HausaTv:
2025-07-05@17:35:16 GMT

Dakarun Qassam sun harba makami mai linzami a kan Tel Aviv

Published: 20th, March 2025 GMT

Dakarun Falasdinawa sun mayar da martani ga kisan kiyashin da Isra’ila ke yi wa fararen hula bayan sake dawo da yakin Isra’ila a kan al’ummar Gaza, inda suka harba rokoki zuwa Tel Aviv.

Al-Qassam Brigades, reshen soji na kungiyar gwagwarmayar Islama ta Hamas, ta sanar a wannan  Alhamis cewa, ta yi ruwan makamai masu linzami samfurin M90 a kan birnin Tel Aviv, a matsayin mayar da martani ga kisan kiyashi da Haramtacciyar Kasar Isra’ila ke yi kan fararen hula a zirin Gaza.

Sojojin mamaya na Isra’ila sun tabbatar da cewa sun gano wasu rokoki guda uku da aka harba daga Gaza zuwa tsakiyar Falasdinu da suka mamaye, tare da jin karar makamai a sararin samniyar Tel Aviv, Gush Dan, da matsugunan yahudawa da ke kewaye.

Isra’ila bat a mutunta yarjejeniyar tsagaita bude wuta ba, kamar yadda ta yi fatali da mataki na biyu na yarjejeniyar , tare da sanya wasu sharudda da gangan domin matsin lamba a kan kungiyoyin  gwagwarmayar Falasdinu.

Isra’ila Ta sake sabunta kai hare-hare a zirin Gaza, inda ta kai hari a wurare daban-daban na yankin tun daga kwanaki biyu zuwa uku da suka gabata har zuwa yau.

Hare-haren na Haramtacciyar Kasar Isra’ila sun yi sanadin shahadar daruruwan fararen hula, galibi mata da kanan yara, tare da jikkata wasu da dama .

Wakilin Al-Mayadeen ya tabbatar da cewa sojojin haramtacciyar kasar Isra’ila sun sake raba arewacin Gaza daga tsakiya da kuma kudancin yankin, inda suka sake kwace iko da yankin Netzarim.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

‘Yan Sanda Sun Hana Yunqurin Fasa Shago a Gombe, Tare da Kwato Babur

 

Rundunar ‘Yan Sandan Jihar Gombe ta hana yunqurin fasa wani shago da wasu vata-gari suka yi qoqarin yi a Unguwar Buba Shongo da ke cikin birnin Gombe, inda ta qwato wani babur da kayan da ake zargin an yi niyyar amfani da su wajen fasa shagon.

A cewar sanarwar da mai Magana da Yawun Rundunar, DSP Buhari Abdullahi, ya fitar, lamarin ya faru ne da misalin qarfe 3:00 na safiyar Litinin, 1 ga Watan Yuli, 2025, lokacin da jami’an Operation Hattara ke kan sintiri a daren.

Jami’an sun hango wasu mutane da ba a san ko su wane ne ba suna qoqarin fasa wani shago mallakin wani Muhammadu Adamu Musa, mai shekara 42 da haihuwa.

Da vatagarin suka hango motar sintirin ‘yan sanda na qaratowa, sai suka tsere suka bar shagon ba tare da cimma burinsu ba.

Kayan da aka samu a wurin sun haxa da baqin babur qirar Yamaha mai lamba GME 480 VN da wani qarfe na tanqwara qoafa da takalmin roba guda xaya.

“Dukkan kayan da aka qwato suna hannun ‘yan sanda, kuma bincike yana ci gaba a kan zargin haxa baki da yunqurin aikata laifi,” in ji sanarwar.

Rundunar ta bayyana cewa wannan lamari ya qara tabbatar da cewar dokar da ta takaita zirga-zirgar babura a cikin dare a faxin jihar na nan daram, domin yawan laifukan da ake aikatawa da su a wannan lokaci na dare.

Rundunar ta kuma tabbatar wa da jama’a cewa tana ci gaba da qoqari don kamo waxanda suka gudu tare da gurfanar da su a gaban shari’a.

Haka zalika, rundunar ta buqaci jama’a da su kasance masu lura da abin da ke faruwa a muhallansu tare da ci gaba da bayar da sahihan bayanai ga jami’an tsaro domin tabbatar da zaman lafiya da kare rayuka da dukiyoyin al’umma

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamna Ademola Adeleke Ya Ƙaryata Jita-Jitar Sauya Sheƙa Daga PDP Zuwa APC
  • Shugaban Amurka Yace Yana Jiran Amsar Hamas Cikin Sa’o’i 24 Masu Zuwa Don Tsagaita Wuta Na Kwanaki 60
  • Sojojin Mamayar Isra’ila Suna Ci Gaba Da Kashe Masu Neman Karbar Kayan Agaji A Gaza
  • Haɗarin Da Ke Ƙunshe Da Jin Ɓangare Ɗaya Na Labari
  • Shugaban Amurka Yace Yana Jirin Hamas Cikin Sa’o’i 24 Masu Zuwa Don Tsagaita Wuta Na Kwanaki 60
  • Sojojin Mamayar Isra’ila Sun Sake Aiwatar Da Kisan Kare Dangi Kan ‘Yan Gudun Hijiran Falasdinawa
  • ‘Yan Sanda Sun Hana Yunqurin Fasa Shago a Gombe, Tare da Kwato Babur
  • Sarayal Kuds Ta Kai Wa  Matsugunin ‘Yan Mamaya Na Sydriot Hari Da Makamai Masu Linzami
  • Kasar Iran Ta Nuna Ire-Iren Makamai Masu Linzami Da Ta Mayar Da Martani Da Su Kan ‘Yan Mamaya
  • Sojojin Mamayar Isra’ila Sun Yi Luguden Bama-Bamai Kan Falasdinawa Da Suka Janyo Shahada Da Jikkata