’Yan Boko Haram 7 sun miƙa wuya ga sojojin MNJTF a Borno
Published: 20th, March 2025 GMT
Wasu ‘yan tada ƙayar baya bakwai da ake zargin ’yan Boko Haram ne sun miƙa wuya ga rundunar haɗin gwiwa ta ƙasa da ƙasa (MNJTF) a Damasak da ke Jihar Borno tare da miƘa tarin makamai da kayan aiki.
Kamar yadda Zagàzola Makama ya ambata wannan miƙa wuyan da waɗannan maharan suka yi ga sojojin da ke aiki ƙarƙashin sashe na 3 Monguno, na nuni da nasarar da aka samu wajen yaƙi da ta’addanci a yankin tafkin Chadi.
‘Yan Boko Haram ɗin da suka miƙa wuya sun haɗa da Malam Baba Ibrahim ɗan shekara 19, Malam Bamai Ali mai shekara 20, Malam Jundu Ali mai shekara 19, Malam Abba Ali mai shekara 25, Malam Abubakar Mohammed mai shekara 20, Tijjani Ali mai shekara 20, da Malam Ali Mommudu mai shekara 25, waɗanda suka miƙa wuya bisa radin kansu ga dakarun haɗin gwiwar MNJTF a ƙauyen Walada da ke Damasak, bayan sun ci gaba da kai farmakin.
“Wannan miƙa wuya wata shaida ce da ke nuna tasirin ayyukan da muke yi a yanzu,” in ji Laftanar Kanar Olaniyi Osoba, babban jami’in yaɗa labarai na soji da ke hedikwatar rundunar MNJTF.
“Waɗannan mutane sun gane rashin amfanin yaƙinsu kuma sun zaɓi hanyar zaman lafiya.”
Maharan dai sun miƙa wuya sun amsa cewa suna da hannu a ayyukan ta’addanci da dama a Arewacin Borno, inda suka nuna gajiyawa da rikicin.
Sun ce a baya suna tsoron za a kashe su idan sun miƘa wuya ga jami’an tsaron, amma a yanzu sai suka ga ba haka lamarin yake ba.
Makaman da suka miƙa ga rundunar tsaron sun haɗa da bututun makamin RPG guda biyu, bama-baman RPG guda huɗu, bindiga ƙirar AK-47, bindiga ƙirar HK 21 ta Jamus.
Har ila yau, sun miƙa dawakai guda biyu, harsasai 30 da harsasai na musamman nau’in 7.62mm, harsashi nau’in 715 na 7.62mm da wayoyin hannu 12, ƙananan na’urori masu amfani da hasken rana guda shida da wuƙaƙe guda huɗu da sauransu.
Laftanar Kanar Osoba ya ce, “Yawan adadin makamai da kayan aikin da suka miƙa ya nuna girman ayyukansu.” “Ba shakka miƙa wuyan nasu zai kawo cikas ga ayyukan ta’addanci a yankin.”
Wadannan tsoffin ‘yan tada ƙayar baya yanzu haka suna bayar da bayanan sirri ga rundunar ta MNJTF, wanda ake sa ran zai taimaka a ci gaba da gudanar da ayyukanta na yaƙi da ‘yan ta’addan a yankin tafkin Chadi.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Boko Haram mai shekara
এছাড়াও পড়ুন:
NECO ta saki sakamakon jarabawar 2025
Hukumar Shirya Jarabawa ta Ƙasa (NECO), ta fitar da sakamakon jarabawar kammala sakandare (SSCE) na shekarar 2025.
Daga cikin ɗaliban da suka zana jarabawar guda 818,492, kashi 60.26 sun ci aƙalla darusa biyar da suka haɗa da Lissafi da Turanci.
Saudiyya ta saki ’yan Najeriya 3 da ta kama kan zargin safarar miyagun ƙwayoyi Gwamnati ta fara duba yara marasa galihu kyauta a asibitin Aminu KanoShugaban NECO, Farfesa Dantani Ibrahim Wushishi, ya ce ɗalibai 1,367,210 suka yi rajistar jarabawar; maza 685,514 da kuma mata 681,696.
Amma daga cikinsu, ɗalibai 1,358,339 ne suka zana jarabawar.
Ya ce ɗalibai 1,144,496, wanda ya kai adadin kashi 84.26, sun samu darusa biyar ba tare da cin Lissafi da Turanci ba.
Sai dai an dakatar da sakin sakamakon makarantu takwas a Ƙaramar Hukumar Lamorde ta Jihar Adamawa saboda rikicin ƙabilanci da ya auku tsakanin 7 zuwa 25 ga watan Yuli, 2025.
Rikicin ya yi sanadin wanda ya hana zana jarabawar darusa 13 da takardu 29.
Hukumar na tattaunawa da gwamnati don sake bai wa ɗaliban damar rubuta jarabawar.
NECO ta kuma bayyana cewa an samu makarantu 38 daga jihohi 13 ds laifin aikatar satar amsa yayin zana jarabawa.
Za a gayyace su zuwa babban ofishin NECO kafin ɗaukar mataki a kansu.
Haka kuma, hukumar ta dakatar da mutum tara da ke aikin sanya ido sake kula da jarabawa saboda gazawarsu wajen hana satar amsa.
Mutanen da aka dakatar, uku sun fito daga Jihar Ribas, uku daga Babban Birnin Tarayya, da kuma mutum ɗai-ɗai daga Jihohin Neja, Kano da Osun.