Aminiya:
2025-12-10@14:19:33 GMT

Matashi ya kai kansa ofishin ’yan sanda

Published: 16th, April 2025 GMT

Wani matashi, Umar Auwal, mai shekaru 20 da ya yi iƙirarin kashe mutane ya miƙa kansa ga rundunar ’yan sanda a Jihar Kano.

Matashin mai inkiyar ‘Abba Dujal’ ya ce ya miƙa kansa ga mahukunta ne sakamakon rashin samun kwanciyar hankali tun bayan ta’addancin da ya aikata a bayan nan.

Kotu ta yanke wa tsohon Shugaban Peru ɗaurin shekaru 15 kan laifin rashawa Dalilin da Kwankwaso zai dawo APC — Ganduje

Hakan dai na ƙunshe ne cikin wani saƙon murya da kakakin ’yan sandan Kano, SP Abdullahi Haruna Kiyawa ya wallafa a shafinsa na Facebook.

Da yake amsa tambayoyi, Abba Dujal ya yi iƙirarin aikata manyan laifuffuka da suka haɗa da kisan kai, fashi da makami da kuma satar babur da wayoyin hannu.

Matashin ya yi iƙirarin kashe wani mutum mai suna ‘Boka’ a unguwar Sabon Gari ta Kano, inda ya sace wayarsa Infinix Hot 40i, ya kuma sayar da ita a kan N40,000.

Haka zalika, ya bayyana yadda ya kashe wani mutum a unguwar Kurna da ke Kano, inda ya arce da wayarsa ƙirar Samsung S26 da ya sayar a kan N160,000.

A Jigawa kuwa, ya ce ya kashe wani mutum a karamar hukumar Ringim tare da sace babur ɗinsa da ya sayar da shi a kan N300,000.

Abba Dujal ya ce yanzu haka ya shekara bakwai bai yi sallah ba. Sai dai ya ce an saka shi a Islamiyya amma malamin ya dawo da shi gida saboda fitinar da yake a makarantar.

A fannin karatun boko kuma, Abba Dujal ya ce ya taɓa shiga firamare amma daga nan bai ƙara gaba ba.

 

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Sanda Jihar Kano

এছাড়াও পড়ুন:

Kasar China Ta Zartar Da Hukuncin Kisa Akan Wani Babban Jami’in Banki

A jiya Talata ne dai aka zartar da hukuncin kisa akan wani babban jami’in Banki na gwamnati bayan da aka same shi da laifin barnata dukiya.

Kafafen watsa labarun kasar China sun ce mutumin da aka zartarwa da hukuncin kisan, tsohon manaja ne a wani babban kamfani na hukuma.

A shekarar 2024 ne dai  aka sami Bay Tian Hua, saboda samunsa da karbar toshiyar baki da ta kai dalar Amurka miliyan 156 domin bai wa wani kamfani fifiko samun kwangilar aiki a tsakanin 2014-2018.

Tashar talabijin din CCTV ta gwamnatin kasar China ta ce; kotun al’umma ce ta yanke hukuncin akan wannan laifin da ta bayyana da cewa mai matukar hatsari ne.

An zartar da hukuncin kisan ne dai akan  Bay a garin Tianjin dake yankin arewa maso gabashin kasar, bayan da ya yi bankwana da ‘yan’uwansa.

A kasar China dai ana zartar da hukuncin kisa akan wadanda aka samu dacin hanci da rashawa. Wasu lokutan kuma ana rage hukuncin kisan zuwa zaman kurkuku na shekaru biyu, ko kuma zaman kurkuku na har abada.

Kamfani da Bay ya yi wa manaja yana cikin manyan cibiyoyin kudi na bayar da bashi mai rassa a fadin kasar ta China.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Ganawa A Tsakanin Mataimakan Ministocin Waje Na Kasashen Saudiyya, China Da Minista Arakci Na Iran December 10, 2025 Antoni Gutress Ya Yi Allawadai Da Kutsen Da “Isra’ila” Ta Yi A Cibiyar Unrwa December 10, 2025 Iran da Saudiyya sun sake jaddada fadada dangantakarsu December 9, 2025 Faransa ta ce da hannunta aka dakile juyin mulki a Benin December 9, 2025 RSF : Rabin ‘Yan jarida 67 da aka kashe a bana, a Zirin Gaza ne December 9, 2025 An cire Tony Blair daga jerin wadanda zasu jagoranci Gaza December 9, 2025 Isra’ila ta sake kai hare-haren a kudancin Lebanon December 9, 2025 Trump Ya Yi Gefe Da Kasashen Turai Dangane Da Tattaunawa Kan Rikicin Ukraine December 9, 2025 Iran Ta Gudanar Da Taro Kan Yadda Manzon Allah (s) Ya Yi Mu’amala Da Wadanda Ba Musulmi Ba December 9, 2025 Najeriya : Matsala ce ta sa jirgin sojinmu yin saukar gaggawa A Burkina Faso December 9, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An kama wani mutum a Abuja yana ƙoƙarin kai harsasai ga ’yan bindiga a Zamfara
  • ‘Yan Ta’adda Sun Kai Hare-Hare Kan Sojojin Pakistan Sun Kuma Kashe 6 Daga Cikinsu
  • Saurayi ya kashe budurwarsa sannan ya soya qwaqwalwarta 
  • Kasar China Ta Zartar Da Hukuncin Kisa Akan Wani Babban Jami’in Banki
  • RSF : Rabin ‘Yan jarida 67 da aka kashe a bana, a Zirin Gaza ne
  • ‘Yan Bindiga 18 Sun Muta a Wata Arangama da Rundunar Operation Fansan Yamma
  • Kasashen Iran Da Azarbaijan Sun Amince Da Ci Gaba Da Tuntubar Juna Domin Warware Duk Wani Rikici
  • An gano gawar malamin Islamiyya da ya ɓace a Neja
  • ’Yan bindiga sun hallaka mutum 4, sun sace mata 4 a Sakkwato
  • ’Yan bindiga ya hallaka mutum 4, sun sace mata 4 a Sakkwato