Masu ƙwacen waya sun kashe ma’aikaciyar ofishin jakadancin Ghana a Abuja
Published: 9th, July 2025 GMT
Masu kwacen da aka fi san da ’yan ‘One Chance’, sun kashe Freda Arnong, wata ma’aikaciya a ofishin jakadancin kasar Ghana da ke babban birnin tarayya Abuja.
Bayanai sun nuna matar, wacce daga bisani ta mutu a asibitin kasa da ke Abuja, ta hau motar da ake zargin ta masu kwacen ce a bisa rashin sani.
Wata majiya daga jami’an tsaro ta shaida wa wakilinmu cewa Freda ta hau motar ta tasi ne daga marabar otal din Transcorp a makon da ya gabata.
Majiyar ta ce a lokacin da matar ta shiga, akwai wasu mutum hudu da har yanzu ba a kai ga tantance su ba.
Majiyar ta ce daga nan ne sai direban motar ya canza hanya ya bi titin zuwa Lugbe-filin jirgin sama, inda suka kashe ta, kafin daga bisani su jefar da gawarta yayin da motar ke ci gaba da tafiya.
Daga nan ne aka dauke ta aka garzaya da ita asibitin, inda daga bisani ta rasu a ranar Talata.
Ita ma wata majiya daga asibitin da ta ce ba ta da hurumin yin magana da ’yan jarida ta tabbatar da mutuwar matar.
“Ta mutu wajen misalin karfe 1:52 na ranar Talata, kuma yanzu haka gawarta tana dakin adana gawarwaki na asibitin domin yin binciken musabbabin mutuwar tata,” in ji majiyar.
Sai dai da wakilinmu ya tuntubi Kakakin rundunar ’yan sanda ta yankin Abuja, SP Adeh Josephine, amma ba ta amsa kira ko sakon kar-ta-kwanan da ya tura mata ba, har zuwa lokacin hada wannan rahoton.
উৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
Falasdinawa Kimani 635 Amurka da HKI Suka Kashe A Cibiyoyin Karban Abinci A Gaza
Kamfanin dillancin Labaran Assosciated Press ta bayyana cewa ana ci gaba da sukar Amurka da HKI kan cibiyoyin kisa da suka kafa a Gaza da sunan tallafawa Falasdinawa da abinci.
Labarin ya bayyana cewa ya zuwa yanzu Amurka da HKI sun kashe Falasdinawa kimani 635 wajen karban abinda suka kira taimakon abinci bayan sun sa su yunwa mai tsanani wanda zai sa su dole su fito su ne mi aminda zasu a sa a cikinsu. Amma idan sun so sojojin HKI su kashesu.
Kamfanin dillancin labaran Associeated Press ya nakalto kamfanoni Amurka guda biyu wadanda sun ce sun shigar da kara Amurka da kuma HKI kan yadda suke gudanar da cibiyoyin rabon abinda suka kira abinci a gaza, wanda bai dace ba.
Kamfanin sun bayyana cewa jami’an tsaron da Amurka da HKI suka kawo a cibiyoyin, da alamun an basu izinin su kashe falasdinawa da suka fito karban abinda suka kira a gaji. Su kuma yi amfani da yuwan da suka sa su don tilasta ,masu fita da kuma kashe su daga karshe.
Wani kamfanin rabon abincin agajin ya ce sojojin na barin wuta kan Falasdinawa hatta kan wadansa suke layin karban agajin.