Aminiya:
2025-10-25@21:38:44 GMT

Matashi ya kai kansa ofishin ’yan sanda

Published: 16th, April 2025 GMT

Wani matashi, Umar Auwal, mai shekaru 20 da ya yi iƙirarin kashe mutane ya miƙa kansa ga rundunar ’yan sanda a Jihar Kano.

Matashin mai inkiyar ‘Abba Dujal’ ya ce ya miƙa kansa ga mahukunta ne sakamakon rashin samun kwanciyar hankali tun bayan ta’addancin da ya aikata a bayan nan.

Kotu ta yanke wa tsohon Shugaban Peru ɗaurin shekaru 15 kan laifin rashawa Dalilin da Kwankwaso zai dawo APC — Ganduje

Hakan dai na ƙunshe ne cikin wani saƙon murya da kakakin ’yan sandan Kano, SP Abdullahi Haruna Kiyawa ya wallafa a shafinsa na Facebook.

Da yake amsa tambayoyi, Abba Dujal ya yi iƙirarin aikata manyan laifuffuka da suka haɗa da kisan kai, fashi da makami da kuma satar babur da wayoyin hannu.

Matashin ya yi iƙirarin kashe wani mutum mai suna ‘Boka’ a unguwar Sabon Gari ta Kano, inda ya sace wayarsa Infinix Hot 40i, ya kuma sayar da ita a kan N40,000.

Haka zalika, ya bayyana yadda ya kashe wani mutum a unguwar Kurna da ke Kano, inda ya arce da wayarsa ƙirar Samsung S26 da ya sayar a kan N160,000.

A Jigawa kuwa, ya ce ya kashe wani mutum a karamar hukumar Ringim tare da sace babur ɗinsa da ya sayar da shi a kan N300,000.

Abba Dujal ya ce yanzu haka ya shekara bakwai bai yi sallah ba. Sai dai ya ce an saka shi a Islamiyya amma malamin ya dawo da shi gida saboda fitinar da yake a makarantar.

A fannin karatun boko kuma, Abba Dujal ya ce ya taɓa shiga firamare amma daga nan bai ƙara gaba ba.

 

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Sanda Jihar Kano

এছাড়াও পড়ুন:

An Kafa Cibiyoyi 296 Na Koyon Fasahar Zamani A Faɗin Nijeriya

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai Ƴan Bindiga Sun Sace Ma’aikatan INEC Uku Da Wasu October 24, 2025 Manyan Labarai Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji October 24, 2025 Manyan Labarai Nnamdi Kanu Ya Sake Bayyana A Kotu Ba Tare Da Lauya Ba, Zai Kare Kansa Da Kansa October 24, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ’Yan sanda sun taimaka wa ’yan daba rusa gidaje — Al’ummar Shendam
  • Kwamishinan Gombe ya rasu a hatsarin mota
  • ’Yan sanda sun sake kama Sowore bayan kotu ta bayar da belinsa
  • An Kafa Cibiyoyi 296 Na Koyon Fasahar Zamani A Faɗin Nijeriya
  • Gobara Ta Ƙone Fiye da Rumbuna 500 a Kasuwar Kano
  • Gwamna Abba Ya Jaddada Mubaya’arsa Ga Kwankwaso 
  • Nnamdi Kanu ya kori lauyoyinsa, ya ce zai kare kansa a kotu
  • DSS ta cafke mutum 3 kan zargin sayar wa ’yan bindiga makamai a Kaduna
  • ’Yan uwana 8 sun rasu a fashewar tanka a Neja — Wani Mutum
  • Dangote zai sayar da kaso 10 na hannun jarin matatar man shi