Aminiya:
2025-07-09@06:24:47 GMT

Dangote ya karya farashin fetur karo na biyu a mako guda

Published: 17th, April 2025 GMT

Mako guda bayan rage farashin fetur da Naira 45, matatar mai ta Dangote ta sake karya farashin man ga ‘yan sari da ragin Naira 30 duk lita.

Aminiya ta rawaito cewa matatar na sayar da man ne a ranar Laraba akan ₦835, saɓanin makon da ya gabata da ta sayar da shi akan ₦865 bayan rage farashin daga ₦880 da ta sayar a makon da ya gabata.

Majalisa ta gayyaci Kantoman Ribas, Ibok-Ete Ibas An naɗa mace ta farko mai magana da yawun rundunar sojin Nijeriya

Hakan dai na nufin a cikin makonni shida, Dangoten ya rage farashin fetur ɗin sau uku.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: matatar man Dangote

এছাড়াও পড়ুন:

 Nijar: An Kashe Sojoji 10 A Wasu Hare-hare Biyu Na ‘Yan Ta’adda

Raundunar sojan jamhuriyar Nijar sun sanar da cewa, an kashe  sojoji 10 da kuma jikkata wasu 15 a wasu hare-hare biyu da masu dauke da makamai su ka kai a yankin Telaberi da kudu masu yammacin kasar.

Yankin Telaberi dai yana cikin yankunan da masu dauke da makamai su ka fara kai hare-hare saboda kusancinta da iyakokin kasashen Mali da Burkina Faso.

Bayanin na sojojin kasar ta Jamhuriyar Nijar wanda kafafen watsa labarun kasar su ka watsa ya kunshi cewa; Daruruwan masu dauke da bindiga sun kai hare-hare a kan sansanonin soja biyu da suke a yankin Telaberi da hakan ya yi sanadiyyar kashe sojoji 10 da kuma jikkatar wasu 15.”

Sai dai kuma sanarwar ta ce, sojojin sun yi nasarar kashe 41 daga cikin maharan.

A watan da ya shude ma dai kasar ta Nijar ta fuskanci hare-hare masu muni. Daga ciki da akwai wani kwanton bauna da aka yi wa sojoji da garin Agadas wanda ya ci rayukan 11 daga cikinsu. Haka nan kuma an kashe fararen hula 40 a wasu jerin hare-hare a fadin kasar a shekarar da ta gabata a kusa iya da Burkina Faso.

Tun daga 2015 ne dai sojojin kasar ta Nijar suke fuskantar hare-haren ta’addanci a cikin yankuna mabanbanta, musamman a yankunan da suke kan iyaka.

Yankin tafikin Chadi dai daya daga yankuann da suke da iyaka da Najeriya, Kamaru da Chadi, wanda yake da maboyar ‘yan kungiyoyin Bokoharam da kuam ISIS.

Kasashe uku da yammacin Afirka da su ka  kafa tsarin Kwanfaderaliyya da su ne; Mali, Nijar da Burkina Faso, suna Shirin kafa rundunar soja ta hadaka mai mayaka 5000 domin fuskantar ‘yan ta’adda da tsararrun laifuka. Sanarwar hakan dai ta fito ne daga bakin ministan tsaron Nijar Salihu Mudi.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Iran Za Ta Yi Nazarin Sabuwar Gayyatar Da Amurka Ta Yi Mata Na  Sabuwar Tattaunawa
  • ASUU Ta Tsunduma Yajin Aiki A Faɗin Nijeriya
  • Asibiti Mai Zaman Kansa A Kano Zai Fara Aikin Manyan Tiyatu Tare Da Rage Kuɗi Kaso 50%
  • Asibiti Mai Zaman Kansa A Kano Zai Fara Manya Manyan Tiyatu Tare Da Rage Kuɗi Kaso 50%
  • Hizbullah Ta Yi Allawadai Da Harin HKI A Kasar Yemen
  • Hukumar Kula da Muhalli ta Jihar Jigawa ta Kwace Gurbatattun Kayayyaki na Miliyoyin Naira
  • Kasar Rasha Tana Ci Gaba Da Karya Kadarin Kasashen Turai A Yakin Da Suke Yi A Ukraine  
  • Xi Ya Ba Da Amsar Wasikar Matasan Amurka ’Yan Wasan Kwallon Pickle Bisa Ziyartar Sin
  •  Nijar: An Kashe Sojoji 10 A Wasu Hare-hare Biyu Na ‘Yan Ta’adda
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Da Tawagarsa Sun Isa Kasar Brazil Don Halartar Taron BRICS Karo Na 17