Rundunar ‘yansandan babban birnin tarayya Abuja ta tabbatar da mutuwar mutane shida a fashewar tankar man fetur da ya afku a yankin Karu da ke Abuja a daren Laraba. Rundunar ta kuma ce motoci 14 ne suka kone a mummunan hatsarin. Jami’an Tsaro Sun Ceto Mutane 84, Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 3 A Katsina Cikar NUJ Shekaru 70: ‘Yan Jarida Abokan Hulɗa Ne Wajen Aza Kyakkyawar Makoma – Gwamnan Gombe Kakakin rundunar ‘yansandan, SP Josephine Adeh, wanda ya bayyana hakan a ranar Alhamis, ya bayyana cewa, rundunar ta yi matukar jimamin hatsarin motar da ya afku a ranar 19 ga Maris, 2025, da misalin karfe 6:58 na yamma kafin gadar Nyanya.

Ta kuma ce, ofishin hukumar na Karu ya samu kiran gaggawa na faruwar lamarin, inda wata motar tirela ta Dangote, dauke da siminti da ta nufo gadar Nyanya daga AYA ta afka cikin motocin da ke tsaye cikin cunkoso.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Tinubu ya ƙirƙiri sabon harajin da zai iya ƙara N100 a kan kowacce litar man fetur

Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya amince da ƙaddamar da sabon harajin shigo da kaya na kashi 15 cikin 100 kan dukkan man fetur da dizil din da aka shigo da shi zuwa Najeriya.

An tsara wannan mataki ne domin kare matatun man cikin gida da kuma daidaita kasuwar man fetur a ƙasa, sai dai ana sa ran hakan zai iya haifar da ƙarin farashin man a gidajen mai.

Majalisa ta amince Tinubu ya karɓo rancen dala biliyan 2.35 Gwamnati ta bai wa ASUU N2.3bn domin biyan bashin albashin malamai

A cikin wata wasiƙa da aka rubuta a ranar 21 ga Oktoba, 2025, kuma aka bayyana a hukumance a ranar 30 ga Oktoba, 2025, zuwa Hukumar Tara Haraji ta Ƙasa (FIRS) da Hukumar Kula da Man Fetur ta Ƙasa (NMDPRA), inda Shugaba Tinubu ya bayar da umarnin aiwatar da harajin nan take a matsayin wani ɓangare na tsarin harajin shigo da kaya da gwamnati ta bayyana a matsayin “tsarin da ke daidaita da kasuwa.”

Wasiƙar, wacce Sakataren Shugaban Ƙasa, Damilotun Aderemi, ya sanya wa hannu, ta nuna amincewar Shugaban bayan da Shugaban Hukumar FIRS, Zacch Adedeji, ya gabatar da shawararsa.

Shawarar ta nemi a fara amfani da harajin kashi 15 cikin 100 kan kuɗin kaya, inshora da jigilar man fetur da dizal da ake shigo da su, domin daidaita farashin shigo da kaya da yanayin kasuwar cikin gida.

A cikin takardar da ya aike wa Shugaban Ƙasa, Adedeji ya ce wannan mataki na daga cikin gyare-gyaren da ake ci gaba da aiwatarwa domin ƙarfafa matatun cikin gida, tabbatar da daidaiton farashi, da kuma ƙarfafa tattalin arzikin man fetur da ke dogaro da naira.

“Babban burin wannan tsari shi ne aiwatar da cinikayyar danyen mai da naira, ƙarfafa matatun cikin gida, da kuma tabbatar da wadataccen man fetur mai arha a fadin Najeriya,” in ji Adedeji.

Shugaban FIRS ya kuma yi gargaɗin cewa rashin daidaito tsakanin farashin kayayyakin da ake tacewa a cikin gida da farashin da ake amfani da shi wajen ƙayyade farashin gidajen mai na shigo da kaya ya janyo rashin tabbas a kasuwa.

A cewar hasashen da ke cikin wasiƙar, harajin kashi 15 cikin 100 zai iya ƙara farashin saukar man fetur da kimanin Naira 99.72 a kowace lita.

Wannan sabon mataki na zuwa ne a daidai lokacin da Najeriya ke ƙara ƙoƙari don rage dogaro da shigo da man fetur da dangoginsa daga ƙasashen waje, tare da ƙarfafa tacewa a cikin gida.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamna Namadi Ya Bada Motocin Aiki Goma Ga Rundunar ‘Yan Sanda
  • Gwamnatin Jigawa Ta Bada Motocin Aiki Goma Ga Rundunar ‘Yan Sanda
  • Barcelona ta shiga zarwacin Victor Osimhen
  • Gwamnatin Jigawa Za Ta Gina Gidaje 52 A Babban Birnin Jihar
  • Rundunar Sojin Nijeriya Ta Shirya Wa Janar Musa Faretin Gama Aiki
  • An raba wa iyalan jami’an ’yan sandan da suka rasu a bakin aiki a Borno N63.4m
  • ‘Yansanda Sun Ceto Mutum Ɗaya, Sun Kama Mace Da Zargin Garkuwa Da Mutane A Dajin Kwara 
  • Gaza: hare-haren Isra’ila sun kashe mutane 100 Cikin Kwanaki Biyu
  • Ci Gaba Da Killace Gaza Bayan Tsagaita Bude Wuta Ya Janyo Mutuwar Mutane 1000 A Yankin
  • Tinubu ya ƙirƙiri sabon harajin da zai iya ƙara N100 a kan kowacce litar man fetur