HausaTv:
2025-11-19@19:42:30 GMT

Dakarun Qassam sun harba makami mai linzami a kan Tel Aviv

Published: 20th, March 2025 GMT

Dakarun Falasdinawa sun mayar da martani ga kisan kiyashin da Isra’ila ke yi wa fararen hula bayan sake dawo da yakin Isra’ila a kan al’ummar Gaza, inda suka harba rokoki zuwa Tel Aviv.

Al-Qassam Brigades, reshen soji na kungiyar gwagwarmayar Islama ta Hamas, ta sanar a wannan  Alhamis cewa, ta yi ruwan makamai masu linzami samfurin M90 a kan birnin Tel Aviv, a matsayin mayar da martani ga kisan kiyashi da Haramtacciyar Kasar Isra’ila ke yi kan fararen hula a zirin Gaza.

Sojojin mamaya na Isra’ila sun tabbatar da cewa sun gano wasu rokoki guda uku da aka harba daga Gaza zuwa tsakiyar Falasdinu da suka mamaye, tare da jin karar makamai a sararin samniyar Tel Aviv, Gush Dan, da matsugunan yahudawa da ke kewaye.

Isra’ila bat a mutunta yarjejeniyar tsagaita bude wuta ba, kamar yadda ta yi fatali da mataki na biyu na yarjejeniyar , tare da sanya wasu sharudda da gangan domin matsin lamba a kan kungiyoyin  gwagwarmayar Falasdinu.

Isra’ila Ta sake sabunta kai hare-hare a zirin Gaza, inda ta kai hari a wurare daban-daban na yankin tun daga kwanaki biyu zuwa uku da suka gabata har zuwa yau.

Hare-haren na Haramtacciyar Kasar Isra’ila sun yi sanadin shahadar daruruwan fararen hula, galibi mata da kanan yara, tare da jikkata wasu da dama .

Wakilin Al-Mayadeen ya tabbatar da cewa sojojin haramtacciyar kasar Isra’ila sun sake raba arewacin Gaza daga tsakiya da kuma kudancin yankin, inda suka sake kwace iko da yankin Netzarim.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Mutane 7 sun mutu a hatsarin mota a Jigawa

Wani mummunan hatsarin mota da ya faru a Jihar Jigawa ya yi sanadin mutuwar mutane bakwai ciki har da direban motar tare da jikkata wasu 11.

Kakakin rundunar ’yan sandan jihar, SP Shiisu Lawan Adam, ya tabbatar da faruwar lamarin cikin wata sanarwa da ya aike wa manema labarai a Dutse.

Anthony Joshua zai yi dambe da tauraron YouTube Jake Paul a Disamba Gwamnonin Arewa sun yi Allah-wadai da sace ɗalibai mata a Kebbi

Ya ce hatsarin ya afku ne da misalin ƙarfe 4:30 na yammacin Lahadi, 16 ga Nuwamba 2025, a ƙauyen Jigawan Kurma da ke kan titin Kiyawa zuwa Azaren Jihar Bauchi.

A cewar SP Shiisu, “Mota kirar Hummer ce da ta taso daga Kano zuwa Potiskum ɗauke da fasinjoji 18. Hatsarin ya faru ne bayan fashewar tayoyi biyu, sakamakon gudun wuce sa’a da direban yake yi.”

Ya ƙara da cewa sauran 11 da suka samu munanan raunuka an garzaya da su babban asibitin Birnin Dutse, inda aka sallami huɗu daga cikinsu bayan samun kulawa.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sojojin Yemen Suna Da Makami Mai Linzami Da Babu Mai Makamancinsa Sai Iran
  • Gwamnatin Mamayar Isra’ila Ta Karya Yarjejeniyar Tsagaita Bude Wuta A Gaza Kusan Sau 400
  • Kimanin Falasdinawa 2 Ne Suka yi Shahada Sakamakon Harin Isra’ila  A  Ainul Hilwa
  • DAGA LARABA: Hanyoyin Da Suka Kamata A Bi Wajen Ceto Daliban Kebbi Da Aka Sace
  • Gwamnan Taraba ya dakatar da ficewa daga PDP saboda sace ɗalibai a Kebbi
  • Mutane 7 sun mutu a hatsarin mota a Jigawa
  • Afrika ta Kudu Ta yi Gargadi Game Da Duk Wani Yunkuri Na Fitar Da Falasdinawa Daga Yankin Gaza
  • MDD ta amince da kudurin tura dakarun kasa da kasa zuwa Gaza
  • Sace Ɗalibai: Gwamnatin Tinubu ba ta shirya kawo ƙarshen ta’addancin ’yan bindiga ba — Amnesty
  • Hamas Da Sauran Bangarorin Falasdinawa Sun yi Watsi Da Shirin Aikewa Da Dakarun Kasashen Waje A Yankin Gaza