Aminiya:
2025-09-17@23:26:40 GMT

Masu ƙwacen waya sun kashe ma’aikaciyar ofishin jakadancin Ghana a Abuja

Published: 9th, July 2025 GMT

Masu kwacen da aka fi san da ’yan ‘One Chance’, sun kashe Freda Arnong, wata ma’aikaciya a ofishin jakadancin kasar Ghana da ke babban birnin tarayya Abuja.

Bayanai sun nuna matar, wacce daga bisani ta mutu a asibitin kasa da ke Abuja, ta hau motar da ake zargin ta masu kwacen ce a bisa rashin sani.

Wata majiya daga jami’an tsaro ta shaida wa wakilinmu cewa Freda ta hau motar ta tasi ne daga marabar otal din Transcorp a makon da ya gabata.

Kaso 90 na ’yan bindigar da suka addabi Katsina ’yan asalin jihar ne – Radda ‘Abin da zai sa APC ba za ta taɓa mantawa da Ganduje ba’

Majiyar ta ce a lokacin da matar ta shiga, akwai wasu mutum hudu da har yanzu ba a kai ga tantance su ba.

Majiyar ta ce daga nan ne sai direban motar ya canza hanya ya bi titin zuwa Lugbe-filin jirgin sama, inda suka kashe ta, kafin daga bisani su jefar da gawarta yayin da motar ke ci gaba da tafiya.

Daga nan ne aka dauke ta aka garzaya da ita asibitin, inda daga bisani ta rasu a ranar Talata.

Ita ma wata majiya daga asibitin da ta ce ba ta da hurumin yin magana da ’yan jarida ta tabbatar da mutuwar matar.

“Ta mutu wajen misalin karfe 1:52 na ranar Talata, kuma yanzu haka gawarta tana dakin adana gawarwaki na asibitin domin yin binciken musabbabin mutuwar tata,” in ji majiyar.

Sai dai da wakilinmu ya tuntubi Kakakin rundunar ’yan sanda ta yankin Abuja, SP Adeh Josephine, amma ba ta amsa kira ko sakon kar-ta-kwanan da ya tura mata ba, har zuwa lokacin hada wannan rahoton.

উৎস: Aminiya

এছাড়াও পড়ুন:

Sin Da Ghana Na Fadada Hadin Gwiwa A Bangaren Ciniki Da Zuba Jari

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Lakurawa Sun Hallaka Jami’in Kwastam A Jihar Kebbi
  • Sin Da Ghana Na Fadada Hadin Gwiwa A Bangaren Ciniki Da Zuba Jari
  • Sojoji sun harbe mayaƙan ISWAP 8 a Borno
  • ’Yan ‘Mafiya’ na ƙoƙarin kashe matatar man fetur da na gina —Ɗangote
  • Jonathan Zai Jagoranci Taron Tattaunawa Kan Dimokuraɗiyya A Ghana
  • Taron Doha: Daga matakin Allawadai zuwa matakan kalubalantar laifukan Isra’ila
  • Majalisar Dattawa Ce Kawai Za Ta Iya Dawo Da Sanata Natasha – Magatakardar Majalisa
  • Burkina Faso: Masu Ikirarin Jihadi Sun Kashe Fararen Hula 50 A Cikin Watanni Hudu
  • Mummunan Hatsarin Mota Ya Kashe Fasinjoji 17 A Zamfara
  • Mutuwar majinyata: Asibitin Aminu Kano na roƙon KEDCO ya dawo da wutar lantarki