Aminiya:
2025-04-30@19:54:57 GMT

Matashi ya kai kansa ofishin ’yan sanda

Published: 16th, April 2025 GMT

Wani matashi, Umar Auwal, mai shekaru 20 da ya yi iƙirarin kashe mutane ya miƙa kansa ga rundunar ’yan sanda a Jihar Kano.

Matashin mai inkiyar ‘Abba Dujal’ ya ce ya miƙa kansa ga mahukunta ne sakamakon rashin samun kwanciyar hankali tun bayan ta’addancin da ya aikata a bayan nan.

Kotu ta yanke wa tsohon Shugaban Peru ɗaurin shekaru 15 kan laifin rashawa Dalilin da Kwankwaso zai dawo APC — Ganduje

Hakan dai na ƙunshe ne cikin wani saƙon murya da kakakin ’yan sandan Kano, SP Abdullahi Haruna Kiyawa ya wallafa a shafinsa na Facebook.

Da yake amsa tambayoyi, Abba Dujal ya yi iƙirarin aikata manyan laifuffuka da suka haɗa da kisan kai, fashi da makami da kuma satar babur da wayoyin hannu.

Matashin ya yi iƙirarin kashe wani mutum mai suna ‘Boka’ a unguwar Sabon Gari ta Kano, inda ya sace wayarsa Infinix Hot 40i, ya kuma sayar da ita a kan N40,000.

Haka zalika, ya bayyana yadda ya kashe wani mutum a unguwar Kurna da ke Kano, inda ya arce da wayarsa ƙirar Samsung S26 da ya sayar a kan N160,000.

A Jigawa kuwa, ya ce ya kashe wani mutum a karamar hukumar Ringim tare da sace babur ɗinsa da ya sayar da shi a kan N300,000.

Abba Dujal ya ce yanzu haka ya shekara bakwai bai yi sallah ba. Sai dai ya ce an saka shi a Islamiyya amma malamin ya dawo da shi gida saboda fitinar da yake a makarantar.

A fannin karatun boko kuma, Abba Dujal ya ce ya taɓa shiga firamare amma daga nan bai ƙara gaba ba.

 

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Sanda Jihar Kano

এছাড়াও পড়ুন:

‘Yansanda Sun Kama Masu Garkuwa da Mutane 12 Da Masu Sayar da Makamai 3 A Taraba Da Kaduna

A Kaduna, an kama wasu mutane uku da ake zargin masu garkuwa da mutane ne, ciki har da wani da ya ce ya koma jihar ne domin kafa sabuwar ƙungiya bayan an kama abokan aikinsa a Kwara.

Haka kuma, an kama wasu biyu da ke ɗauke da bindigogi.

‘Yansanda sun gano makamai da dama, ciki har da bindigogi ƙirar AK-47 da AK-49, da kuma wasu makamai da aka ƙera a gida.

Wannan aiki na daga cikin ƙoƙarin gwamnati na yaƙar garkuwa da mutane da safarar makamai a faɗin ƙasar.

Kakakin rundunar, Olumuyiwa Adejobi, ya ce ana ci gaba da bincike, kuma za a gurfanar da waɗanda ake zargi a kotu da zarar an kammala binciken.

Ya kuma yaba da goyon bayan da al’umma da jami’an tsaro suka bayar wajen nasarar kama su.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An kashe Falasdinawa kusan 30 a wani sabon kisan kiyashin Isra’ila a Gaza
  • ‘Yansanda Sun Kama Masu Garkuwa da Mutane 12 Da Masu Sayar da Makamai 3 A Taraba Da Kaduna
  • ISWAP ta ɗauki alhakin kashe mutum 26 a Borno
  • An kashe mafarauta 10 a Adamawa
  • Wani abin fashewa ya kashe mutum 26 a Borno
  • Za a rataye wani soja saboda laifin kashe budurwarsa
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Jadadda Cewa: Duk Wani Harin Wuce Gona Da Iri Kan Iran Zai Fuskanci Mayar Da Martani
  • Shekara 10 ina sayar da sassan jikin ɗan Adam — Wanda ake zargi
  • Aminu Bayero ya naɗa Sanusi a matsayin Galadiman Kano
  • Ƴan Ta’adda Sun Kashe Maharba 10 A Adamawa