar Talata, aa daidai lokacin da ake raya makon kungiyar.

Babban sakataren ma’aikatar harkokin wajen kasar Laouali Labo, a wata wasika da ya aikewa jakadun kasar ya ce: “Gwamnatin Nijar ta yanke shawarar ficewa daga kungiyar ta OIF.

Nijar dai na daga cikin kasashen da suka asassa kungiyar ta OIF, wacce aka kafa a Yamai babban birinin kasar a ranar 20 ga watan Maris na shekarar 1970, kuma tsohon shugaban kasar Dojori Hamani na waccen lokacin na daga cikin jagororin da suka kafa kungiyar.

To saidai dangankata ta yi tsami tsakanin faransa da sojojin dake mulki a kasashen guda uku a baya bayan nan.

Kungiyar ta OIF, “maimakon tallafawa wadannan kasashe wajen cimma manufofin raya al’ummarsu, (…) ta kauce wa hanya inda ta sanya siyasa a cikin lamuranta,” in ji ministocin harkokin wajen kawancen kasashen guda uku na Sahel a wata sanarwar hadin gwiwa da suka fitar a yammacin jiya Talata.

Kungiyar ta OIF, da ta hada kasashe da gwamnatoci 93, manufarta ita ce inganta harshen Faransanci da raya al’adu, don ƙarfafa zaman lafiya, da dimokuradiyya da ‘yancin dan adam, don tallafawa ilimi, horo da bincike, da kuma inganta hadin gwiwar tattalin arziki don samun ci gaba mai dorewa.

Sai nan da watanni shida masu zuwa ne ficewar kasashen za ta tabbata.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: kungiyar ta OIF daga kungiyar

এছাড়াও পড়ুন:

Abubuwan Da Na Gani A Yankin ‘Hero Bay’ Da Ke Cikin Kasar China

kauyuka a China, ana nufin yankunan da suka bunkasa, wadanda suka kasance, sun yi kamance-ceniya da sun anguwanin GRA a Nijeriya da kuma a nahiyar Afirka.

 

A yankin na Hero Bay, an tanadar da tituna inganciyyar wutar lantarki, tsaftatattacen ruwan sha da kuma kafar Inernet

 

Akwai manyan bene masu tsawo a yankin, wadanda tsawonsu ya dara na bene mai hawa biyar, inda kuma aka tanadar wa da yankin, ababen more rayuwa.

 

kananan hukumomi ne, suka gina wadannan matsugunnan, musamman donin a dakile barazanar kwararowa alumma daga kauye, zuwa cikin birane.

 

A gwajin da aka yi na yankunan da su habaka sosai a China, ana buga misali da Hero Bay kan yadda gwamnati ke bai wa alumma kwarin guiwa na su ci gaba da zama a yankunan da suke, musamman ta hayar samar masu tallafin kudi da gidaje.

 

Wannan dabarun, baya ga kara bunkasa fannin aikin noma a kauyukan, sun kuma kara habaka fannin fasaha kimiyya a kauyukan da kuma kara bunkasa tattalin arzikin kasar.

 

Wani mai gudanar da aikin bincike a cibiyar yin bincike a fannin fasaha ta kasar Wang Yongzhong, ya alakanta kauyukan a matsayin guraren da suka yi fice a duniya, da makuntan kasar, suka samar masu da ababen more rayuwa.

 

Samar da hanyoyi na daga cikin ayyukan da gwamnatin China, ke bai wa mahimmanci, musamman domin a samar da damar gudanar da zirga-zirgar gudanar da ayyukan yau da kullum, a cikin sauki.

 

Samar da yankin na Hero Bay, na daga cikin babban misalin mayar da kan gwamnatin kasar, na dakile kwararowar mazauna a karkara, musamman a tsakanin matasa zuwa cikin birane.

 

Wasu biranen sun kasance cike suke da manyan rukunonin gidage, amma wannan sabanin haka ne, a Hero Bay, duba da yadda aka samar da gidaje, ga ‘yan kauyen da ke da ra’ayin zama a cikinsu, wanda kuma za su iya habaka kasuwancinsu da gudanar da aikin noma, tare da kuma samar da makarantu, Asibiti da jami’an tsaro da sauransu.

