Aminiya:
2025-05-01@04:02:48 GMT

’Yan Boko Haram 7 sun miƙa wuya ga sojojin MNJTF a Borno

Published: 20th, March 2025 GMT

Wasu ‘yan tada ƙayar baya bakwai da ake zargin ’yan Boko Haram ne sun miƙa wuya ga rundunar haɗin gwiwa ta ƙasa da ƙasa (MNJTF) a Damasak da ke Jihar Borno tare da miƘa tarin makamai da kayan aiki.

Kamar yadda Zagàzola Makama ya ambata wannan miƙa wuyan da waɗannan maharan suka yi ga sojojin da ke aiki ƙarƙashin sashe na 3 Monguno, na nuni da nasarar da aka samu wajen yaƙi da ta’addanci a yankin tafkin Chadi.

Dabarun Rabauta Da Kwanaki 10 Na Ƙarshen Ramadan Muhimman ayyuka 8 a goman ƙarshe na Ramadan

‘Yan Boko Haram ɗin da suka miƙa wuya sun haɗa da Malam Baba Ibrahim ɗan shekara 19, Malam Bamai Ali  mai shekara 20, Malam Jundu Ali  mai shekara 19, Malam Abba Ali mai shekara 25, Malam Abubakar Mohammed  mai shekara 20, Tijjani Ali mai shekara 20, da Malam Ali Mommudu mai shekara 25, waɗanda suka miƙa wuya bisa radin kansu ga dakarun haɗin gwiwar MNJTF a ƙauyen Walada da ke Damasak, bayan sun ci gaba da kai farmakin.

“Wannan miƙa wuya wata shaida ce da ke nuna tasirin ayyukan da muke yi a yanzu,” in ji Laftanar Kanar Olaniyi Osoba, babban jami’in yaɗa labarai na soji da ke hedikwatar rundunar MNJTF.

“Waɗannan mutane sun gane rashin amfanin yaƙinsu kuma sun zaɓi hanyar zaman lafiya.”

Maharan dai sun miƙa wuya sun amsa cewa suna da hannu a ayyukan ta’addanci da dama a Arewacin Borno, inda suka nuna gajiyawa da rikicin.

Sun ce a baya suna tsoron za a kashe su idan sun miƘa wuya ga jami’an tsaron, amma a yanzu sai suka ga ba haka lamarin yake ba.

Makaman da suka miƙa ga rundunar tsaron sun haɗa da bututun makamin RPG guda biyu, bama-baman RPG guda huɗu, bindiga ƙirar AK-47, bindiga ƙirar HK 21 ta Jamus.

Har ila yau, sun miƙa dawakai guda biyu, harsasai 30 da harsasai na musamman nau’in 7.62mm, harsashi nau’in 715 na 7.62mm da  wayoyin hannu 12, ƙananan na’urori masu amfani da hasken rana guda shida da wuƙaƙe guda huɗu da  sauransu.

Laftanar Kanar Osoba ya ce, “Yawan adadin makamai da kayan aikin da suka miƙa ya nuna girman ayyukansu.”  “Ba shakka miƙa wuyan nasu zai kawo cikas ga ayyukan ta’addanci a yankin.”

Wadannan tsoffin ‘yan tada ƙayar baya yanzu haka suna bayar da bayanan sirri ga rundunar ta MNJTF, wanda ake sa ran zai  taimaka a ci gaba da gudanar da ayyukanta na yaƙi da ‘yan ta’addan a yankin tafkin Chadi.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Boko Haram mai shekara

এছাড়াও পড়ুন:

ISWAP ta ɗauki alhakin kashe mutum 26 a Borno

Ƙungiyar ISWAP mai yaƙi da tayar da ƙayar baya a yammacin Afirka, ta ɗauki alhakin harin da ya yi ajalin mutum 26 a Jihar Borno.

Ƙungiyar ta iƙirarin ɗaukar alhakin harin ne a wani saƙo da ta wallafa a shafin Telegram kamar yadda BBC ya ruwaito.

Aminiya ta ruwaito yadda wani abin fashewa da ake zargin bam ne ya kashe aƙalla mutum 26, ciki har da mata da yara a kan hanyar Rann zuwa Gamboru Ngala da ke Jihar Borno.

Lamarin ya faru ne da yammacin ranar Litinin a lokacin da motoci suka tayar da bama-baman da aka ɗana a gefen hanyar, da ya rutsa da maza 16 da mata huɗu da ƙananan yara guda shida.

Ta yi wa saurayinta ƙaryar shekarunta 27 maimakon 47 An dawo da wutar lantarki a Sifaniya da Portugal

Majiyoyi, ciki har da wani babba soja, sun tabbatar wa kamfanin dillancin labarai na Anadolu da harin na baya bayan da safiyar ranar Talata.

Sun bayyana cewa waɗanda lamarin ya rutsa da su suna kan hanyarsu ta tafiya Gamboru Ngala ne daga Rann lokacin da suka isa inda ‘yan ta’addan ISWAP suka ɗana bam ɗin.

Bayanai sun ce baya ga mutum 26 da suka mutu, ƙarin mutum uku sun ji munanan raunuka.

“Mun tura wasu masu ba da agajin gaggawa inda lamarin ya auku domin kwashe mutane tare da tabbatar da tsaron sauran fararen-hula a wurin,” kamar yadda wata majiyar sojin da ba ta yarda a bayyana sunanta ba ta shaida wa Anadolu.

Ali Abass, wani ganau wanda ke tafiya a kan hanyar a lokacin da lamarin ya auku, ya ce sojojin da ‘yan sa-kai sun kai waɗanda suka jikkata wani asibiti.

Ya ƙara da cewa ɗaya daga cikin ‘yan’uwansa na cikin waɗanda lamarin ya rutsa da su.

Harin yana zuwa ne yayin da hare-hare ke ƙara ƙaruwa a yankin Tafkin Chadi, inda ‘yan ta’addan Boko Haram da ISWAP ke ƙara ƙaddamar da hare-haren bama-bamai da kwanton-ɓauna kan motocin fararen-hula da na sojoji.

An ba da rahoton hare-hare irin wannan a ranakun 21 ga watan Maris da 12 ga watan Afrilu. Kawo safiyar ranar Talata dai, jami’an tsaro a Borno ba su fitar da wata sanarwa a hukumance game da lamarin ba.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kar A Mika Wuya Ga “Damisar Takarda”
  • Amurka ta sake laftawa wasu kamfaninin mai na Iran takunkumi
  • Talauci Da Rashin Ilimi Ne Ya Sa Ayyukan Boko Haram Ke Dawowa – Gwamnan Yobe
  • ISWAP ta ɗauki alhakin kashe mutum 26 a Borno
  • An kashe mafarauta 10 a Adamawa
  • Sojojin Mamayar Isra’ila Sun Kutsa Cikin Quneitra Na Kasar Siriya Tare Da Kafa Shingen Bincike
  • Boko Haram ta kashe masu zaman makoki 7 a Chibok
  • Boko Haram Sun Hallaka ‘Yan Zaman Makoki 7, Sun Jikkata Wasu A Borno
  • Bom ɗin Boko Haram ya kashe mutane 26 a Borno
  • Shekara 10 ina sayar da sassan jikin ɗan Adam — Wanda ake zargi