Aminiya:
2025-07-31@00:37:45 GMT

’Yan Boko Haram 7 sun miƙa wuya ga sojojin MNJTF a Borno

Published: 20th, March 2025 GMT

Wasu ‘yan tada ƙayar baya bakwai da ake zargin ’yan Boko Haram ne sun miƙa wuya ga rundunar haɗin gwiwa ta ƙasa da ƙasa (MNJTF) a Damasak da ke Jihar Borno tare da miƘa tarin makamai da kayan aiki.

Kamar yadda Zagàzola Makama ya ambata wannan miƙa wuyan da waɗannan maharan suka yi ga sojojin da ke aiki ƙarƙashin sashe na 3 Monguno, na nuni da nasarar da aka samu wajen yaƙi da ta’addanci a yankin tafkin Chadi.

Dabarun Rabauta Da Kwanaki 10 Na Ƙarshen Ramadan Muhimman ayyuka 8 a goman ƙarshe na Ramadan

‘Yan Boko Haram ɗin da suka miƙa wuya sun haɗa da Malam Baba Ibrahim ɗan shekara 19, Malam Bamai Ali  mai shekara 20, Malam Jundu Ali  mai shekara 19, Malam Abba Ali mai shekara 25, Malam Abubakar Mohammed  mai shekara 20, Tijjani Ali mai shekara 20, da Malam Ali Mommudu mai shekara 25, waɗanda suka miƙa wuya bisa radin kansu ga dakarun haɗin gwiwar MNJTF a ƙauyen Walada da ke Damasak, bayan sun ci gaba da kai farmakin.

“Wannan miƙa wuya wata shaida ce da ke nuna tasirin ayyukan da muke yi a yanzu,” in ji Laftanar Kanar Olaniyi Osoba, babban jami’in yaɗa labarai na soji da ke hedikwatar rundunar MNJTF.

“Waɗannan mutane sun gane rashin amfanin yaƙinsu kuma sun zaɓi hanyar zaman lafiya.”

Maharan dai sun miƙa wuya sun amsa cewa suna da hannu a ayyukan ta’addanci da dama a Arewacin Borno, inda suka nuna gajiyawa da rikicin.

Sun ce a baya suna tsoron za a kashe su idan sun miƘa wuya ga jami’an tsaron, amma a yanzu sai suka ga ba haka lamarin yake ba.

Makaman da suka miƙa ga rundunar tsaron sun haɗa da bututun makamin RPG guda biyu, bama-baman RPG guda huɗu, bindiga ƙirar AK-47, bindiga ƙirar HK 21 ta Jamus.

Har ila yau, sun miƙa dawakai guda biyu, harsasai 30 da harsasai na musamman nau’in 7.62mm, harsashi nau’in 715 na 7.62mm da  wayoyin hannu 12, ƙananan na’urori masu amfani da hasken rana guda shida da wuƙaƙe guda huɗu da  sauransu.

Laftanar Kanar Osoba ya ce, “Yawan adadin makamai da kayan aikin da suka miƙa ya nuna girman ayyukansu.”  “Ba shakka miƙa wuyan nasu zai kawo cikas ga ayyukan ta’addanci a yankin.”

Wadannan tsoffin ‘yan tada ƙayar baya yanzu haka suna bayar da bayanan sirri ga rundunar ta MNJTF, wanda ake sa ran zai  taimaka a ci gaba da gudanar da ayyukanta na yaƙi da ‘yan ta’addan a yankin tafkin Chadi.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Boko Haram mai shekara

এছাড়াও পড়ুন:

’Yansanda Sun Ceto Mutane 28 Da ‘Yan Bindiga Suka Sace A Katsina

An ceto dukkanin mutane 14 ba tare da wani ya ji rauni ba, amma abin baƙin ciki, wani matashi ɗan shekara 27 mai suna Abba daga garin Funtua ya rasa ransa kafin isowar ’yansanda.

A wani lamari da ya faru a ranar 28 ga watan Yuli da misalin ƙarfe 11:27 na dare, an sake kiran ’yansanda daga ƙauyen Zagaizagi, inda aka sanar da su cewa wasu ’yan bindiga sum hari tare da sace wasu mutane ƙauyen.

’Yansanda sun isa wajen suka gwabza da ’yan bindigar, kuma sun samu nasarar ceto wasu mutane 14 da kuma ƙwato shanun da aka sace guda biyu.

Amma, mutane biyu daga cikin mazauna ƙauyen sun rasa rayukansu a harin.

Rundunar ta ce har yanzu tana ci gaba da ƙoƙarin kamo ’yan bindigar da suka tsere.

Kwamishinan ’yansandan, CP Bello Shehu, ya yaba wa jami’ansa bisa jarumtaka da suka nuna.

Ya kuma buƙaci jama’a da su ci gaba da bai wa ’yansanda sahihan bayanai a kan lokaci.

Ya tabbatar da cewa rundunar za ta ci gaba da kare rayuka da dukiyoyin al’umma a faɗin jihar.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gine-gine 8 Sun Ruguje, Makabarta Ta Nutse A Wata Sabuwar Ambaliyar Ruwa A Borno
  • Sojoji sun daƙile hari, sun kashe mayaƙan Boko Haram 9 a Borno
  • ’Yansanda Sun Ceto Mutane 28 Da ‘Yan Bindiga Suka Sace A Katsina
  • Sojojin Yemen Sun Kai Hari Kan Filin Jirgin Saman Lod Da Ke Jaffa Da Makami Mai Linzami
  • Ku Daina Kashe Mutane Ko Ku Miƙa Wuya – Ribadu Ya Gargaɗi ‘Yan Bindiga
  • Gwamna Namadi Ya Naɗa Shugabannin Hukumar Hisbah Ta Jihar Jigawa
  • Sojojin Sin Sun Bi Sahun Shiga Ayyukan Ba Da Agajin Ambaliyar Ruwa
  • Sojojin HKI Sun Ci Gaba Da Kashe Kawunansu
  • Ambaliyar Ruwa: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Ya Ƙaru Zuwa 23 A Jihar Adamawa
  • Harin Sojojin Sama Ya Hallaka Manyan Shugabannin ISWAP A Borno