Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp.

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Gwamnatin Tarayya Wutar Lantarki

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnati ta fara duba yara marasa galihu kyauta a asibitin Aminu Kano

Hukumar Kula da Inshorar Lafiya ta Kasa (NHIA) a ranar Laraba ta kaddamar da shirin bayar da kulawar lafiyar gaggawa kyauta ga yara a Asibitin Koyarwa na Aminu Kano (AKTH), Kano.

Shirin, a cewar Darakta a hukumar, Dr. Salahudeen Sikiru, wani bangare ne na fadada shirin lafiyar iyaye da NHIA ke aiwatarwa zuwa ga yara masu rauni da masu bukata ta musamman.

Tun Tinubu yana Gwamna ba abin da ya fi shahara da shi kamar tara haraji – Adebayo Ana zargin mace da kashe ’yar uwarta a kan N800 din barkono

Ya ce an fara shirin fiye da shekara ɗaya da ta gabata da nufin rage mace-macen jarirai ’yan kasa da shekaru biyar.

“Mun fara wannan shiri fiye da shekara guda da ta gabata da nufin rage mace-macen jarirai. Yanzu mun zo nan don fara na ɓangaren jarirai. Mu za mu biya kudin kulawar gaggawar yaran sannan mu tabbatar an kula da su har su samu ingantacciyar lafiya,” in ji Dr. Sikiru.

Ya kuma ce a karkashin shirin, yara da ke fama da matsalolin gaggawa kamar rashin numfashi, amosanin jini, cutar shawara da yaran da aka haifa bakwaini da ma cututtukan da ke buƙatar tiyata za su samu kulawa kyauta.

Ya ce asibitoci za su fara ba da kulawa da zarar an kawo yara, sannan su tura adadin kuɗin kula da yaran a kowanne mako ga NHIA don a biya su.

Daraktan ya kara da cewa duk yaran da ya sami kulawar gaggawar kuma, za a saka shi cikin shirin inshorar lafiya na NHIS, inda hukumar za ta ci gaba da biyan kudin inshorar don tabbatar da samun kulawar lafiya mai inganci.

“Kafin yaro ya ci gajiyar shirin, dole ne a tantance shi a a tabbatar yana da rauni da kuma ba zai iya biyan kuɗin asibiti ba. Haka nan dole ne yaro ya mallaki Lambar Shaida ta Kasa (NIN) don tabbatar da gaskiya da shigar da su cikin tsarin,” in ji shi.

Dr. Sikiru ya kuma ce, “Shiri ne kula da marasa lafiya cikin gaggawan. Da zarar sun zo, za a duba su. Asibitin sai ya turo mana jimillar adadin kudin, mu kuma mu biya.”

Ya ce wannan shiri wani bangare ne na kudurin gwamnatin tarayya na rage mace-macen jarirai da tabbatar da cewa babu yaron da ya rasa kulawar asibiti saboda rashin kudi.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnati ta fara duba yara marasa galihu kyauta a asibitin Aminu Kano
  • Jihar Jigawa Ta Amince Da Karin Kasafin Kuɗi Na Naira Biliyan 75 Na Shekarar 2025
  • Sojoji Sun Harbe Wasu ‘Yan Ta’adda 2 A Taraba
  • Wata Ta Kashe ’Yar Uwarta Kan Bashin Naira 800 A Ondo
  • NDLEA ta kama ɗan Indiya da ƙwaya ta Naira biliyan 3 a Legas
  • ’Yan sanda sun sasanta rikicin asibitin AKTH da KEDCO
  • KEDCO ya ƙaryata asibitin AKTH kan mutuwar majinyata saboda ɗauke wuta
  • Likitoci Sun Tsunduma Yajin Aiki Na Dindindin A Abuja
  • KEDCO Ta Mayar Da Wutar Lantarki A Asibitin Aminu Kano
  • Sarki Sanusi II ya koka kan yawan cin bashin Najeriya