HausaTv:
2025-12-12@10:36:52 GMT

Nijar, Burkina Faso da Mali sun fice daga kungiyar kasashe renon Faransa

Published: 19th, March 2025 GMT

Kasashen Nijar da Burkina Faso da kuma Mali kowannensu sun sanar da ficewa daga kungiyar kasashe renon faransa ta (OIF).

Nijar ta sanar da ficewa daga kungiyar a ranar Litini, yayin da Mali ta bi sahu a ranar Talata, aa daidai lokacin da ake raya makon kungiyar.

Babban sakataren ma’aikatar harkokin wajen kasar Laouali Labo, a wata wasika da ya aikewa jakadun kasar ya ce: “Gwamnatin Nijar ta yanke shawarar ficewa daga kungiyar ta OIF.

Nijar dai na daga cikin kasashen da suka asassa kungiyar ta OIF, wacce aka kafa a Yamai babban birinin kasar a ranar 20 ga watan Maris na shekarar 1970, kuma tsohon shugaban kasar Dojori Hamani na waccen lokacin na daga cikin jagororin da suka kafa kungiyar.

To saidai dangankata ta yi tsami tsakanin faransa da sojojin dake mulki a kasashen guda uku a baya bayan nan.

Kungiyar ta OIF, “maimakon tallafawa wadannan kasashe wajen cimma manufofin raya al’ummarsu, (…) ta kauce wa hanya inda ta sanya siyasa a cikin lamuranta,” in ji ministocin harkokin wajen kawancen kasashen guda uku na Sahel a wata sanarwar hadin gwiwa da suka fitar a yammacin jiya Talata.

Kungiyar ta OIF, da ta hada kasashe da gwamnatoci 93, manufarta ita ce inganta harshen Faransanci da raya al’adu, don ƙarfafa zaman lafiya, da dimokuradiyya da ‘yancin dan adam, don tallafawa ilimi, horo da bincike, da kuma inganta hadin gwiwar tattalin arziki don samun ci gaba mai dorewa.

Sai nan da watanni shida masu zuwa ne ficewar kasashen za ta tabbata.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: kungiyar ta OIF daga kungiyar

এছাড়াও পড়ুন:

Bankin Duniya Ya Daga Hasashen Ci Gaban Tattalin Arzikin Sin Na 2025 Da Maki Kaso 0.4

Bankin duniya ya fitar da sabon hasashensa kan tattalin arzikin Sin a bana a jiya Alhamis, inda ya daga na kasar Sin da maki kaso 0.4.

Bankin ya ce manufofin kudi masu inganci sun sun taimaka wa harkokin sayayya da na zuba jari. Haka kuma, bukatu daga kasashe masu tasowa sun ingiza fitar da kayayyaki daga kasar.

Daraktar sashen kula da harkokin Sin da Mongolia da Korea na bankin duniya, Mara Warwick, ta ce ci gaban kasar Sin a shekaru masu zuwa zai kara dogara kan sayayya a cikin gida. Kuma baya ga dabarun kashe kudi na gajeren lokaci, inganta gyare-gyaren tsarin kyautatawa al’umma da samar da kyakkyawan muhallin kasuwanci, ka iya taimakawa kara kwarin gwiwa da shimfida tubalin juriya da ci gaba mai dorewa. (FMM)

ADVERTISEMENT ShareTweetSendShare MASU ALAKA Daga Birnin Sin Kamfanin CRCC Ya Kammala Shimfida Hanyar Jirgin Kasa A Gadar Layin Dogo Mafi Tsawo A Afrika Dake Algeria December 11, 2025 Daga Birnin Sin Yadda Bunkasar Tattalin Arzikin Kasar Sin Ke Samar Da Karin Damammaki Ga Kasashe Masu Tasowa December 11, 2025 Daga Birnin Sin Kamfanonin Sin Sun Kera Tare Da Sayar Da Motoci Sama Da Miliyan 31 Tsakanin Janairu Zuwa Nuwamban Bana December 11, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Yadda Bunkasar Tattalin Arzikin Kasar Sin Ke Samar Da Karin Damammaki Ga Kasashe Masu Tasowa
  • Bankin Duniya Ya Daga Hasashen Ci Gaban Tattalin Arzikin Sin Na 2025 Da Maki Kaso 0.4
  • Shugabannin Sin Sun Yi Taron Koli Na Tattauna Aikin Raya Tattalin Arziki Don Tsara Abubuwan Da Za A Aiwatar A 2026
  • Kyaftin Traoré : Yau Burkina ta zama misali a duniya
  • ‘Yan Ta’adda Sun Kai Hare-Hare Kan Sojojin Pakistan Sun Kuma Kashe 6 Daga Cikinsu
  • Saurayi ya kashe budurwarsa sannan ya soya qwaqwalwarta 
  • Ganawa A Tsakanin Mataimakan Ministocin Waje Na Kasashen Saudiyya, China Da Minista Arakci Na Iran
  • Faransa ta tabbatar da sa hannunta wajen dakile juyin mulki a Benin
  • Trump Ya Yi Gefe Da Kasashen Turai Dangane Da Tattaunawa Kan Rikicin Ukraine
  • Najeriya: Jirgin Sojojin Kasar Yana Kan Hanyarsa Ta Zuwa Portugal, Amma Ta Sauka A Burkina Faso