 

Daura da Hero Bay, akwai masana’antar kera motoci, wadda kuma ke samar da ayyukan yi ga mazauna yankin, ta hanyar goyon bayan ayyuakn shirye-shirye na kananan hukumomi.

 

A cewar Mataimakin Daraktan shirin bayar da horo China, Mista Wu Hao, gwamnatin kasar ta samar da wadannan ababen more rayuwar ne, domin a dakile kwararar mazauna kauyukan zuwa cikin biranen kasar.

 

daya daga cikin mazauna yankin Madam Yang Baozhen, ta tabbatar da wannan maganar ta Mista Wu Hao, inda ta ce, ana karfafawa, musamman matasa guiwa domin su shiga a dama da su, a fannin hada-hadar kasuwancin yankin, wanda hakan ka samar da kauyukan kudaden shiga.

 

Kazalika, mazauna kauyukan da ba su da bukatar shiga fannin noma ko yin aiki a masana’anta, su kan bude gidajen sayar da abinci ko kuma yin wasu kanannan sana’oi.

 

A kauykan, ana kuma bayar da ilimin zamani kyauta, tun daga matakin Firamare zuwa na Sakandare.

 

Bisa tsarin mallakar filaye a kauyukan ba za ka sayi fili ko kuma ka sayar da shi ba, amma za ka iya bayar da jinginarsa, har zuwa tsawon shekaru 50 zuwa 70, wanda daga baya, za ka sabunta jinginar.

 

A cewar wani mai zagaya wa masu yawon bude ido, “A kasar duk wani fili da ke kasar, mallakar gwamnatin kasar ne, wadda kuma kowanne fili, an tsara abinda za a yi a kansa,”

 

A yayin da ake ci gaba da tattauna wa kan batun bunkasa nahiyar Afrika ciki har da Nijeriya, akwai bukatar a rungumi irin wannan tsarin na China, duba da cewa, abu ne, da kwalliya za ta biya kudin Sabulu.

 

Kazalika, ta hanyarin yin hadaka da tsarin samar da hanyoyi na BRI na China hakan zai samar da wata ingantacciyar hadaka ga kasashe masu tasowa da kuma ga cibiyar bunkasa kasuwanci ta kasa da kasa ta AIBO da ke a karkashin ikon ma’aikatar bunkasa kasuwanci ta China, musamman wajen bayar da horo kan dabarun zamani na bunkasa kasuwanci.

 

Hakazalika, ta hanyar rungumar wannan tsarin China, Afirka za ta iya magance yawan kwararowar mazauna karkara, zuwa cikin birane, wanda hakan zai kuma taimaka wa kasashen da ke a Afrika, wajen kara bunkasa tattalin arzikinsu da samar wa da ‘yan Afrika, alkibla mai dorewa.

 

 

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Iran ta sha alwashin ci gaba da aiwatar da manufofinta na raya dangantakarta da Nijar
  • Kar A Mika Wuya Ga “Damisar Takarda”
  • Tarayyar Afirka ta dage takunkumin da ta kakabawa Gabon
  • Iran Da Iraki Sun Ce An Kammala Shimfida Layin Dogo Daga Shalamcheh Zuwa Basra
  • Katafaren Jirgin Daukar Jiragen Yaki Na Kasar Amurka Harry Truman Zai Fice Daga Tekun Maliya
  • Xi Jinping Ya Ziyarci Sabon Bankin Raya Kasashen BRICS
  • Abubuwan Da Na Gani A Yankin ‘Hero Bay’ Da Ke Cikin Kasar China
  • Har Yanzun Ana Zaman Dar-Dar A Burkina Faso Bayan Kokarin Juyin Mulkin Da Bai SamiNasara Ba
  • Shugaban Kungiyar Hizbullah Ya Abbaci Abubuwa 3 Wadanda Yakamata Kasar Ta Maida Hankali A Kansu
  • Shugaban Kasar Yana Maraba Da Masu Zuba Hannun Jari A Kasarsa Daga Kasashen Waje