Nijar, Burkina Faso da Mali sun fice daga kungiyar kasashe renon Faransa
Published: 19th, March 2025 GMT
Kasashen Nijar da Burkina Faso da kuma Mali kowannensu sun sanar da ficewa daga kungiyar kasashe renon faransa ta (OIF).
Nijar ta sanar da ficewa daga kungiyar a ranar Litini, yayin da Mali ta bi sahu a ranar Talata, aa daidai lokacin da ake raya makon kungiyar.
Babban sakataren ma’aikatar harkokin wajen kasar Laouali Labo, a wata wasika da ya aikewa jakadun kasar ya ce: “Gwamnatin Nijar ta yanke shawarar ficewa daga kungiyar ta OIF.
Nijar dai na daga cikin kasashen da suka asassa kungiyar ta OIF, wacce aka kafa a Yamai babban birinin kasar a ranar 20 ga watan Maris na shekarar 1970, kuma tsohon shugaban kasar Dojori Hamani na waccen lokacin na daga cikin jagororin da suka kafa kungiyar.
To saidai dangankata ta yi tsami tsakanin faransa da sojojin dake mulki a kasashen guda uku a baya bayan nan.
Kungiyar ta OIF, “maimakon tallafawa wadannan kasashe wajen cimma manufofin raya al’ummarsu, (…) ta kauce wa hanya inda ta sanya siyasa a cikin lamuranta,” in ji ministocin harkokin wajen kawancen kasashen guda uku na Sahel a wata sanarwar hadin gwiwa da suka fitar a yammacin jiya Talata.
Kungiyar ta OIF, da ta hada kasashe da gwamnatoci 93, manufarta ita ce inganta harshen Faransanci da raya al’adu, don ƙarfafa zaman lafiya, da dimokuradiyya da ‘yancin dan adam, don tallafawa ilimi, horo da bincike, da kuma inganta hadin gwiwar tattalin arziki don samun ci gaba mai dorewa.
Sai nan da watanni shida masu zuwa ne ficewar kasashen za ta tabbata.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: kungiyar ta OIF daga kungiyar
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamnatin Jigawa Ta Raba Tallafin Kayayyakin Sana’o’i A Karamar Hukumar Gagarawa
Gwamnatin Jihar Jigawa za ta kafa ƙananan masana’antu a karamar hukumar Gagarawa.
Gwamna Umar Namadi ya bayyana hakan yayin kaddamar da rabon kayayyakin bunkasa tattalin arziki ga wasu daga cikin al’ummar Gagarawa.
Malam Umar Namadi ya yi bayanin cewar, masana’antun za su hada da na sarrafa shinkafa da sauransu.
Yana mai cewar hakan zai taimaka wajen samar da ayyukan yi ga matasa marasa aikin yi a yankin.
Kazalika, Gwamnan yace gwamnatin jihar za ta ware kudi a kasafin kudin shekarar badi don gina hanyar mota daga Medu zuwa Dandidi zuwa Madaka, domin saukaka sufuri ga al’ummar yankin.
Baya ga kaddamar da tallafin, Malam Umar Namadi, ya bude wasu ayyukan ci gaba ciki har da makarantar Tahfizul Qur’ani ta Hajiya Maryam Namadi da babban dakin taro da kuma gyaran babban masallacin Gagarawa.
A halin yanzu, mutane sama da 2,000 ne aka zakulo domin cin gajiyar kayayyakin tallafin.
Kayayyakin sun hada da tallafin naira miliyan 70 da babura da injinan dinki da na niƙa.
Sai kuma kekuna ga ɗalibai da injinan yin taliya da kuma shigar da makiyaya sama da 1,000 cikin makarantun ‘yayan fulani makiyaya.
Taron ya samu halartar shugaban majalisar dokokin jihar da wasu daga cikin ‘yan majalisar zartarwar jihar, da dai sauransu.
Usman Mohammed Zaria