Kungiyar hadin kan kasashen musulmi ta duniya ta fitar da wata sanarwa inda ta yi Allah wadai da sake dawo da hare-haren wuce gona da irin da Isra’ila ke yi a zirin Gaza tare da yin kira da a dauki matakin gaggawa na kasashen duniya domin dakile wadannan laifuka.

Kungiyar hadin kan kasashen musulmi ta yi Allah wadai da sake kai hare-haren bama-bamai a yankin zirin Gaza da yahudawan sahyuniya suka yi, lamarin da ya janyo hasarar rayukan fararen hula da ba su ji ba ba su gani ba.

A cikin wata sanarwa da ya fitar, Sheik Muhammad bin Abdulkarim Issa, babban sakataren kungiyar hadin kan kasashen musulmi ta duniya, ya yi Allah wadai da zaluncin gwamnatin sahyoniyawa, wanda hakan ya saba wa dukkanin dokokin kasa da kasa.

Ya kuma jaddada bukatar daukar matakin gaggawa na kasashen duniya domin dakile wannan kisan kiyashi da mashinan yakin gwamnatin haramtacciyar kasar Isra’ila ke ci gaba da kai hare-hare kan fararen hula da fararen hula.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: yi Allah wadai da

এছাড়াও পড়ুন:

Majalisar Dattawa ta gindaya sharaɗin dawo da Sanata Natasha

Majalisar Dattawan Nijeriya ta gindaya sharaɗin dawo da Sanata Natasha Akpoti Uduaghan gabanin cikar wa’adin dakatar da ita da ta yi tsawon watanni shida.

Majalisar ta ce ala tilas ne dakatacciyar Sanatar ta bayar da hakuri tare da neman afuwa a hukumance gabanin cika umarnin da ta wata Babbar Kotun Tarayya ta bayar na dawo da ita.

Ambaliyar ruwa ta yi ajalin mutum 50 a Amurka An kama ɗan Najeriya yana taimaka wa Rasha a yaƙinta da Ukraine

Shugaban Kwamitin Labarai da Harkokin Jamaa na Majalisar Dattawa, Sanata Adeyemi Adaramodu ne ya bayyana hakan yayin da yake martani kan hukuncin da kotun ta yanke a kan Sanata Natasha.

Ya yi bayanin cewa, a yayin yanke hukuncin da ta bayar da umarnin dawo da Sanata Natasha, kotun ba ta hana majalisar ladabtar da mambobinta a yayin da ta same su da laifi kamar yadda yake a cikin kundin tsarinta.

A bayan nan ne dai wata Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja, ta buƙaci Majalisar Dattawan ta dawo da Sanata Natasha Akpoti.

Da take yanke hukunci, Mai Shari’a Binta Nyako ta kwatanta cewa dakatar da Natasha tsawon watanni shida da aka yi, ya yi tsauri.

Kotun ta kuma ce Shugaban Majalisar Dattawan Godswill Akpabio bai yi laifi ba, lokacin da ya hana Natasha yin magana a majalisa saboda lokacin ba ta zauna kan ainihin kujerar da aka ware mata ba.

Ta kuma buƙaci Sanata Natasha ta bai wa majalisar hakuri.

Sai dai a cewar kotun, tun da ’yan majalisa suna da tsawon kwanaki 181 don zama a kowane zango, dakatar da Natasha tsawon watanni da aka yi — yana kamar hana ta aiwatar da haƙƙokinta ne ga ’yan mazaɓarta na tsawon kwanaki 180.

Har ila yau, kotun ta ce Majalisar Dattawa tana da damar hukunta kowane ɗan majalisa da ya yi laifi, sai dai kada hukuncin ya yi tsaurin da zai hana aiwatar da ayyukan mazaɓar ɗan majalisa da aka dakatar.

Mai Shari’a Nyako ta kuma kori batun da Akpabio ya gabatar cewa kotun ba ta hurumin sauraron ƙarar.

Tun da farko, kotun ta ci Sanata Natasha tarar naira miliyan biyar saboda raina kotu, wanda ya hana ɓangarorin biyu yin magana a bainar jama’a kan batun.

Ta kuma buƙaci Natasha ta nemi afuwa a gidajen jaridu biyu da shafinta na Facebook cikin kwanaki bakwai.

A watan Maris ne Majalisar Dattawa ta dakatar da Sanata Natasha bayan da ta zargi Sanata Godswill Akpabio da cin zarafi na lalata, laifin da har yanzu ya musanta.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • HKI Ta Kashe Falasdianwa 6 A Gaza, Kuma Tsoffin Fursinoni
  • Firaminsitan Sin: Dole Ne Hadin Gwiwar Brics Ya Gaggauta Kafa Ka’idar Ciniki Da Tattalin Arzikin Duniya Mai Adalci Da Bude Kofa
  • Zan Yi Ƙoƙarin Dawo Da Martabar Kano Pillars A Idon Duniya — Ahmed Musa
  • Falasdinawa 13 Ne Suka Yi Shahada Wasu Da Dama Suka Jikkata A Hare-Haren Sojojin Mamayar Isra’ila A Gaza
  • Kasar China Ta Yi Watsi da Barazanar Trump Na Kakabawa Kasashen BRICS Karin Takunkuman Tattalin Arziki
  • Gwamnatin Kasar Iran Ta Yi Allawadai Da Hare-Haren HKI Kan Kasar Yemen
  • Sojojin Mamayar Isra’ila Sun Kai Hare-Haren Wuce Gona Da Iri Kan Lardin Hodeidah Na Kasar Yemen
  • Kungiyoyin Gwagwarmayar Falasdinawa Sun Yi Allah Wadai Da Harin Mamayar Isra’ila Kan Kasar Yemen
  • Majalisar Dattawa ta gindaya sharaɗin dawo da Sanata Natasha
  • Al’ummar A sassan Duniya Sun Gudanar Da Zanga-Zangar Goyon Bayan Falasdinawa