Aminiya:
2025-11-02@12:30:12 GMT

Masu ƙwacen waya sun kashe ma’aikaciyar ofishin jakadancin Ghana a Abuja

Published: 9th, July 2025 GMT

Masu kwacen da aka fi san da ’yan ‘One Chance’, sun kashe Freda Arnong, wata ma’aikaciya a ofishin jakadancin kasar Ghana da ke babban birnin tarayya Abuja.

Bayanai sun nuna matar, wacce daga bisani ta mutu a asibitin kasa da ke Abuja, ta hau motar da ake zargin ta masu kwacen ce a bisa rashin sani.

Wata majiya daga jami’an tsaro ta shaida wa wakilinmu cewa Freda ta hau motar ta tasi ne daga marabar otal din Transcorp a makon da ya gabata.

Kaso 90 na ’yan bindigar da suka addabi Katsina ’yan asalin jihar ne – Radda ‘Abin da zai sa APC ba za ta taɓa mantawa da Ganduje ba’

Majiyar ta ce a lokacin da matar ta shiga, akwai wasu mutum hudu da har yanzu ba a kai ga tantance su ba.

Majiyar ta ce daga nan ne sai direban motar ya canza hanya ya bi titin zuwa Lugbe-filin jirgin sama, inda suka kashe ta, kafin daga bisani su jefar da gawarta yayin da motar ke ci gaba da tafiya.

Daga nan ne aka dauke ta aka garzaya da ita asibitin, inda daga bisani ta rasu a ranar Talata.

Ita ma wata majiya daga asibitin da ta ce ba ta da hurumin yin magana da ’yan jarida ta tabbatar da mutuwar matar.

“Ta mutu wajen misalin karfe 1:52 na ranar Talata, kuma yanzu haka gawarta tana dakin adana gawarwaki na asibitin domin yin binciken musabbabin mutuwar tata,” in ji majiyar.

Sai dai da wakilinmu ya tuntubi Kakakin rundunar ’yan sanda ta yankin Abuja, SP Adeh Josephine, amma ba ta amsa kira ko sakon kar-ta-kwanan da ya tura mata ba, har zuwa lokacin hada wannan rahoton.

উৎস: Aminiya

এছাড়াও পড়ুন:

Dalibin Jami’ar Jos Ya Kashe Abokinsa Ya Binne Gawar A Rami

A wani bidiyo daban da PUNCH Metro ta gani a Facebook, wanda Mc Pee ya wallafa, wani mutum da ake zargin dalibi ne na jami’ar ya bayyana abin da ya faru.

A cewarsa, marigayin ya roki a bar shi ya rayu kafin daga bisani wanda ake zargin ya kashe shi.

Ya ce: “Nanpon ya riga ya yanke Peter a kumatunsa yayin da yake rokon a bar shi. Lokacin da muka shiga tsakani muka ce ya daina, sai ya yi barazanar yanka duk wanda ya kusanto shi.

“Da Peter ya ga ba ya sauraron rokonsa, sai ya rungume shi yana rokonsa da kuka.

“Mun fita neman taimako amma babu wanda ya amsa mana. Da Peter ya yi kokarin tserewa sai ya fadi, Nanpon ya kamo shi ya ci gaba da saransa da adda.”

Wani kwararren masanin tsaro da yaki da ta’addanci ya wallafa a dandalin D a ranar Lahadi cewa jami’an rundunar ‘yan sandan Jihar Filato sun kama wanda ake zargin.

Ya kuma ambaci majiyoyi da suka tabbatar da faruwar lamarin ta hanyar rahoton da aka samu daga Babban Jami’in Tsaro na jami’ar.

Ya rubuta cewa, “Rundunar ‘Yansanda ta Filato ta kama wani dalibi mai shekaru 23 na Jami’ar Jos bisa zargin kashe abokinsa sannan ya binne shi a rami mara zurfi a cikin dakinsa da ke kauyen Rusau a Karamar Hukumar Jos ta Arewa.

“Majiyoyi sun tabbatar da faruwar lamarin a ranar Lahadi a Jos, inda suka danganta da rahoton da aka samu daga Babban Jami’in Tsaron jami’ar.

“A cewar majiyoyin, wanda ake zargin mai suna Dabid Nanpon Timmap, dalibi a matakin shekara ta uku a jami’ar, ya kai wa Peter Mata Mafurai, mai shekaru 22, hari da adda, ya kashe shi a gidansa.”

Zagazola ya kara da cewa, bayan samun kiran gaggawa da misalin karfe 9:30 na safiya, DPO na sashin Laranto ya jagoranci tawagar ‘yansanda zuwa wurin, inda aka kama wanda ake zargin.

“Majiyoyin sun ce bincike ya nuna cewa wanda ake zargin ya binne mamacin a cikin rami mara zurfi da ya haka a cikin dakinsa. An tono gawar kuma an kai ta dakin ajiye gawarwaki na Asibitin koyarwa na Jami’ar Bingham domin yin binciken gawar (autopsy),” in ji shi.

Ya kara da cewa, an tsare wanda ake zargin yayin da ake ci gaba da bincike domin gano hakikanin dalilin kashe abokin nasa.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 20, Sun Ceto Mutane 17 Da Aka Yi Garkuwa Da Su November 1, 2025 Manyan Labarai Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Martani Kan Iƙirarin Trump Na Kisan Ƙare Dangi Ga Kiristoci November 1, 2025 Manyan Labarai Shugabar Tanzania Samia Suluhu Ta Lashe Zaɓe, Duk Da Rikicin Da Ya Mamaye Ƙasar November 1, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  •  Gaza: Daga Tsagaita Wuta Zuwa Yanzu Fiye Da Mutane 200 Ne Su Ka Yi Shahada
  • Dalibin Jami’ar Jos Ya Kashe Abokinsa Ya Binne Gawar A Rami
  • ‘An Kashe Masu Zanga-zanga Akalla 500 a Tanzania’
  • Waye Zai Lashe Ƙyautar Gwarzon Ɗan Wasan Afrika Na 2025?
  • Israila Ta Kai Hari  Kan Ofishin kungiyar UNICEF Dake Gaza A
  • Ministan Wajen Malawi: Tsarin Ci Gaban Kasar Sin Ya Samar Da Darussa Ga Kasashe Masu Tasowa
  • ’Yan bindiga sun sace fasinjoji a cikin motocin bas a Kogi
  • Kotu ta tsige dan majalisar da ya sauya sheka zuwa APC
  • Ana zargin ɗa da kashe mahaifinsa a Kano saboda hana shi ƙara aure
  • Gobara ta tashi a babban kanti a Abuja